< Genesis 49 >
1 Forsothe Jacob clepide hise sones, and seide to hem, Be ye gaderid that Y telle what thingis schulen come to you in the laste daies;
Sai Yaƙub ya kira’ya’yansa maza ya ce, “Ku tattaru don in faɗa muku abin da zai faru gare ku, a kwanaki masu zuwa.
2 be ye gaderid, `and here, ye sones of Jacob, here ye Israel youre fadir.
“Ku tattaru, ku saurara,’ya’yan Yaƙub maza; ku saurari mahaifinku, Isra’ila.
3 Ruben, my firste gendrid sone, thou art my strengthe and the bigynnyng of my sorewe; thou ouytist to be the former in yiftis, the more in lordschip;
“Ruben, kai ne ɗan farina, ƙarfina, alamar farko ta ƙarfina, mafi matsayi, kuma mafi iko.
4 thou art sched out as watir; wexe thou not, for thou stiedist on the bed of thi fader, and defoulidist his bed.
Mai tumbatsa kamar ruwa, amma ba za ka ƙara zama mai daraja ba, gama ka hau gadon mahaifinka ka hau kujerata, ka kuma ƙazantar da shi.
5 Symeon and Leuy, britheren, fiytynge vessils of wickidnesse;
“Simeyon da Lawi’yan’uwa ne, takubansu makamai ne na tā da hankali.
6 my soule come not in to the councel of hem, and my glorie be not in the congregacioun of hem; for in her woodnesse thei killiden a man, and in her wille thei myneden the wal;
Ba zan shiga shawararsu ba, ba zan shiga taronsu ba, gama sun kashe maza cikin fushinsu cikin ganin dama suka kashe bijimai.
7 curside be the woodnesse of hem, for it is obstynat, and the indignacioun of hem for it is hard; Y schal departe hem in Jacob, and I schal scatere hem in Israel.
La’ananne ne fushinsu, mai tsanani ne ƙwarai, hasalarsu kuwa, muguwa ce ƙwarai! Zan warwatsa su cikin Yaƙub in kuma daidaita su cikin Isra’ila.
8 Judas, thi britheren schulen preise thee, thin hondis schulen be in the nollis of thin enemyes; the sones of thi fadir schulen worschipe thee.
“Yahuda,’yan’uwanka za su yabe ka; hannuwanka za su kasance a wuyan abokan gābanka,’ya’yan mahaifinka maza za su rusuna maka.
9 `A whelp of lioun `is Judas; my sone thou stiedist to prey; thou restidist, and hast leyn as a lioun, and as a lionesse who schal reise hym?
Kai ɗan zaki ne, ya Yahuda, ka dawo daga farauta, ɗana. Kamar zaki, yakan kwanta a miƙe, kamar zakanya, wa yake da ƙarfin halin tashe shi?
10 The septre schal not be takun awey fro Juda, and a duyk of his hipe, til he come that schal be sent, and he schal be abiding of hethene men;
Kursiyi ba zai tashi daga Yahuda ba, ba kuwa sandan mulki daga tsakani ƙafafunsa ba, sai ya zo ga wanda yake mai shi. Biyayyar al’umma kuwa tasa ce.
11 and he schal tye his colt at the vyner, and his femal asse at the vyne; A! my sone, he schal waische his stoole in wyn, and his mentil in the blood of grape;
Zai daure jakinsa a kuringa, aholakinsa a rassa mafi kyau; zai wanke tufafinsa cikin ruwan inabi rigunansa cikin inabi ja wur kamar jini.
12 hise iyen ben fairere than wyn, and hise teeth ben whittere than mylk.
Idanunsa za su duhunce fiye da ruwan inabi, haƙorarsa farare kamar madara.
13 Zabulon schal dwelle in the brenk of the see, and in the stondyng of schipis; and schal stretche til to Sydon.
“Zebulun zai zauna a bakin teku, yă zama tasar jiragen ruwa; iyakarsa za tă nausa zuwa Sidon.
14 Isachar, a strong asse,
“Issakar doki mai ƙarfi, kwance tsakanin buhunan sirdi.
15 liggynge bitwixe termes, seiy reste, that it was good and seiy the lond that it was best, and he vndirsettide his schuldre to bere, and he was maad seruynge to tributis.
Sa’ad da ya ga yadda wurin hutunsa yana da kyau da kuma daɗin da ƙasarsa take, zan tanƙware kafaɗarsa ga nauyi yă miƙa kai ga aikin dole.
16 Dan schal deme his puple, as also another lynage in Israel.
“Dan zai tanada adalci wa mutanensa kamar ɗaya cikin kabilan Isra’ila.
17 Dan be maad a serpent in the weie, and cerastes in the path, and bite the feet of an hors, that the `stiere therof falle bacward; Lord,
Dan zai zama maciji a gefen hanya, kububuwa a bakin hanya, da take saran ɗiɗɗigen doki domin mahayinsa yă fāɗi da baya.
18 Y schal abide thin helthe.
“Ina zuba ido ga cetonka, ya Ubangiji.
19 Gad schal be gird, and schal fiyte bifor hym, and he schal be gird bihynde.
“Masu fashi za su fāɗa wa Gad, amma zai runtume su.
20 Aser his breed schal be plenteuouse, and he schal yyue delicis to kyngis.
“Abincin Asher zai zama a wadace, zai yi tanadin abinci iri-iri da suka dace don sarki.
21 Neptalym schal be an hert sent out, and yyuynge spechis of fairenesse.
“Naftali sakakkiyar barewa ce da take haihuwar kyawawan’ya’ya.
22 Joseph, a sone encreessynge, `a sone encresinge, and fair in biholdyng; douytris runnen aboute on the wal,
“Yusuf kuringa ce mai ba da amfani. Kuringa mai ba da amfani kusa da rafi wadda rassanta na hawan bango.
23 but hise brithren wraththeden hym, and chidden, and thei hadden dartis, and hadden enuye to hym.
Da ɗaci rai mahara suka fāɗa masa; suka harbe shi babu tausayi.
24 His bowe sat in the stronge, and the boondis of his armes, and hondis weren vnboundun bi the hond of the myyti of Jacob; of hym a scheepherd yede out, the stoon of Israel.
Amma bakansa yana nan daram hannuwansa masu ƙarfi ba sa jijjiguwa saboda hannun Maɗaukaki na Yaƙub, saboda Makiyayi, Dutsen Isra’ila,
25 God of thi fadir schal be thin helpere, and Almyyti God schal blesse thee with blessyngis of heuene fro aboue, and with blessyngis of the see liggynge binethe, with blessyngis of tetis, and of wombe;
saboda Allah na mahaifinka, wanda ya taimake ka, saboda Maɗaukaki, wanda yake albarkace ka da albarkar sama da take bisa albarkun zurfafa da suke ƙarƙashin ƙasa albarkun mama da kuma mahaifa.
26 the blessyngis of thi fadir ben coumfortid, the blessyngis of his fadris, til the desire of euerlastynge hillis cam; blessyngis ben maad in the heed of Joseph, and in the nol of Nazarei among his britheren.
Albarkun mahaifi suna da girma fiye da albarkun daɗaɗɗun duwatsu fiye da yalwar madawwaman tuddai. Bari dukan waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin ɗan sarki a cikin’yan’uwansa.
27 Beniamyn, a rauyschynge wolf, schal ete prey eerly, and in the euentid he schal departe spuylis.
“Benyamin kyarkeci ne mai kisa; da safe yakan cinye abin da ya farauto da yamma yakan raba ganima.”
28 Alle these weren in twelue kynredis of Israel; her fadir spak these thingys to hem, and blesside hem alle by propre blessyngis,
Dukan waɗannan su ne kabilu goma sha biyu na Isra’ila, kuma abin da mahaifinsu ya faɗa musu ke nan sa’ad da ya albarkace su, yana ba kowane albarkar da ta dace da shi.
29 and comaundide hem, and seide, Y am gaderid to my puple, birie ye me with my fadris in the double denne, which is in the lond of Efron Ethei, ayens Manbre,
Sa’an nan ya ba su waɗannan umarnai ya ce, “Ina gab da a tara ni ga mutanena. Ku binne ni tare da kakannina a kogon da yake cikin filin Efron mutumin Hitti,
30 in the lond of Canaan, which denne Abraham bouyte with the feeld of Efron Ethei, in to possessioun of sepulcre.
kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre a Kan’ana, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, yă zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
31 There thei birieden hym, and Sare his wijf, also Ysaac was biried there with Rebecca his wijf; there also Lia liggith biried.
A can aka binne Ibrahim da matarsa Saratu, a can aka binne Ishaku da matarsa Rebeka, a can kuma na binne Liyatu.
Filin tare da kogon da yake ciki, an saya daga Hittiyawa.”
33 And whanne the comaundementis weren endid, bi whiche he tauyte the sones, he gaderide hise feet on the bed, and diede, and he was put to his puple.
Sa’ad da Yaƙub ya gama ba da umarnan ga’ya’yansa maza, sai ya ɗaga ƙafafunsa zuwa gado, ya ja numfashinsa na ƙarshe, aka kuwa tara shi ga mutanensa.