< Hebrews 2 >
1 Therfor more plenteuousli it bihoueth vs to kepe tho thingis, that we han herd, lest perauenture we fleten awei.
Dole mu ƙara mai da hankali sosai ga abubuwan da muka ji, don kada mu kauce.
2 For if the ilke word that was seid bi aungels, was maad sad, and ech brekyng of the lawe and vnobedience took iust retribucioun of meede,
Gama in saƙon da aka faɗi ta bakin mala’iku ya zama tabbatacce, kuma kowane ƙeta umarni da rashin biyayya suka karɓi sakamakonsu da ya dace,
3 hou schulen we ascape, if we despisen so greet an heelthe? Which, whanne it hadde takun bigynnyng to be teld out by the Lord, of hem that herden is confermyd in to vs.
yaya za mu tsira in muka ƙyale irin wannan babban ceto? Wannan ceto, wanda Ubangiji ne ya fara sanar, aka kuma tabbatar mana ta bakin waɗanda suka ji shi.
4 For God witnesside to gidere bi myraclis, and wondris, and grete merueilis, and dyuerse vertues, and departyngis of the Hooli Goost, bi his wille.
Allah shi ma ya shaida ta wurin alamu, abubuwan banmamaki da mu’ujizai iri-iri, da kuma baye-bayen Ruhu Mai Tsarki da aka rarraba bisa ga nufinsa.
5 But not to aungels God sugetide the world that is to comynge, of which we speken.
Ba ga mala’iku ba ne ya sa su yi mulkin duniya mai zuwa, wanda muke magana a kai ba.
6 But sum man witnesside in a place, and seide, What thing is man, that thou art myndeful of hym, or mannus sone, for thou visitist hym?
Amma akwai wani wurin da wani ya shaida cewa, “Mene ne mutum, da kake tuna da shi, ɗan mutum da kake kula da shi?
7 Thou hast maad hym a litil lesse than aungels; thou hast corowned hym with glorie and onour; and thou hast ordeyned him on the werkis of thin hondis.
Ka sa shi ƙasa kaɗan da darajar mala’iku; ka naɗa shi da ɗaukaka da girma,
8 Thou hast maad alle thingis suget vndur hise feet. And in that that he sugetide alle thingis to hym, he lefte no thing vnsuget to him. But now we seen not yit alle thingis suget to hym;
ka kuma sa kome a ƙarƙashin ƙafafunsa.” Ta wurin sa kome a ƙarƙashinsa, Allah bai bar wani abu da bai sa a ƙarƙashinsa ba. Duk da haka a yanzu ba mu ga kowane abu a ƙarƙashinsa ba.
9 but we seen hym that was maad a litil lesse than aungels, Jhesu, for the passioun of deth crowned with glorie and onour, that he thorouy grace of God schulde taste deth for alle men.
Sai dai muna ganin Yesu, wanda aka mai da shi ƙasa kaɗan da darajar mala’iku, yanzu kuwa an naɗa shi da ɗaukaka da girma domin yă sha wahalar mutuwa, domin ta wurin alherin Allah yă ɗanɗana mutuwa saboda kowa.
10 For it bisemede hym, for whom alle thingis, and bi whom `alle thingis weren maad, which hadde brouyt many sones into glorie, and was auctour of the heelthe of hem, that he hadde an ende bi passioun.
Ta wurin kawo’ya’ya masu yawa zuwa ga ɗaukaka, ya dace cewa Allah, wanda dominsa da kuma ta wurinsa ne kome yake kasancewa, ya sa tushen cetonsu yă zama cikakke ta wurin shan wahala.
11 For he that halewith, and thei that ben halewid, ben alle of oon; for which cause he is not schamed to clepe hem britheren,
Da shi wanda yake tsarkake mutane da kuma su waɗanda ake tsarkakewa duk’yan iyali ɗaya ne. Saboda haka Yesu ba ya kunyan kiransu’yan’uwansa.
12 seiynge, Y schal telle thi name to my britheren; in the myddil of the chirche Y schal herie thee.
Ya ce, “Zan sanar da sunanka ga’yan’uwana; a gaban jama’a zan rera yabonka.”
13 And eftsoone, Y schal be tristnynge in to hym; and eftsoone, Lo! Y and my children, whiche God yaf to me.
Har wa yau ya ce, “Zan dogara gare shi.” Ya kuma ce, “Ga ni, da’ya’yan da Allah ya ba ni.”
14 Therfor for children comyneden to fleisch and blood, and he also took part of the same, that bi deth he schulde destrie hym that hadde lordschipe of deth, that is to seie, the deuel,
Da yake’ya’yan suna da nama da jini, shi ma sai ya ɗauki kamanninsu na mutum domin ta wurin mutuwarsa yă hallaka wanda yake riƙe da ikon mutuwa, wato, Iblis
15 and that he schulde delyuere hem that bi drede of deth, `bi al lijf weren boundun to seruage.
ya kuma’yantar da waɗanda dukan rayuwarsu tsoron mutuwa ya riƙe su cikin bauta.
16 And he took neuere aungelis, but he took the seed of Abraham.
Gama tabbatacce ba mala’iku ne ya taimaka ba, sai dai zuriyar Ibrahim.
17 Wherfor he ouyte to be likned to britheren bi alle thingis, that he schulde be maad merciful and a feithful bischop to God, that he schulde be merciful to the trespassis of the puple.
Saboda wannan dole a mai da shi kamar’yan’uwansa ta kowace hanya, domin yă zama babban firist mai aminci da mai jinƙai cikin hidima ga Allah, yă kuma miƙa hadayar sulhu saboda zunuban mutane.
18 For in that thing in which he suffride, and was temptid, he is miyti to helpe also hem that ben temptid.
Domin shi kansa ya sha wahala sa’ad da aka gwada shi, yana iya taimakon waɗanda ake yi wa gwaji.