< Genesis 15 >
1 And so whanne these thingis weren don, the word of the Lord was maad to Abram bi a visioun, and seide, Abram, nyle thou drede, Y am thi defender, and thi meede is ful greet.
Bayan wannan, maganar Ubangiji ta zo wa Abram cikin mafarki cewa, “Kada ka ji tsoro, Abram. Ni ne garkuwarka, kuma ladanka zai zama mai girma.”
2 And Abram seide, Lord God, what schalt thou yyue to me? Y schal go with oute fre children, and this Damask, sone of Elieser, the procuratour of myn hous, schal be myn eir.
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mene ne za ka ba ni, ganin cewa ba na haihuwa, wanda kuma zai gāji gādon gidana shi ne Eliyezer mutumin Damaskus?”
3 And Abram addide, Sotheli thou hast not youe seed to me, and, lo! my borun seruaunt schal be myn eir.
Abram ya kuma ce, “Ga shi ba ka ba ni ɗa ba, don haka bawan da aka haifa a gidana ne zai zama magājina.”
4 And anoon the word of the Lord was maad to hym, and seide, This schal not be thin eir, but thou schalt haue hym eir, that schal go out of thi wombe.
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Wannan mutum ba zai zama magājinka ba, ɗa da yake zuwa daga jikinka ne zai zama magājinka.”
5 And the Lord ledde out Abram, and seide to hym, Biholde thou heuene, and noumbre thou sterris, if thou maist. And the Lord seide to Abram, So thi seed schal be.
Sai Ubangiji ya fito da kai shi waje ya ce, “Ka dubi sammai ka kuma ƙirga taurari, in har za ka iya ƙirga su.” Sa’an nan ya ce masa, “Haka zuriyarka za tă zama.”
6 Abram bileuede to God, and it was arettid to hym to riytfulnesse.
Abram ya gaskata, Ubangiji kuma ya lasafta shi adalci ga Abram.
7 And God seide to hym, Y am the Lord, that ladde thee out of Vr of Caldeis, that Y schulde yyue this lond to thee, and thou schuldist haue it in possessioun.
Ubangiji ya kuma ce wa Abram, “Ni ne Ubangiji wanda ya fitar da kai daga Ur na Kaldiyawa, domin in ba ka wannan ƙasa ka mallake ta.”
8 And Abram seide, Lord God, wherbi may I wite that Y schal welde it?
Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, yaya zan san cewa zan mallake ta?”
9 And the Lord answerde, and seide, Take thou to me a cow of thre yeer, and a geet of thre yeer, and a ram of thre yeer, a turtle also, and a culuer.
Saboda haka Allah ya ce masa, “Kawo mini karsana, akuya, da kuma rago kowanne yă kasance shi shekara uku ne, da kurciya da kuma ɗan tattabara.”
10 Which took alle these thingis, and departide tho bi the myddis, and settide euer eithir partis ech ayens other; but he departide not the briddis.
Abram ya kawo waɗannan duka a gaban Allah, ya raba kowannensu a tsakiya, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba.
11 And foulis camen doun on the careyns, and Abram drof hem awey.
Sai tsuntsaye masu cin nama suka sauko a kan gawawwakin, amma Abram ya kore su.
12 And whanne the sunne was gon doun, drede felde on Abram, and a greet hidousenesse and derk asaylide him.
Yayinda rana tana fāɗuwa, sai Abram ya yi barci mai zurfi, sai wani duhu mai kauri mai kuma bantsoro ya rufe shi.
13 And it was seid to hym, Wite thou bifore knowinge, that thi seed schal be pilgrim foure hundrid yeer in a lond not his owne, and thei schulen make hem suget to seruage, and thei schulen turment hem;
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani tabbatacce cewa shekaru ɗari huɗu, zuriyarka za tă zama baƙi a ƙasar da ba tasu ba, za a mai da su bayi, a kuma wulaƙanta su.
14 netheles Y schal deme the folk to whom thei schulen serue; and aftir these thingis thei schulen go out with greet catel.
Amma zan hukunta al’ummar da suka yi bauta kamar bayi, daga baya kuma za su fita da mallaka mai yawa.
15 Forsothe thou schalt go to thi fadris in pees, and schalt be biried in good age.
Amma kai za ka koma wurin kakanninka cikin salama a kuma binne ka da kyakkyawan tsufa.
16 Sotheli in the fourthe generacioun thei schulen turne ayen hidir, for the wickidnesses of Amoreis ben not yit fillid, `til to present tyme.
A tsara ta huɗu zuriyarka za tă komo nan, saboda zunubin Amoriyawa bai riga ya cika ba.”
17 Therfor whanne the sunne was gon doun, a derk myst was maad, and a furneis smokynge apperide, and a laumpe of fier, and passide thorou tho departingis.
Sa’ad da rana ta fāɗi, aka kuwa yi duhu, sai wata tukunya mai hayaƙi, mai harshen wuta mai ci, ta bayyana, ta kuma wuce tsakanin abubuwan nan da aka tsaga.
18 In that dai the Lord made a couenaunt of pees with Abram, and seide, Y schal yyue to thi seed this lond, fro the ryuer of Egipt til to the greet ryuer Eufrates; Cyneis,
A wannan rana, Ubangiji ya yi alkawari da Abram ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga kogin Masar zuwa babban kogi, Yuferites ke nan,
19 and Cyneseis, and Cethmoneis, and Etheis,
ƙasar Keniyawa, Kenizziyawa, Kadmoniyawa,
20 and Fereseis, and Raphaym, and Amorreis,
Hittiyawa, Ferizziyawa, Refahiyawa,
21 and Cananeis, and Gergeseis, and Jebuseis.
Amoriyawa, Kan’aniyawa, Girgashiyawa da kuma Yebusiyawa.”