< Genesis 50 >

1 Which thing Joseph seiy, and felde on `the face of the fader, and wepte, and kiste hym;
Yusuf kuwa ya fāɗa a kan mahaifinsa, ya yi kuka a kansa, ya kuma sumbace shi.
2 and he comaundide hise seruauntis, lechis, that thei schulden anoynte the fadir with swete smellynge spiceries.
Sa’an nan Yusuf ya umarci masu maganin da suke yin masa hidima, su shafe mahaifinsa Isra’ila da maganin hana ruɓa. Saboda haka masu maganin suka shafe shi da maganin hana ruɓa.
3 While thei `filliden the comaundementis, fourti daies passiden, for this was the custom of deed bodies anoyntid; and Egipt biwepte hym seuenti daies.
Suka ɗauki kwana arba’in cif suna yin wannan, gama kwanakin da ake bukata ke nan don shafewa da maganin hana ruɓa. Masarawa kuwa suka yi makoki dominsa kwana saba’in.
4 And whanne the tyme of weiling was fillid, Joseph spak to the meyne of Farao, If Y haue founde grace in youre siyt, speke ye in the eeris of Farao; for my fadir chargide me,
Sa’ad da kwanakin makoki suka wuce, sai Yusuf ya ce wa iyalin gidan Fir’auna, “In na sami tagomashi a idanunku, ku yi magana da Fir’auna domina. Ku faɗa masa,
5 and seide, Lo! Y die, thou schalt birie me in my sepulcre which Y diggide to me in the lond of Canaan; therfor Y schal stie that Y birie my fadir, and Y schal turne ayen.
‘Mahaifina ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, “Ina gab da mutuwa, ka binne ni a kabarin da na haƙa wa kaina a ƙasar Kan’ana.” Yanzu fa bari in haura in binne mahaifina, sa’an nan in dawo.’”
6 And Farao seide to hym, Stie, and birie thi fader, as thou art chargid.
Fir’auna ya ce, “Haura ka binne mahaifinka, kamar yadda ya sa ka rantse za ka yi.”
7 And whanne `he stiede, alle the elde men of `the hous of Farao yeden with him, and alle the grettere men in birthe of the lond of Egipt; the hous of Joseph with her britheren,
Saboda haka Yusuf ya haura don yă binne mahaifinsa. Dukan hafsoshin Fir’auna suka yi masa rakiya tare da manyan mutanen gidan Fir’auna, da kuma dukan manyan mutanen Masar
8 without litle children, and flockis, and grete beestis, whiche thei leften in the lond of Gessen, yeden with him.
da kuma dukan membobin gidan Yusuf, da’yan’uwansa da kuma waɗanda suke na gidan mahaifinsa. Yara kaɗai da garkunansu da kuma shanunsu ne aka bari a Goshen.
9 And he hadde charis, and horsmen, and felouschip, and cumpany was maad not litil.
Kekunan yaƙi da mahayan dawakai su ma suka haura tare da shi. Babbar ƙungiya jama’a ce ƙwarai.
10 And thei camen to the cornfloor of Adad, which is set ouer Jordan, where thei maden the seruice of the deed bodi, with greet weilyng and strong, and fillide seuen daies.
Sa’ad da suka kai masussukar Atad, kusa da Urdun, sai suka yi kuka da ƙarfi da kuma mai zafi, a can Yusuf ya yi makoki kwana bakwai saboda mahaifinsa.
11 And whanne the dwellers of the lond of Canaan hadden seyn this, thei seiden, This is a greet weiling to Egipcians; and therfor thei clepiden the name of that place the weilyng of Egipt.
Sa’ad da Kan’aniyawa waɗanda suke zama a can suka ga makokin a masussukan Atad, sai suka ce, “Masarawa suna bikin makoki na musamman.” Shi ya sa ake kira wannan wurin da yake kusa da Urdun, Abel-Mizrayim.
12 Therfor the sones of Jacob diden, as he hadde comaundid to hem;
Haka fa’ya’yan Yaƙub maza suka yi yadda ya umarce su.
13 and thei baren hym in to the lond of Canaan, and thei birieden hym in the double denne, which denne with the feeld Abraham hadde bouyt of Effron Ethei, ayens the face of Mambre, into possessioun of sepulcre.
Suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan’ana suka kuma binne shi a kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, ya zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
14 And Joseph turnede ayen in to Egipt with hise britheren and al the felouschipe, whanne the fadir was biried.
Bayan ya binne mahaifinsa, sai Yusuf ya koma Masar, tare da’yan’uwansa da kuma dukan waɗanda suka tafi tare da shi don binne mahaifinsa.
15 And whanne the fadir was deed, the britheren of Joseph dredden, and spaken togidere, lest perauenture he be myndeful of the wrong which he suffride, and yelde to vs al the yuel, that we diden.
Sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, sai suka ce, “Mai yiwuwa Yusuf yana riƙe da mu a zuciya, wataƙila zai rama dukan abubuwa marasa kyau da muka yi masa?”
16 And thei senten to hym, and seiden, Thi fadir comaundide to vs,
Saboda haka suka aika wa Yusuf suna cewa, “Mahaifinka ya bar waɗannan umarnai kafin yă rasu.
17 bifore that he diede, that we schulden seie to thee these thingis bi hise wordis; Y beseche, that thou foryete the wickidnesse of thi britheren, and the synne, and malice which thei hauntiden ayens thee; also we preien, that thou foryyue this wickidnesse to thi fadir, the seruaunt of God. Whanne these thingis weren herd, Joseph wepte.
Ga abin da za ku ce wa Yusuf, ‘Na roƙe ka, ka gafarta wa’yan’uwanka zunubai da laifofin da suka aikata na abubuwa marasa kyau da suka yi maka.’ Yanzu muna roƙonka ka gafarta zunuban bayin Allah na mahaifinka.” Sa’ad da saƙonsu ya zo masa, sai Yusuf ya yi kuka.
18 And hise britheren camen to hym, and worschipiden lowe to erthe, and seiden, We ben thi seruauntis.
’Yan’uwansa kuwa suka zo suka fāɗi a gabansa suka ce, “Mu bayinka ne.”
19 To whiche he answeride, Nyle ye drede; whether we moun ayenstonde Goddis wille?
Amma Yusuf ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Ni Allah ne?
20 Ye thouyten yuel of me, and God turnede it in to good, that he schulde enhaunse me, as ye seen in present tyme, and that he schulde make saaf many puplis;
Kun yi niyya ku yi mini lahani, amma Allah ya nufe wannan ya zama alheri don yă cika abin da yanzu yake faruwa, ceton rayuka masu yawa.
21 nyle ye drede, Y schal fede you and youre litle children. And he coumfortide hem, and spak swetli, and liytly;
Saboda haka, kada ku ji tsoro. Zan tanada muku da kuma’ya’yanku.” Ya sāke tabbatar musu, ya kuma yi musu magana ta alheri.
22 and he dwellide in Egipt, with al the hows of his fadir. And he lyuyde an hundrid yeer,
Yusuf ya zauna a Masar tare da dukan iyalin mahaifinsa. Ya rayu shekara ɗari da goma.
23 and he seiy the sones of Effraym til to the thridde generacioun; also the sones of Machir, son of Manasses, weren borun in the knees of Joseph.
Ya kuma ga tsara ta uku ta’ya’yan Efraim. Haka ma’ya’yan Makir ɗan Manasse, an haife su aka sa a gwiwoyin Yusuf.
24 Whanne these thingis weren don, Joseph spak to hise brithren, Aftir my deeth God schal visite you, and he schal make to stie fro this lond to the loond which he swoor to Abraham, Ysaac, and Jacob.
Sai Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ina gab da mutuwa. Amma tabbatacce Allah zai taimake ku, yă fid da ku daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.”
25 And whanne he hadde chargid hem, and hadde seid, God schal visite you, bere ye out with you my boonus fro this place,
Yusuf kuwa ya sa’ya’yan Isra’ila maza suka yi rantsuwa, ya kuma ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, ku kuma dole ku ɗauki ƙasusuwana, ku haura da su daga wannan wuri.”
26 he diede, whanne an hundrid and ten yeeris of his lijf weren fillid; and he was anoyntid with swete smellynge spiceries, and was kept in a beere in Egipt.
Yusuf kuwa ya rasu yana da shekara ɗari da goma. Bayan an shafe shi da maganin hana ruɓa, sai aka sa shi a akwatin gawa a Masar.

< Genesis 50 >