< Genesis 27 >

1 Forsothe Isaac wexe eld, and hise iyen dasewiden, and he miyte not se. And he clepide Esau, his more sone, and seide to hym, My sone! Which answerde, Y am present.
Sa’ad da Ishaku ya tsufa idanunsa suka raunana har ba ya iya gani, sai ya kira Isuwa babban ɗansa ya ce masa, “Ɗana.” Isuwa kuwa ya amsa, ya ce “Ga ni.”
2 To whom the fadir seide, Thou seest that Y haue woxun eld, and Y knowe not the dai of my deeth.
Ishaku ya ce, “Yanzu na tsufa kuma ban san ranar mutuwata ba.
3 Take thin armeres, `arewe caas, and a bowe, and go out; and whanne thou hast take ony thing bi huntyng,
Saboda haka yanzu, ka ɗauki makamanka, kwari da bakanka, ka tafi jeji ka farauto mini nama.
4 make to me a seew therof, as thou knowist that Y wole, and brynge that Y ete, and my soule blesse thee bifore that Y die.
Ka shirya mini irin abinci mai daɗin da nake so, ka kawo mini in ci, domin in sa maka albarka kafin in mutu.”
5 And whanne Rebecca hadde herd this thing, and he hadde go in to the feeld to fille the comaundment of the fadir,
Ashe, Rebeka tana ji sa’ad da Ishaku ya yi wa ɗansa Isuwa magana. Da Isuwa ya tafi jeji don yă farauto nama yă kawo,
6 sche seide to hir sone Jacob, Y herde thi fadir spekynge with Esau, thi brothir, and seiynge to him, Brynge thou me of thin huntyng,
sai Rebeka ta ce wa ɗanta Yaƙub, “Ka ji nan, na ji mahaifinka ya ce wa ɗan’uwanka Isuwa,
7 and make thow metis, that Y ete, and that Y blesse thee bifor the Lord bifor that Y die.
‘Kawo mini nama ka shirya mini abinci mai daɗi don in ci, in sa maka albarka a gaban Ubangiji kafin in mutu.’
8 Now therfor, my sone, assent to my counsels,
Saboda haka ɗana, ka saurara da kyau ka kuma yi abin da na faɗa maka.
9 and go to the floc, and brynge to me tweyne the beste kidis, that Y make metis of tho to thi fadir, whiche he etith gladli;
Je garke ka kawo mini awaki biyu kyawawa, domin in shirya abinci mai daɗi wa mahaifinka, kamar yadda dai yake so.
10 and that whanne thow hast brouyt in tho metis, and he hath ete, he blesse thee bifore that he die.
Sa’an nan ka kai wa mahaifinka yă ci, domin yă sa maka albarka kafin yă mutu.”
11 To whom Jacob answerde, Thou knowist that Esau my brother is an heeri man, and Y am smethe; if my fadir `touchith and feelith me,
Yaƙub ya ce wa mahaifiyarsa Rebeka, “Amma ɗan’uwana Isuwa mutum ne mai gashi a jiki, ni kuma jikina sumul yake.
12 Y drede lest he gesse that Y wolde scorne him, and lest he brynge in cursyng on me for blessyng.
A ce baba ya tattaɓa ni fa? Zai zama kamar ina ruɗunsa ne, wannan fa zai jawo mini la’ana a maimakon albarka.”
13 To whom the modir seide, My sone, this cursyng be in me; oonly here thou my vois, and go, and brynge that that Y seide.
Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, bari la’anar tă fāɗo a kaina. Kai dai yi abin da na faɗa, jeka ka kawo mini su.”
14 He yede, and brouyte, and yaf to his modir. Sche made redi metis, as sche knewe that his fadir wolde,
Sai ya tafi ya kamo su, ya kawo wa mahaifiyarsa, ta kuwa shirya abinci mai daɗi, yadda mahaifinsa yake so.
15 and sche clothide Jacob in ful goode clothis of Esau, whiche sche hadde at home anentis hir silf.
Sa’an nan Rebeka ta ɗauki riguna mafi kyau na Isuwa babban ɗanta, waɗanda take da su a gida ta sa wa ƙaramin ɗanta Yaƙub.
16 And sche `compasside the hondis with litle skynnys of kiddis, and kyuerede the `nakide thingis of the necke;
Sai ta mamanne gashin awakin nan biyu a hannuwansa da bayan wuyarsa wanda ba gashi.
17 and sche yaf seew, and bitook the loouys whiche sche hadde bake.
Sa’an nan ta ba wa ɗanta Yaƙub abinci mai daɗi da kuma burodin da ta yi.
18 And whanne these weren brouyt in, he seide, My fadir! And he answerde, Y here; who art thou, my sone?
Shi kuwa ya tafi wurin mahaifinsa ya ce, “Babana.” Shi kuma ya amsa “I, ɗana, wane ne?”
19 And Jacob seide, Y am Esau, thi first gendrid sone. Y haue do to thee as thou comaundist to me; rise thou, sitte, and ete of myn huntyng, that thi soule blesse me.
Yaƙub ya ce wa mahaifinsa, “Ni ne Isuwa ɗan farinka. Na yi yadda ka faɗa mini. Ina roƙonka tashi ka zauna ka ci naman, domin ka sa mini albarkarka.”
20 Eft Ysaac seide to his sone, My sone, hou miytist thou fynde so soone? Which answerde, It was Goddis wille, that this that Y wolde schulde come soone to me.
Ishaku ya tambayi ɗansa, “Yaya aka yi ka samo shi da sauri haka, ɗana?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Ubangiji Allahnka ne ya ba ni nasara.”
21 And Isaac seide, My sone, come thou hidir, that Y touche thee, and that Y preue wher thou art my sone Esau, ethir nay.
Sai Ishaku ya ce wa Yaƙub, “Zo kusa don in taɓa ka, ɗana, domin in sani ko tabbatacce kai ne ɗana Isuwa ko babu.”
22 He neiyede to the fadir; and whanne he hadde feelid hym, Isaac seide, Sotheli the vois is the vois of Jacob, but the hondis ben the hondis of Esau.
Yaƙub kuwa ya matsa kusa da mahaifinsa Ishaku, wanda ya tattaɓa shi, sa’an nan ya ce, “Muryan nan dai, muryar Yaƙub ce, amma hannuwan, hannuwan Isuwa ne.”
23 And Isaac knew not Jacob, for the heery hondis expressiden the licnesse of the more sone.
Bai gane shi ba, gama hannuwansa suna da gashi kamar na ɗan’uwansa Isuwa, saboda haka ya albarkace shi.
24 Therfor Isaac blesside him, and seide, Art thou my sone Esau? Jacob answerde, Y am.
Ya tambaya, “Tabbatacce kai ne ɗana Isuwa?” Ya amsa ya ce “Ni ne.”
25 And Isaac seide, My sone, brynge thou to me metis of thin huntyng, that my soule blesse thee. And whanne Isaac hadde ete these metis brouyt, Jacob brouyte also wyn to Isaac, and whanne this was drunkun,
Sa’an nan ya ce, “Ɗana, kawo mini naman da ka farauto in ci, domin in sa maka albarka.” Yaƙub ya kawo masa ya kuwa ci; ya kuma kawo masa ruwan inabi ya kuma sha.
26 Isaac seide to him, My sone, come thou hidir, and yyue to me a cos.
Sa’an nan mahaifinsa Ishaku ya ce masa, “Zo nan, ɗana ka sumbace ni.”
27 Jacob neiyede, and kisside hym; and anoon as Isaac feelide the odour of hise clothis, he blesside him, and seide, Lo! the odour of my sone as the odour of a `feeld ful which the Lord hath blessid.
Saboda haka ya je gunsa ya sumbace shi. Sa’ad da Ishaku ya ji ƙanshin rigunansa, sai ya sa masa albarka ya ce, “Aha, ƙanshin ɗana yana kama da ƙanshin jejin da Ubangiji ya sa wa albarka ne.
28 God yyue to thee of the dewe of heuene, and of the fatnesse of erthe, aboundaunce of whete, and of wyn, and of oile;
Allah yă ba ka daga raɓar sama da kuma yalwar ƙasa, yalwar hatsi da sabon ruwan inabi.
29 and puplis serue thee, and lynagis worschipe thee; be thou lord of thi britheren, and the sones of thi modir be bowid bifor thee; be he cursid that cursith thee, and he that blessith thee, be fillid with blessyngis.
Bari al’ummai su bauta maka mutane kuma su rusuna maka. Ka zama shugaba a kan’yan’uwanka bari kuma’ya’yan mahaifiyarka su rusuna maka. Bari waɗanda suka la’anta ka, su la’antu; waɗanda kuma suka sa maka albarka, su sami albarka.”
30 Vnnethis Isaac hadde fillid the word, and whanne Jacob was gon out,
Bayan Ishaku ya gama sa masa albarka, Yaƙub yana fita daga mahaifinsa ke nan, sai ga ɗan’uwansa Isuwa ya dawo daga farauta.
31 Esau cam, and brouyte in metis sodun of the huntyng to the fadir, and seide, My fadir, rise thou, and ete of the huntyng of thi sone, that thi soule blesse me.
Shi ma ya shirya abinci mai daɗi ya kawo wa mahaifinsa. Sa’an nan ya ce masa, “Babana, tashi ka zauna ka ci daga abin da na farauto, domin ka sa mini albarka.”
32 And Isaac seide, Who forsothe art thou? Which answerde, Y am Esau, thi firste gendrid sone.
Mahaifinsa Ishaku ya tambaye shi, “Wane ne kai?” Ya amsa, “Ni ne ɗanka, ɗan farinka, Isuwa.”
33 Isaac dredde bi a greet astonying; and he wondride more, than it mai be bileued, and seide, Who therfor is he which a while ago brouyte to me huntyng takun, and Y eet of alle thingis bifor that thou camest; and Y blesside him? and he schal be blessid.
Ishaku ya yi makyarkyata ƙwarai ya ce, “To, wane ne wannan da ya farauto nama ya kawo mini kafin ka zo, har na ci na kuma sa masa albarka? Tabbatacce zai zama mai albarka!”
34 Whanne the wordis of the fadir weren herd, Esau rorid with a greet cry, and was astonyed, and seide, My fadir, blesse thou also me.
Sa’ad da Isuwa ya ji kalmomin mahaifinsa, sai ya fashe da kuka mai zafi kuma da ƙarfi, ya ce wa mahaifinsa, “Ka albarkace ni, ni ma, baba!”
35 Which seide, Thy brother cam prudentli, and took thi blessyng.
Amma ya ce, “Ɗan’uwanka ya zo da makirci ya karɓi albarkarka.”
36 And Esau addide, Justli his name is clepid Jacob, for lo! he supplauntide me another tyme; bifor he took awei `my firste gendride thingis, and now the secounde tyme he rauyschide priueli my blessyng. And eft he seide to the fadir, Wher thou hast not reserued a blessyng also to me?
Isuwa ya ce, “Ba saboda haka ne aka raɗa masa suna Yaƙub ba? Ya yi mini ƙwace sau biyu ke nan; ya ƙwace mini matsayina na ɗan fari, ga shi yanzu kuma ya karɓi albarkata.” Sa’an nan ya yi tambaya, “Ba sauran albarkar da ka rage mini?”
37 Ysaac answeride, Y haue maad him thi lord, and Y haue maad suget alle hise britheren to his seruage; Y haue stablischid him in whete, and wyn, and oile; and, my sone, what schal Y do to thee aftir these thingis?
Ishaku ya amsa wa Isuwa, “Na mai da shi shugaba a kanka, na sa dukan dangoginsa su zama bayinsa, na kuma ba shi hatsi da sabon ruwan inabi. Saboda haka me kuma zan yi maka ɗana?”
38 To whom Esau saide, Fadir, wher thou hast oneli o blessyng? Y biseche that also thou blesse me. And whanne Esau wepte with greet yellyng,
Isuwa ya ce wa mahaifinsa, “Iyakar albarkar da kake da ita ke nan, baba? Ka albarkace ni ni ma, baba!” Sai Isuwa ya ɗaga murya ya yi kuka.
39 Isaac was stirid, and seide to hym, Thi blessyng schal be in the fatnesse of erthe, and in the dew of heuene fro aboue;
Mahaifinsa Ishaku ya amsa masa ya ce, “Ga shi, ni’imar ƙasar za tă nisanci mazauninka. Raɓar samaniya can ƙwanƙoli za tă nisance ka.
40 thou schalt lyue bi swerd, and thou schalt serue thi brothir, and tyme schal come whanne thou schalt shake awei, and vnbynde his yok fro thi nollis.
Za ka rayu ta wurin takobi za ka kuwa bauta wa ɗan’uwanka. Amma sa’ad da ka ɓalle, za ka kakkarye karkiyarsa daga wuyanka.”
41 Therfor Esau hatide euer Jacob for the blessyng bi which the fadir hadde blessid hym; and Esau seide in his herte, The daies of morenyng of my fadir schulen come, and Y schal sle Jacob, my brothir.
Isuwa ya riƙe Yaƙub a zuciya saboda albarkar da mahaifinsa ya sa masa. Ya ce wa kansa, “Kwanakin mutuwar mahaifina sun yi kusa; sa’an nan zan kashe ɗan’uwana Yaƙub.”
42 These thingis weren teld to Rebecca, and sche sente, and clepide hir sone Jacob, and seide to hym, Lo! Esau, thi brothir, manaasith to sle thee;
Sa’ad da aka faɗa wa Rebeka abin da babban ɗanta Isuwa ya faɗa, sai ta kira ɗanta Yaƙub ta ce masa, “Ɗan’uwanka Isuwa yana ta’azantar da kansa da tunanin kashe ka.
43 now therfor, my sone, here thou my vois, and rise thou, and fle to Laban, my brother, in Aran;
To, fa, ɗana, yi abin da na ce; gudu nan take zuwa wurin ɗan’uwana Laban a Haran.
44 and thou schalt dwelle with hym a fewe daies, til the woodnesse of thi brother reste,
Zauna tare da shi na ɗan lokaci sai ɗan’uwanka ya huce.
45 and his indignacioun ceesse, and til he foryite tho thingis whiche thou hast don ayens hym. Aftirward Y schal sende, and Y schal brynge thee fro thennus hidir. Whi schal Y be maad soneles of euer eithir sone in o dai?
Sa’ad da ɗan’uwanka ya daina fushi da kai, ya kuma manta da abin da ka yi masa, zan aika don ka dawo daga can. Don me zan rasa ku biyu a rana guda?”
46 And Rebecca seide to Isaac, It anoieth me of my lijf for the douytris of Heth; if Jacob takith a wijf of the kynrede of this lond, Y nyle lyue.
Sa’an nan Rebeka ta ce wa Ishaku, “Ni fa na gaji da matan Hittiyawan nan. In Yaƙub ya auri mata daga cikin matan ƙasan nan, wato, daga matan Hittiyawa irin waɗannan, rayuwata ba za tă daɗa mini kome ba.”

< Genesis 27 >