< Genesis 31 >

1 Aftir that Jacob herde the wordis of the sones of Laban, that seiden, Jacob hath take awei alle thingis that weren oure fadris, and of his catel Jacob is maad riche, and noble.
Yaƙub ya ji cewa’ya’ya Laban mazan suna cewa, “Yaƙub ya kwashe dukan abin da mahaifinmu yake da shi, ya kuma sami dukan wannan arziki daga abin da yake na mahaifinmu.”
2 Also Jacob perseyuede the face of Laban, that it was not ayens hym as yistirdai, and the thridde dai agoon,
Yaƙub kuma ya lura cewa halin Laban gare shi ya canja ba kamar yadda yake a dā ba.
3 moost for the Lord seide to hym, Turne ayen into the lond of thi fadris, and to thi generacioun, and Y shal be with thee.
Sai Ubangiji ya ce wa Yaƙub, “Koma ƙasar kakanninka da kuma danginka, zan kuwa kasance tare da kai.”
4 He sente, and clepide Rachel, and Lya, in to the feeld, where he kepte flockis, and he seide to hem,
Saboda haka Yaƙub ya aika a ce wa Rahila da Liyatu su zo jeji inda garkunan suke.
5 Y se the face of youre fadir, that it is not ayens me as `yisterdai and the thridde dai agoon; but God of my fadir was with me.
Sai ya ce musu, “Na ga cewa halin mahaifinku gare ni ba kamar yadda dā yake ba, amma Allah na mahaifina yana tare da ni.
6 And ye witen that with alle my strengthis Y seruede youre fadir;
Kun san cewa na yi aiki wa mahaifinku da dukan ƙarfina,
7 but and youre fadir disseyuyde me, and chaungide my meede ten sithis; and netheles God suffride not hym to anoye me.
duk da haka mahaifinku ya cuce ni ta wurin sauya albashina sau goma. Amma dai, Allah bai yardar masa yă yi mini lahani ba.
8 If he seide ony tyme, Dyuerse colourid sheep schulen be thi medis, alle sheep brouyten forth dyuerse colourid lambren; forsothe whanne he seide ayenward, Thou shalte take alle white for mede, alle the flockis brouyten forth white beestis;
In ya ce, ‘Dabbare-dabbare ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi dabbare-dabbare, in kuma ya ce, ‘Masu zāne-zāne ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi ƙananan masu zāne-zāne.
9 and God took a wey the substaunce of youre fadir, and yaf to me.
Ta haka Allah ya kwashe dabbobin mahaifinku ya ba ni.
10 For aftir that the tyme of conseyuyng of sheep cam, Y reiside myn iyen, and seiy in sleep malis dyuerse, and spotti, and of dyuerse colouris, stiynge on femalis.
“A lokacin ɗaukar cikin garken, na taɓa yin mafarki inda na ga bunsuran da suke barbara da garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne.
11 And the aungel of the Lord seide to me in sleep, Jacob! and Y answeride, Y am redy.
Sai mala’ikan Allah ya ce mini a mafarkin, ‘Yaƙub.’ Sai na amsa na ce, ‘Ga ni.’
12 Which seide, Reise thin iyen, and se alle malis dyuerse, byspreynt, and spotti, stiynge on femalis; for Y seiy alle thingis whiche Laban dide to thee;
Ya ce, ‘Ɗaga idanunka ka gani, dukan bunsuran da suke hawan garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne, gama na ga dukan abin da Laban yake yin maka.
13 Y am God of Bethel, where thou anoyntidist a stoon, and madist auow to me. Now therefor rise thou, and go out of this lond, and turne ayen in to the lond of thi birthe.
Ni ne Allah na Betel, inda ka zuba wa al’amudi mai, da kuma inda ka yi mini alkawari. Yanzu ka bar wannan ƙasa nan take, ka koma ƙasarka ta ainihi.’”
14 And Rachel and Lya answeriden, Wher we han ony thing residue in the catels, and eritage of oure fadir?
Sai Rahila da Liyatu suka amsa suka ce, “Muna da wani rabo a gādon kayan mahaifinmu ne?
15 Wher he `arettide not vs as aliens, and selde, and eet oure prijs?
Ba kamar baƙi ne yake ɗaukarmu ba? Ba sayar da mu kaɗai ya yi ba, har ma ya yi amfani da abin da aka biya saboda mu.
16 But God took awei the richessis of oure fadir, and yaf tho to vs, and to oure sones; wherfor do thou alle thingis whiche God hath comaundide to thee.
Tabbatacce dukan dukiyar da Allah ya kwashe daga mahaifinmu ya zama namu da’ya’yanmu. Saboda haka ka yi duk abin da Allah ya faɗa maka.”
17 Forsothe Jacob roos, and puttide hise fre children and wyues on camels, and yede forth;
Sa’an nan Yaƙub ya sa’ya’yansa da matansa a kan raƙuma,
18 and he took al his catel, flockis, and what euer thing he hadde gete in Mesopotanye, and yede to Isaac, his fadir, into the lond of Canaan.
ya kuma kora dukan dabbobinsa, suka ja gabansa, tare da dukan abubuwan da ya samu a Faddan Aram, don su tafi wurin mahaifinsa Ishaku a ƙasar Kan’ana.
19 In that tyme Laban yede to schere scheep, and Rachel stal the idols of hir fadir.
Sa’ad da Laban ya tafi don askin tumakinsa, sai Rahila ta sace gumakan gidan mahaifinta.
20 And Jacob nolde knouleche to the fadir of his wijf, that he wolde fle;
Yaƙub kuwa ya ruɗe Laban mutumin Aram da bai sanar da shi zai gudu ba.
21 and whanne he hadde go, as wel he as alle thingis that weren of his riyt, and whanne he hadde passid the water, and he yede ayens the hil of Galaad,
Saboda haka ya gudu da dukan abin da ya mallaka, ya ƙetare Kogi, ya nufi yankin tuddan Gileyad.
22 it was teld to Laban, in the thridde dai, that Jacob fledde.
A rana ta uku, sai aka faɗa wa Laban cewa Yaƙub ya gudu.
23 And Laban took his britheren, and pursuede hym seuene daies, and took hym in the hil of Galaad.
Sai Laban ya ɗauki danginsa tare da shi, ya bi bayan Yaƙub har kwana bakwai, ya kuma same shi a yankin tuddan Gileyad.
24 And Laban seiy in sleep the Lord seiynge to him, Be war that thou speke not ony thing sharpli ayens Jacob.
Sai Allah ya bayyana ga Laban mutumin Aram a mafarki da dare, ya ce masa, “Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu, ko mai kyau ko marar kyau.”
25 And thanne Jacob hadde stretchid forth the tabernacle in the hil; and whanne he hadde sued Jacob with his britheren, `he settide tente in the same hil of Galaad; and he seide to Jacob,
Yaƙub ya riga ya kafa tentinsa a yankin tuddan Gileyad sa’ad da Laban ya same shi. Laban da danginsa suka kafa sansani a can su ma.
26 Whi hast thou do so, that the while I wiste not thou woldist dryue awey my douytris as caitifs by swerd?
Sai Laban ya ce wa Yaƙub, “Me ke nan ka yi? Ka ruɗe ni, ka kuma ɗauki’ya’yana mata kamar kamammun yaƙi.
27 Whi woldist thou fle the while Y wiste not, nether woldist shewe to me, that Y shulde sue thee with ioie, and songis, and tympans, and harpis?
Me ya sa ka gudu a ɓoye ka kuma ruɗe ni? Me ya sa ba ka faɗa mini don in sallame ka da farin ciki da waƙoƙi haɗe da kiɗin ganguna da garayu ba?
28 Thou suffridist not that Y schulde kisse my sones and douytris; thou hast wrouyt folili.
Ba ka ma bari in sumbaci jikokina da’ya’yana mata in yi musu bankwana ba. Ka yi wauta.
29 And now sotheli myn hond mai yelde yuel to thee, but the God of thi fadir seide to me yisterdai, Be war that thou speke not ony harder thing with Jacob.
Ina da iko in cuce ka; amma jiya da dare Allahn mahaifinka ya faɗa mini, ‘Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu ko mai kyau ko marar kyau.’
30 Suppose, if thou coueitedist to go to thi kynesmen, and the hows of thi fadir was in desir to thee, whi hast thou stole my goddis?
Yanzu ka gudu domin kana marmari komawa gidan mahaifinka. Amma don me ka sace mini gumakana?”
31 Jacob answeride, That Y yede forth while thou wistist not, Y dredde lest thou woldist take awey thi douytris violentli;
Yaƙub ya amsa wa Laban, “Na ji tsoro ne, domin na yi tsammani za ka ƙwace’ya’yanka mata daga gare ni ƙarfi da yaji.
32 sotheli that thou repreuest me of thefte, at whom euer thou fyndist thi goddis, be he slayn bifor oure britheren; seke thou, what euer thing of thine thou fyndist at me, and take awei. Jacob seide these thingis, and wiste not that Rachel stal the idols.
Amma in ka sami wani wanda yake da gumakanka, ba zai rayu ba. Kai da kanka ka duba a gaban danginmu, ko akwai wani abin da yake naka a nan tare da ni; in ka gani, ka ɗauka.” Yaƙub dai bai san cewa Rahila ta sace gumakan ba.
33 And so Laban entride into the tabernacle of Jacob, and of Lya, and of euer eithir meyne, and foond not; and whanne Laban hadde entrid in to the tente of Rachel,
Saboda haka Laban ya shiga tentin Yaƙub, ya shiga tentin Liyatu da kuma tentuna matan nan biyu bayi, amma bai sami kome ba. Bayan ya fita daga tentin Liyatu, sai ya shiga tentin Rahila.
34 sche hastide, and hidde the idols vndur the strewyngis of the camel, and sat aboue. And sche seide to Laban, sekynge al the tente and fyndynge no thing,
Rahila fa ta kwashe gumakan gidan ta sa su cikin sirdin raƙumi, ta kuma zauna a kansu. Laban ya bincika cikin kowane abu a tentin amma bai sami kome ba.
35 My lord, be not wrooth that Y may not rise bifore thee, for it bifelde now to me bi the custom of wymmen; so the bisynesse of the sekere was scorned.
Sai Rahila ta ce wa mahaifinta, “Kada ka yi fushi, ranka yă daɗe da ban tashi tsaye a gabanka ba; gama ina al’adar mata ne.” Saboda haka ya bincika amma bai sami gumakan gidan ba.
36 And Jacob bolnyde, and seide with strijf, For what cause of me, and for what synne of me, hast thou come so fersly aftir me,
Yaƙub ya fusata, ya kuma yi wa Laban faɗa. Ya tambayi Laban, “Mene ne laifina? Wanda zunubi na yi da kake farautata?
37 and hast souyt al `the portenaunce of myn hous? What `hast thou founde of al the catel of thin hows? Putte thou here bifore my britheren and thi britheren, and deme thei betwixe me and thee.
Yanzu da ka bincika dukan kayayyakina, me ka samu da yake na gidanka? Kawo shi nan a gaban danginka da kuma dangina, bari su zama alƙali tsakaninmu biyu.
38 Was I with thee herfore twenti yeer? Thi sheep and geet weren not bareyn, Y eet not the rammes of thi flok,
“Na kasance tare da kai shekaru ashirin. Tumakinka da awakinka ba su yi ɓarin ciki ba, ban kuwa ci raguna daga garkunanka ba.
39 nether Y schewide to thee ony thing takun of a beeste; Y yeldide al harm; what euer thing perischide bi thefte, thou axidist of me;
Ban kawo dabbobinka da namun jeji suka yayyaga; na kuma ɗauki hasarar ba? Ka nemi in biya dukan abin da aka sace da rana ko da dare.
40 Y was angwischid in dai and nyyt with heete and frost, and sleep fledde fro myn iyen;
Yanayin da na kasance ke nan, da rana na sha zafin rana da dare kuma na sha sanyi, ga rashin barci.
41 so Y seruede thee bi twenti yeer in thin hows, fourtene yeer for thi douytris, and sixe yeer for thi flockis; and thou chaungidist my mede ten sithis.
Haka ya kasance shekaru ashirin da na yi a gidanka. Na yi maka aiki shekaru goma sha huɗu domin’ya’yanka mata biyu, na kuma yi shekaru shida domin garkunanka, ka kuma canja albashina sau goma.
42 If God of my fadir Abraham, and the drede of Isaac hadde not helpid me, perauenture now thou haddist left me nakid; the Lord bihelde my turmentyng and the traueyl of myn hondis, and repreuyde thee yistirdai.
Da ba don Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim da kuma Tsoron Ishaku ya kasance tare da ni ba, tabbatacce da ka sallame ni hannu wofi. Amma Allah ya ga wahalata da famar hannuwana, ya kuwa tsawata maka da dare jiya.”
43 Laban answeride hym, The douytris, and thi sones, and flockis, and alle thingis whiche thou seest, ben myne, what mai Y do to my sones, and to the sones of sones?
Laban ya amsa wa Yaƙub, “Matan,’ya’yana ne,’ya’yansu,’ya’yana ne, garkunan kuma garkunana ne. Dukan abin da kake gani, nawa ne. Duk da haka me zan yi a rana ta yau ga waɗannan’ya’yana mata, ko kuma ga’ya’yan da suka haifa?
44 Therfor come thou, and make we boond of pees, that it be witnessyng bitwixe me, and thee.
Zo, bari mu ƙulla yarjejjeniya, da kai da ni, bari kuma ta kasance shaida a tsakaninmu.”
45 And so Jacob took a stoon, and reiside it in to a signe, and seide to hise britheren,
Saboda haka Yaƙub ya ɗauki dutse ya kafa yă zama al’amudi.
46 Brynge ye stoonus; whiche gadriden, and maden an heep, and eten on it.
Ya ce wa danginsa. “Ku tattara waɗansu duwatsu.” Sai suka kwashe duwatsu suka tsiba, suka kuwa ci abinci a can kusa da tsibin.
47 And Laban clepide it the heep of wittnesse, and Jacob clepide it the heep of witnessyng; euer eithir clepide bi the proprete of his langage.
Laban ya sa masa suna Yegar Sahaduta, Yaƙub kuwa ya kira shi Galeyed.
48 And Laban seide, This heep schal be witnesse bytwixe me and thee to day, and herfor the name therof was clepid Galaad, that is, the heep of witnesse.
Laban ya ce, “Wannan tsibi, shi ne shaida tsakaninka da ni a yau.” Shi ya sa aka kira shi Galeyed.
49 And Laban addide, The Lord biholde, and deme bitwixe vs, whanne we schulen go awei fro yow;
Aka kuma kira shi Mizfa, domin ya ce, “Ubangiji yă sa ido tsakanin ni da kai sa’ad da muka rabu da juna.
50 if thou schalt turmente my douytris, and if thou schal brynge yn othere wyues on hem, noon is witnesse of oure word, outakun God, whiche is present, and biholdith.
Laban ya ce in ka wulaƙanta’ya’yana mata, ko ka auri waɗansu mata ban da’ya’yana mata, ko da yake babu wani da yake tare da mu, ka tuna cewa Allah shi ne shaida tsakaninka da ni.”
51 And eft he seide to Jacob, Lo! this heep, and stoon, whiche Y reiside bitwixe me and thee, schal be witnesse;
Laban ya kuma ce wa Yaƙub, “Ga wannan tsibi, ga kuma wannan al’amudin da na kafa tsakaninka da ni.
52 sotheli this heep, and stoon be in to witnessyng, forsothe if Y schal passe it, and go to thee, ether thou shalt passe, and thenke yuel to me.
Wannan tsibin shi ne shaida, wannan al’amudi kuma shaida ne, cewa ba zan tsallake wannan tsibi zuwa gefenka don in cuce ka ba, kai kuma ba za ka tsallake wannan tsibi da al’amudi zuwa gefena don ka cuce ni ba.
53 God of Abraham, and God of Nachor, God of the fadir of hem, deme bitwixe vs. Therfor Jacob swoor by the drede of his fadir Ysaac;
Bari Allah na Ibrahim da Allah na Nahor, Allah na iyayensu, yă zama alƙali tsakaninmu.” Saboda haka Yaƙub ya yi rantsuwa da sunan Tsoron mahaifinsa Ishaku.
54 and whanne slayn sacrifices weren offrid in the hil, he clepyde his britheren to ete breed, and whanne thei hadden ete, thei dwelliden there.
Ya miƙa hadaya a can a ƙasar tudu, ya kuma gayyaci danginsa zuwa wurin cin abinci. Bayan suka ci, sai suka kwana a can.
55 Forsothe Laban roos bi nyyt, and kisside his sones, and douytris, and blesside hem, and turnede ayen in to his place.
Da sassafe kashegari sai Laban ya sumbaci jikokinsa da’ya’yansa mata, ya sa musu albarka. Sa’an nan ya yi bankwana da su, ya koma gida.

< Genesis 31 >