< Genesis 13 >

1 Therfore Abram stiede fro Egipt, he, and his wijf, and alle thingis that he hadde; and Loth stiede with hym, to the south coost.
Saboda haka Abram ya haura daga Masar zuwa Negeb tare da matarsa, da dukan abin da yake da shi tare da Lot.
2 Forsothe he was ful riche in possessyoun of siluer and of gold.
Abram ya azurta ƙwarai da dabbobi, da azurfa, da kuma zinariya.
3 And he turnede ayen bi the weye in which he cam fro the south in to Bethel, `til to the place, in which bifore he hadde sett tabernacle, bitwixe Bethel and Hay,
Daga Negeb, ya ci gaba da tafiyarsa a wurare dabam-dabam har ya kai tsakanin Betel da Ai, a inda dā ya kafa tentinsa na fari
4 in the place of the auter which he made bifore, and inwardli clepide there the name of the Lord.
da kuma inda dā ya gina bagade. A can Abram ya kira bisa sunan Ubangiji.
5 But also flockis of scheep, and droues of oxun, and tabernaclis weren to Loth, that was with Abram;
Lot wanda yake tafiya tare da Abram, shi ma yana da garken shanu da tumaki da kuma tentuna.
6 and the lond miyte not take hem, that thei schulden dwelle togidre, for the catel of hem was myche, and thei miyten not dwelle in comyn.
Wannan ya sa har ƙasar ba tă ishe su yayinda suke zama tare ba, saboda mallakarsu ta yi yawa har ba za su iya zama tare ba.
7 Wherfor also strijf was maad bitwixe the keperis of flockis of Abram and of Loth. Forsothe Chananei and Feresei dwelliden in that lond in that tyme.
Rikici kuma ya tashi tsakanin masu kiwon dabbobin Abram da na Lot. Mazaunan ƙasar, a lokacin kuwa Kan’aniyawa da Ferizziyawa ne.
8 Therfor Abram seide to Loth, Y biseche, that no strijf be bitwixe me and thee, and bitwixe my scheepherdis and thi scheepherdis; for we ben britheren.
Saboda haka Abram ya ce wa Lot, “Kada mu bar rikici yă shiga tsakaninmu, ko kuma tsakanin masu kiwon dabbobinka da nawa, gama mu’yan’uwa ne.
9 Lo! al the lond is bifore thee, Y biseche, departe thou fro me; if thou go to the left side, Y schal holde the riyt side; if thou chese the riyt side, Y schal go to the left side.
Ba ga dukan ƙasar tana gabanka ba? Bari mu rabu. In ka yi hagu sai ni in yi dama. In ka yi dama, sai ni in yi hagu.”
10 And so Loth reiside hise iyen, and seiy aboute al the cuntrei of Jordan, which was al moistid, bifor that the Lord distriede Sodom and Gomorre, as paradis of the Lord, and as Egipt, as men comen in to Segor.
Lot ya ɗaga idanunsa sama ya dubi kwarin Urdun, sai ya ga kwarin yana da ciyawa mai kyau ƙwarai sai ka ce lambun Ubangiji, kamar ƙasar Masar, wajajen Zowar. (Wannan fa kafin Ubangiji yă hallaka Sodom da Gomorra.)
11 And Loth chees to him the cuntre aboute Jordan, and departide fro the eest; and thei weren departid ech fro his brother.
Saboda haka sai Lot ya zaɓar wa kansa dukan kwarin Urdun, ya tashi ya nufi wajen gabas. Haka fa suka rabu da juna.
12 Abram dwellide in the lond of Chanaan; sotheli Loth dwellide in townes aboute Jordan, and wonide in Sodom.
Abram ya zauna a ƙasar Kan’ana, yayinda Lot ya zauna cikin biranen kwari, ya kafa tentunansa kusa da Sodom.
13 Forsothe men of Sodom weren ful wickid, and synneris greetly bifore the Lord.
Mutanen Sodom kuwa mugaye ne, sun aikata zunubi ƙwarai ga Ubangiji.
14 And the Lord seide to Abram, aftir that Loth was departid fro him, Reise thin iyen forth riyt, and se fro the place in which thou art now, to the north and south, to the eest and west;
Bayan Lot ya rabu da Abram, sai Ubangiji ya ce wa Abram, “Ɗaga idanunka daga inda kake, ka dubi arewa da kudu, gabas da yamma.
15 Y schal yyue al the lond which thou seest to thee and to thi seed, til in to with outen ende.
Dukan ƙasar da kake gani zan ba ka, kai da zuriyarka har abada.
16 And Y schal make thi seed as the dust of erthe; if ony man may noumbre the dust of erthe, also he schal mowe noumbre thi seed.
Zan sa zuriyarka tă yi yawa kamar ƙurar ƙasa, har in wani yana iya ƙidaya ƙurar, to, za a iya ƙidaya zuriyarka.
17 Therfor rise thou, and passe thorou the lond in his lengthe and breede, for Y schal yyue it to thee.
Tafi, ka ratsa tsawo da fāɗin ƙasar, gama zan ba ka ita.”
18 Therfor Abram, mouynge his tabernacle, cam and dwellide bisidis the valei of Mambre, which is in Ebron; and he bildide there an auter to the Lord.
Saboda haka Abram ya cire tentunansa, ya zo ya zauna kusa da manyan itatuwan Mamre a Hebron, inda ya gina bagade ga Ubangiji.

< Genesis 13 >