< Genesis 29 >

1 Therfor Jacob passide forth, and cam in to the eest lond;
Sa’an nan Yaƙub ya ci gaba da tafiyarsa har ya kai ƙasar mutanen gabashi.
2 and seiy a pit in the feeld, and thre flockis of scheep restynge bisidis it, for whi scheep weren watrid therof, and the mouth therof was closid with a greet stoon.
A can ya ga rijiya a jeji da garkuna uku na tumaki kwance kusa da ita, gama a wannan rijiya ce ake shayar da garkuna. Dutsen da ake rufe bakin rijiyar mai girma ne.
3 And the custom was that whanne alle scheep weren gaderid togidere, thei schulden turne awei the stoon, and whanne the flockis weren fillid thei schulden put it eft on the mouth of the pit.
Sa’ad da dukan garkuna suka taru a can, sai makiyayan su gungurar da dutsen daga bakin rijiyar su shayar da tumaki. Sa’an nan su mai da dutsen a wurinsa a bakin rijiya.
4 And Jacob seide to the scheepherdis, Brithren, of whennus ben ye? Whiche answeriden, Of Aran.
Yaƙub ya tambayi makiyayan ya ce, “’Yan’uwa, ina kuka fito?” Suka amsa, “Mu daga Haran ne.”
5 And he axide hem and seide, Wher ye knowen Laban, the sone of Nachor? Thei seiden, We knowen.
Sai ya ce musu, “Kun san Laban, jikan Nahor?” Suka amsa, “I, mun san shi.”
6 Jacob seide, Is he hool? Thei seiden, He is in good staat; and lo! Rachel, his douytir, cometh with his flok.
Sa’an nan Yaƙub ya tambaye su, “Yana nan lafiya?” Suka ce, “I, yana lafiya, ga ma’yarsa Rahila tafe da tumaki.”
7 And Jacob seide, Yit myche of the dai is to come, and it is not tyme that the flockis be led ayen to the fooldis; sotheli yyue ye drynk to the scheep, and so lede ye hem ayen to mete.
Ya ce, “Duba har yanzu da sauran rana da yawa, lokaci bai kai na tara garkuna ba. Ku shayar da tumaki ku mai da su wurin kiwo.”
8 Whiche answeriden, We moun not til alle scheep be gederid to gidere, and til we remouen the stoon fro the mouth of the pit to watir the flockis.
Suka amsa suka ce, “Ba za mu iya ba, sai dukan garkunan sun taru, aka kuma gungurar da dutsen daga bakin rijiyar. Sa’an nan za mu shayar da tumakin.”
9 Yit thei spaken, and lo! Rachel cam with the scheep of hir fadir.
Tun yana cikin magana da su, sai ga Rahila ta zo da tumakin mahaifinta, gama ita makiyayyiya ce.
10 And whanne Jacob seiy hir, and knewe the douytir of his modris brothir, and the scheep of Laban his vncle, he remeuyde the stoon with which the pit was closid;
Sa’ad da Yaƙub ya ga Rahila’yar Laban, ɗan’uwan mahaifiyarsa, da tumakin Laban, sai ya tafi ya gungurar da dutsen daga bakin rijiyar, ya kuma shayar da tumakin kawunsa.
11 and whanne the flok was watrid, he kisside hir, and he wepte with `vois reisid.
Sa’an nan Yaƙub ya sumbaci Rahila, ya kuma ɗaga murya ya yi kuka.
12 And he schewide to hir that he was the brothir of hir fadir, and the sone of Rebecca; and sche hastide, and telde to hir fadir.
Ya riga ya faɗa wa Rahila cewa shi dangin mahaifinta ne kuma ɗan Rebeka. Saboda haka ta ruga da gudu ta faɗa wa mahaifinta.
13 And whanne he hadde herd, that Jacob, the sone of his sistir, cam, he ran ayens hym, and he biclippide Jacob and kisside hym, and ledde in to his hows. Forsothe whanne the causis of the iurney weren herd,
Nan da nan, da Laban ya sami labari game da Yaƙub, ɗan’yar’uwarsa, ya gaggauta yă sadu da shi. Sai ya rungume shi ya sumbace shi, ya kuma kawo shi gidansa, a can kuwa Yaƙub ya faɗa masa dukan waɗannan abubuwa.
14 Laban answeride, Thou art my boon and my fleisch. And aftir that the daies of o moneth weren fillid, Laban seide to him,
Sa’an nan Laban ya ce masa, “Kai nama da jinina ne.” Bayan Yaƙub ya zauna da shi na wata guda cif,
15 `Whethir for thou art my brothir, thou schalt serue me frely? seie thou what mede thou schalt take.
sai Laban ya ce masa, “Don kawai kai dangina ne na kusa, sai kawai ka yi mini aiki a banza? Faɗa mini abin da albashinka zai zama.”
16 Forsothe Laban hadde twei douytris, the name of the more was Lya, sotheli the lesse was clepid Rachel;
Laban dai yana da’ya’ya mata biyu; sunan babbar Liyatu, sunan ƙaramar kuwa Rahila.
17 but Lya was blere iyed, Rachel was of fair face, and semeli in siyt.
Liyatu tana da raunannun idanu, amma Rahila dai tsarinta yana da kyau kuma kyakkyawa ce.
18 And Jacob louede Rachel, and seide, Y schal serue thee seuene yeer for Rachel thi lesse douytir.
Yaƙub ya ƙaunaci Rahila, sai ya ce, “Zan yi maka aiki na shekaru bakwai domin ƙaramar’yarka Rahila.”
19 Laban answeride, It is betere that Y yyue hir to thee than to anothir man; dwelle thou at me.
Laban ya ce, “Ya fi kyau in ba ka ita, da in ba wani mutum dabam. Zauna tare da ni.”
20 Therfor Jacob seruyde seuene yeer for Rachel; and the daies semyden fewe to hym for the greetnesse of loue.
Saboda haka Yaƙub ya yi bauta shekaru bakwai domin a ba shi Rahila, amma shekarun suka zama kamar’yan kwanaki ne kawai gare shi saboda ƙaunar da yake mata.
21 And he seide to Laban, Yyue thou my wijf to me, for the tyme is fillid that Y entre to hir.
Sa’an nan Yaƙub ya ce wa Laban, “Ba ni matata. Lokacina ya cika, ina kuma so in kwana da ita.”
22 And whanne many cumpenyes of freendis weren clepid to the feeste, he made weddyngis,
Saboda haka Laban ya tara dukan mutanen wurin, ya yi biki.
23 and in the euentid Laban brouyte in to hym Lya his douytir,
Amma da yamma ta yi, sai ya ɗauki’yarsa Liyatu ya ba da ita ga Yaƙub, sai Yaƙub ya kwana da ita.
24 and yaf an handmaide, Selfa bi name, to the douyter. And whanne Jacob hadde entrid to hir bi custom, whanne the morewtid was maad, he seiy Lya,
Laban kuma ya ba da baranyarsa Zilfa wa’yarsa tă zama mai hidimarta.
25 and seide to his wyues fadir, What is it that thou woldist do? wher Y seruede not thee for Rachel? whi hast thou disseyued me?
Sa’ad da safiya ta yi, sai ga Liyatu! Saboda haka Yaƙub ya ce wa Laban, “Mene ne ke nan ka yi mini? Na yi maka bauta domin Rahila, ba haka na yi ba? Don me ka ruɗe ni?”
26 Laban answerde, It is not custom in oure place that we yyue first the `lesse douytris to weddyngis;
Laban ya amsa, “Ba al’adarmu ba ce a nan a ba da’ya ƙarama aure kafin’yar fari.
27 fille thou the wouke of daies of this couplyng, and Y schal yyue to thee also this Rachel, for the werk in which thou schalt serue me bi othere seuene yeer.
Ka gama makon amaryanci na’yar nan; sa’an nan za mu ba ka ƙaramar ita ma, don ƙarin waɗansu shekaru bakwai na aiki.”
28 Jacob assentide to the couenaunt, and whanne the wouke was passid,
Haka kuwa Yaƙub ya yi. Ya gama mako guda da Liyatu, sa’an nan Laban ya ba shi’yarsa Rahila tă zama matarsa.
29 he weddide Rachel, to whom the fadir hadde youe Bala seruauntesse.
Laban ya ba da baranyarsa Bilha wa’yarsa Rahila ta zama mai hidimarta.
30 And at the laste he vside the weddyngis desirid, and settide the loue of the `wijf suynge bifore the former; and he seruede at Laban seuene othere yeer.
Yaƙub ya kwana da Rahila ita ma, ya kuwa ƙaunaci Rahila fiye da Liyatu. Ya kuma yi wa Laban aiki na ƙarin waɗansu shekaru bakwai.
31 Forsothe the Lord seiy that he dispiside Lya, and openyde hir wombe while the sistir dwellide bareyn.
Sa’ad da Ubangiji ya ga ba a ƙaunar Liyatu, sai ya buɗe mahaifarta, amma Rahila ta zama bakararriya.
32 And Lia childide a sone conseyued, and clepide his name Ruben, and seide, The Lord seiy my mekenesse; now myn hosebonde schal loue me.
Sai Liyatu ta yi ciki ta haifi ɗa. Ta sa masa suna Ruben, gama ta ce, “Domin Ubangiji ya ga wahalata. Tabbatacce mijina zai ƙaunace ni yanzu.”
33 And eft sche conseyuede, `and childide a sone, and seide, For the Lord seiy that Y was dispisid, he yaf also this sone to me; and sche clepide his name Symeon.
Ta sāke yin ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Gama Ubangiji ya ji cewa ba a ƙaunata, ya ba ni wannan shi ma.” Saboda haka ta ba shi suna Simeyon.
34 And sche conseyuede the thridde tyme, and childide anothir sone, and she seide also, Now myn hosebonde schal be couplid to me, for Y childide thre sones to him; and therfor sche clepide his name Leuy.
Har yanzu ta yi ciki, sa’ad da kuma ta haifi ɗa sai ta ce, “Yanzu, a ƙarshe mijina zai manne mini, gama na haifa masa’ya’ya maza uku.” Saboda haka ta ba shi suna Lawi.
35 The fourthe tyme sche conseyuede, and childide a sone, and seide, Now I schal knouleche to the Lord; and herfor she clepide his name Judas; and ceesside to childe.
Ta sāke yin ciki, sa’ad da ta haifi ɗa sai ta ce, “A wannan lokaci zan yabi Ubangiji.” Saboda haka ta ba shi suna Yahuda. Sa’an nan ta daina haihuwa.

< Genesis 29 >