< Genesis 8 >

1 Forsothe the Lord hadde mynde of Noe, and of alle lyuynge beestis, and of alle werk beestis, that weren with hym in the schip; and brouyte a wynd on the erthe.
Amma Allah ya tuna da Nuhu da dukan namun jeji da dabbobin da suke tare da shi a cikin jirgi, ya kuma aika da wata iska ta hura dukan duniya, ruwan kuwa ya janye.
2 And watris weren decreessid, and the wellis of the see weren closid, and the wyndowis of heuene weren closid, and reynes of heuene weren ceessid.
Aka toshe maɓuɓɓugan zurfafa da ƙofofin ambaliyar sammai, ruwan sama kuma ya daina saukowa daga sarari.
3 And watrys turneden ayen fro erthe, and yeden ayen, and bigunnen to be decreessid aftir an hundrid and fifti daies.
Ruwan ya janye a hankali daga ƙasa. A ƙarshen kwanaki ɗari da hamsin ɗin, ruwan ya ragu.
4 And the schip restide in the seuenthe monthe, in the seuene and twentithe dai of the monthe, on the hillis of Armenye.
A rana ta goma sha bakwai ga watan bakwai, jirgin ya sauka a duwatsun Ararat.
5 And sotheli the watrys yeden and decresiden til to the tenthe monethe, for in the tenthe monethe, in the firste dai of the monethe, the coppis of hillis apperiden.
Ruwan ya ci gaba da janyewa har watan goma. A rana ta fari ga watan goma kuwa ƙwanƙolin duwatsun suka bayyana.
6 And whanne fourti daies weren passid, Noe openyde the wyndow of the schip which he hadde maad, and sente out a crowe,
Bayan kwana arba’in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi,
7 which yede out, and turnede not ayen til the watris weren dried on erthe.
ya saki hankaka. Hankaka ya yi ta kai da kawowa har sai da ruwa ya shanye a duniya.
8 Also Noe sente out a culuer aftir hym, to se if the watris hadden ceessid thanne on the face of erthe;
Sai ya saki kurciya don yă ga in ruwan ya janye daga doron ƙasa.
9 and whanne the culuer foond not where hir foot schulde reste, sche turnede ayen to hym in to the schip, for the watris weren on al erthe; and Noe helde forth his hoond, and brouyte the culuer takun in to the schip.
Amma kurciyar ba tă sami inda za tă sa ƙafafunta ba gama akwai ruwa a dukan doron ƙasa, saboda haka ta komo wurin Nuhu a jirgi. Ya miƙa hannunsa ya ɗauko kurciyar ya shigar da ita wurinsa a cikin jirgi.
10 Sotheli whanne othere seuene daies weren abedun aftirward, eft he leet out a culuer fro the schip;
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar daga jirgi.
11 and sche cam to hym at euentid, and bare in hir mouth a braunche of olyue tre with greene leeuys. Therfor Noe vndirstood that the watris hadden ceessid on erthe;
Sa’ad da kurciya ta komo wurinsa da yamma, sai ga ɗanyen ganyen zaitun da ta tsinko a bakinta! Sa’an nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga duniya.
12 and neuerthelesse he abood seuene othere daies, and sente out a culuer, which turnede `no more ayen to hym.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar, amma a wannan ƙaro ba tă komo wurinsa ba.
13 Therfor in the sixe hundrid and o yeer of the lijf of Noe, in the firste monethe, in the firste day of the monethe, watris weren decreessid on erthe; and Noe openede the roof of the schip, and bihelde and seiy that the face of the erthe was dried.
A rana ta fari ga wata na fari wanda Nuhu ya cika shekaru 601, ruwa ya shanye a ƙasa. Sai Nuhu ya buɗe murfin jirgin, ya ga cewa doron ƙasa ya bushe.
14 In the secunde monethe, in the seuene and twentithe dai of the monethe, the erthe was maad drie.
A ran ashirin da bakwai ga wata na biyu, ƙasa ta bushe ƙaƙaf.
15 Sotheli the Lord spak to Noe;
Sa’an nan Allah ya ce wa Nuhu,
16 and seide, Go out of the schip, thou, and thi wijf, thi sones, and the wyues of thi sones with thee;
“Fito daga jirgin, kai da matarka da’ya’yanka maza da matansu.
17 and lede out with thee alle lyuynge beestis that ben at thee of ech fleisch, as wel in volatilis as in vnresonable beestis, and alle `reptils that crepen on erthe; and entre ye on the erthe, encreesse ye, and be ye multiplied on erthe.
Ka fitar da kowane iri halitta mai rai da take tare da kai waje, tsuntsaye, dabbobi, da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa, don su yi ta haihuwa, su yi yawa, su ƙaru a duniya.”
18 Therfor Noe yede out, and hise sones, and his wijf, and the wyues of hise sones with hym;
Sai Nuhu ya fito tare da matarsa da’ya’yansa maza da matan’ya’yansa,
19 but also alle lyuynge beestis, and werk beestis, and `reptils that crepen on erthe, bi her kynde, yeden out of the schip.
da kowace irin dabba, da kowane mai rarrafe, da kowane irin tsuntsu, da kowane irin abu da yake tafiya a bisa duniya, suka fito daga jirgi daki-daki bisa ga irinsu.
20 Forsothe Noe bildide an auter to the Lord, and he took of alle clene beestis and briddis, and offride brent sacrifices on the auter.
Sai Nuhu ya gina bagaden hadaya ga Ubangiji, ya ɗiba waɗansu dabbobi da tsuntsaye masu tsabta, ya yi hadaya ta ƙonawa da su a kan bagaden.
21 And the Lord sauerede the odour of swetnesse, and seide to hym, Y schal no more curse the erthe for men, for the wit and thouyt of mannus herte ben redi in to yuel fro yong wexynge age; therfor Y schal no more smyte ech lyuynge soule as Y dide;
Da Ubangiji ya ji ƙanshi mai daɗi, sai ya ce a zuciyarsa, “Ba zan ƙara la’anta ƙasa saboda mutum ba, ko da yake dukan tunanin zuciyar mutum mugu ne tun yana ƙarami. Ba kuwa zan ƙara hallaka dukan halittu masu rai, kamar yadda na yi ba.
22 in alle the daies of erthe, seed and ripe corn, coold and heete, somer and wyntir, nyyt and dai, shulen not reste.
“Muddin duniya tana nan, lokacin shuki da na girbi, lokacin sanyi da na zafi, lokacin damina da na rani, dare da rana ba za su daina ba.”

< Genesis 8 >

A Dove is Sent Forth from the Ark
A Dove is Sent Forth from the Ark