< Genesis 4 >

1 Forsothe Adam knewe Eue his wijf, which conseyuede, and childide Cayn, and seide, Y haue gete a man bi God.
Adamu ya kwana da matarsa Hawwa’u, ta kuwa yi ciki ta haifi Kayinu. Sai ta ce, “Da taimakon Ubangiji na sami ɗa namiji.”
2 And efte sche childide his brother Abel. Forsothe Abel was a kepere of scheep, and Cayn was an erthe tilyere.
Daga baya ta haifi ɗan’uwansa, ta kuma ba shi suna Habila. Sa’ad da suka yi girma sai Habila ya zama makiyayin tumaki, Kayinu kuwa ya zama manomi.
3 Sotheli it was don after many daies, that Cayn offride yiftis to the Lord of the fruytis of erthe;
Ana nan sai Kayinu ya kawo waɗansu amfanin gona a matsayin hadaya ga Ubangiji.
4 and Abel offride of the first gendrid of his floc, and of the fatnesse of tho. And the Lord bihelde to Abel and to the yiftis of hym;
Amma Habila ya kawo mafi kyau daga’ya’yan fari na garkensa. Ubangiji ya yi farin ciki da sadakar da Habila ya kawo,
5 sotheli he bihelde not to Cayn and to hise yiftis. And Cayn was wrooth greetli, and his cheer felde doun.
amma bai yi farin ciki da sadakar da Kayinu ya kawo ba. Saboda haka Kayinu ya ji fushi sosai, fuskarsa kuma ta ɓace.
6 And the Lord seide to hym, Whi art thou wrooth, and whi felde doun thi face?
Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Don me kake fushi? Don me fuskarka ta ɓace?
7 Whether not if thou schalt do wel, thou schalt resseyue; but if thou doist yuele, thi synne schal be present anoon in the yatis? but the desir therof schal be vndur thee, and thou schalt be lord therof.
Da ka yi abin da yake daidai, ai, da ka sami karɓuwa. Amma tun da ba ka yi abin da ba daidai ba, zunubi zai yi fakonka don yă rinjaye ka kamar naman jeji. Yana so yă mallake ka, amma tilas ka rinjaye shi.”
8 And Cayn seide to Abel his brother, Go we out. And whanne thei weren in the feeld, Cayn roos ayens his brother Abel, and killide him.
To, Kayinu ya ce wa ɗan’uwansa Habila, “Mu tafi gona.” Yayinda suke a gona, sai Kayinu ya tasar wa Habila ya buge shi ya kashe.
9 And the Lord seide to Cayn, Where is Abel thi brother? Which answerde, Y woot not; whether Y am the kepere of my brothir?
Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Ina ɗan’uwanka Habila?” Sai Kayinu ya ce, “Ban sani ba, ni mai gadin ɗan’uwana ne?”
10 And God seide to Cayn, What hast thou do? the vois of the blood of thi brother crieth to me fro erthe.
Ubangiji ya ce, “Me ke nan ka yi? Saurara! Ga jinin ɗan’uwanka yana mini kuka daga ƙasa.
11 Now therfor thou schalt be cursid on erthe, that openyde his mouth, and resseyuede of thin hond the blood of thi brothir.
Yanzu, kai la’ananne ne, an kuma kore ka daga ƙasa wadda ta buɗe bakinta ta shanye jinin ɗan’uwanka daga hannunka.
12 Whanne thou schalt worche the erthe, it schal not yyue his fruytis to thee; thou schalt be vnstable of dwellyng and fleynge aboute on erthe in alle the daies of thi lijf.
In ka nome ƙasa, ba za tă ƙara ba ka hatsinta ba. Za ka kuma zama mai yawo barkatai a duniya.”
13 And Cayn seide to the Lord, My wickidnesse is more than that Y disserue foryyuenesse; lo!
Kayinu ya ce wa Ubangiji, “Horon nan ya sha ƙarfina.
14 to dai thou castist me out fro the face of the erthe; and Y schal be hid fro thi face, and Y schal be vnstable of dwellyng and fleynge aboute in erthe; therfore ech man that schal fynde me schal slee me.
Ga shi, yau kana kori na daga ƙasar, zan zama a ɓoye daga fuskarka, zan kuma zama mai yawo barkatai, duk wanda ya same ni kuwa zai kashe ni.”
15 And the Lord seide to hym, It schal not be don so, but ech man that schal slee Cayn shal be punyschid seuenfold. And the Lord settide a signe in Cayn, that ech man that schulde fynde hym schulde not slee hym.
Amma Ubangiji ya ce masa, “Ba haka ba ne! Duk wanda ya kashe Kayinu, za a ninƙa hukuncinsa har sau bakwai.” Sa’an nan Ubangiji ya sa wa Kayinu alama don duk wanda ya same shi kada yă kashe shi.
16 And Cayn yede out fro the face of the Lord, and dwellide fleynge aboute in erthe, at the eest coost of Eden.
Saboda haka Kayinu ya yi tafiyarsa ya rabu da Ubangiji, ya je ya zauna ƙasar Nod a gabashin Eden.
17 Forsothe Cayn knewe his wiif, which conseyuede, and childide Enoth; and Cayn bildide a citee, and clepide the name therof of the name of hise sone Enoth.
Kayinu ya kwana da matarsa, ta kuwa yi ciki, ta haifi Enok. A lokacin Kayinu yana gina birni, sai ya sa wa birnin sunan ɗansa Enok.
18 Forsothe Enoth gendride Irad, and Irad gendride Manyael, and Manyael gendride Matusael, and Matusael gendride Lameth;
Aka haifa wa Enok Irad, Irad kuma ya haifi Mehujayel, Mehujayel kuma ya haifi Metushayel, Metushayel kuma ya haifin Lamek.
19 that took twei wyues, the name to o wijf was Ada, and the name to the tother was Sella.
Lamek ya auri mata biyu, ana ce da ɗaya Ada, ɗayan kuma Zilla.
20 And Ada gendride Jabel, that was the fadir of dwellers in tentis and of shepherdis;
Ada ta haifi Yabal, shi ne mahaifi waɗanda suke zama a tentuna, suna kuma kiwon dabbobi.
21 and the name of his brother was Tubal, he was the fadir of syngeris in harpe and orgun.
Sunan ɗan’uwansa Yubal, shi ne mahaifin dukan makaɗan garaya da masu hura sarewa.
22 And Sella gendride Tubalcayn, that was an hamerbetere, and smyyt on alle werkis of bras and of yrun; forsothe the sistir of Tubalcayn was Neoma.
Zilla ma ta haifi ɗa, Tubal-Kayinu, shi ne wanda ya ƙera kowane iri kayan aiki daga tagulla da kuma ƙarfe.’Yar’uwar Tubal-Kayinu ita ce Na’ama.
23 And Lameth seide to his wyues Ada and Sella, Ye wyues of Lameth, here my vois, and herkne my word; for Y haue slayn a man bi my wounde, and a yong wexynge man bi my `violent betyng;
Wata rana, Lamek ya ce wa matansa, Ada da Zilla, “Ku saurara, matan Lamek, ku ji maganata. Na kashe wani saboda ya yi mini rauni, na kashe wani saurayi saboda ya ji mini ciwo.
24 veniaunce schal be youun seuenfold of Cayn, forsothe of Lameth seuentisithis seuensithis.
Idan za a rama wa Kayinu har sau bakwai, lalle za a rama wa Lamek sau saba’in da bakwai ke nan.”
25 Also yit Adam knewe his wijf, and sche childide a sone, and clepide his name Seth, and seide, God hath put to me another seed for Abel, whom Cayn killide.
Sai Adamu ya sāke kwana da matarsa, ta haifi ɗa, aka kuma ba shi suna Set, gama ta ce, “Allah ya ba ni wani yaro a madadin Habila, tun da yake Kayinu ya kashe shi.”
26 But also a sone was borun to Seth, which sone he clepide Enos; this Enos bigan to clepe inwardli the name of the Lord.
Set ma ya haifi ɗa, ya kuma kira shi Enosh. A lokaci ne, mutane suka fara kira ga sunan Ubangiji.

< Genesis 4 >