< Ezra 10 >
1 Therfor while Esdras preiede so, and bisouyte God, and wepte, and lai bifor the temple of God, a ful greet cumpenye of Israel, of men, and of wymmen, and of children, was gaderid to him; and the puple wepte bi myche weping.
Yayinda Ezra yake addu’a, yake kuma furta laifi, yana kuka, yana a durƙushe da kansa ƙasa a gaban gidan Allah, sai babban taron jama’ar Isra’ilawa, maza, mata da yara, suka taru a wurinsa. Su ma suka yi kuka mai zafi.
2 And Sechenye, the sone of Jehiel, of the sones of Helam, answeride, and seide to Esdras, We han trespasside ayens oure God, and han weddid wyues, alien wymmen, of `the puplis of the lond. And now, for penaunce is in Israel on this thing,
Sai Shekaniya ɗan Yehiyel, daga zuriyar Elam ya ce wa Ezra, “Mun yi wa Allah rashin aminci ta wurin yin auratayya da maƙwabtanmu, amma duk da haka bai yashe mutanen Isra’ila ba.
3 smyte we boond of pees with `oure Lord God, and caste we awei alle `wyues aliens, and hem that ben borun of tho wyues, bi the wille of the Lord; and of hem that dreden the comaundement of oure God, `be it don bi the lawe.
Yanzu bari mu yi alkawari da Allahnmu, mu kori matan da yaransu bisa ga abin da ranka yă daɗe da sauran shugabannin da kuke girmama umarnin Allah kuka shawarce mu, bari mu yi haka bisa ga doka.
4 Rise thou, it `is thin office to deme, and we schulen be with thee; be thou coumfortid, and do.
Sai ka tashi, gama wannan hakkinka ne, za mu ba ka goyon baya. Saboda haka ka yi ƙarfin hali ka aikata shi.”
5 Therfor Esdras roos, and chargide greetli the princes of prestis, and of dekenes, and of al Israel, to do after this word; and thei sworen.
Sai Ezra ya tashi ya sa firistoci da suke shugabanni, da Lawiyawa, da dukan mutanen Isra’ila su rantse, cewa za su yi abin da aka ce. Sai suka yi rantsuwar.
6 And Esdras roos bifor the hows of God, and he yede to the bed of Johannan, sone of Eliasiph, and entride thidur; he eet not breed, and drank not watir; for he biweilide the trespassing of hem, that weren comun fro the caitifte.
Sa’an nan Ezra ya tashi daga gidan Allah ya tafi gidan Yehohanan ɗan Eliyashib, a can ma bai ci wani abu ba, bai sha ruwa ba domin ya ci gaba da yin baƙin cikin rashin aminci na waɗanda suka dawo daga bauta.
7 And a vois of hem was sent in to Juda and Jerusalem, to alle the sones of transmygracioun, that thei schulden be gaderid in to Jerusalem;
Aka yi shela a duk fāɗin Yahuda da Urushalima cewa dukan waɗanda suka dawo daga bauta su tattaru a Urushalima.
8 and ech man that cometh not in thre daies, bi the counsel of the princes and of eldre men, al his catel schal be takun awey fro him, and he schal be cast awei fro the cumpeny of transmygracioun.
Duk wanda bai zo a cikin kwana uku ba, za a washe shi, a kuma ware shi daga jama’ar da suka dawo daga bauta. Haka shugabanni da dattawa suka zartar.
9 Therfor alle the men of Juda and of Beniamyn camen togidere in to Jerusalem in thre daies; thilke is the nynthe monethe, in the twentithe dai of the monethe; and al the puple sat in `the street of Goddis hows, and trembliden for synne and reyn.
A cikin kwana uku duk mutanen Yahuda da na Benyamin suka taru a Urushalima. A ranar ashirin ga watan tara, dukan mutanen suka zauna a dandali a gaban gidan Allah cike da ɓacin rai saboda abin da ya faru da kuma ruwan da aka yi.
10 And Esdras, the preest, roos, and seide to hem, Ye han trespassid, and han weddid wyues, alien wymmen, that ye schulden `leie to on the trespas of Israel.
Sai Ezra firist ya miƙe tsaye ya yi musu magana ya ce, “Kun yi rashin aminci; kun aure mata baƙi, ta haka kuka ƙara kan zunubin Isra’ila.
11 And now yyue ye knowlechyng to the Lord God of oure fadris, and do ye his pleasaunce, and be ye departid fro the puplis of the lond, and fro `wyues aliens.
Yanzu sai ku furta zunubanku ga Ubangiji, Allahn kakanninku, ku kuma yi nufinsa. Ku raba kanku da mutanen da suke kewaye da ku, ku kuma rabu da baƙin mata.”
12 And al the multitude answeride, and seide with greet vois, Bi thi word to vs, so be it doon.
Mutanen kuwa suka tā da murya da ƙarfi suka ce, “Gaskiya ka faɗa, dole mu yi yadda ka ce,
13 Netheles for the puple is myche, and the tyme of reyn is, and we suffren not to stonde withoutforth, and it is not werk of o dai, nether of tweyne; for we han synned greetli in this word;
Amma akwai mutane da yawa, kuma lokacin damina ne; saboda haka ba za mu iya tsayawa a waje ba. Ban da haka ma, aikin nan ba na kwana ɗaya ko biyu ba ne, domin ba ƙaramin laifi muka yi ba.
14 `princes be ordeyned in al the multitude, and alle men in oure citees, that han weddid `wyues aliens, come in tymes ordeyned, and with hem come the eldere men, bi citee and citee, and the iugis therof, til the ire of oure God be turned awei fro vs on this synne.
Bari shugabanninmu su yi wani abu a madadin mutane duka, sa’an nan sai duk wanda ya san ya auri baƙuwar mace a garuruwanmu, sai yă zo nan a lokacin da aka shirya tare da dattawa da alƙalan kowane gari, har sai Allah ya huce fushinsa mai zafi da yake kanmu.”
15 Therfor Jonathan, the sone of Asahel, and Jaazie, the sone of Thecue, stoden on this thing; and Mosollam, and Sebethai, dekenes, helpiden hem.
Yonatan ɗan Asahel, da Yazehiya ɗan Tikba su ne kaɗai ba su yarda da wannan shirin ba, sai Meshullam da Shabbetai Balawe kuma suka goyi bayansu.
16 And the sones of transmygracioun diden so. And Esdras, the prest, and men, princes of meynees, yeden into the howsis of her fadris, and alle men bi her names; and thei saten in the firste dai of the tenthe monethe, for to seke the thing.
Sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi yadda aka zartar. Ezra firist ya zaɓi mutane waɗanda su ne shugabannin iyalai, ɗaya daga kowane sashe, aka rubuta sunan kowannensu. A ranar ɗaya ga watan goma kuwa suka zauna don su yi binciken waɗannan abubuwa.
17 And alle men weren endid, that hadden weddid `wyues aliens, `til to the firste dai of the firste monethe.
A rana ta farko ga watan farko, suka gama da bincike duk waɗanda suka auri baƙin mata.
18 And there weren foundun of the sones of preestis, that weddiden `wyues aliens; of the sones of Josue, the sone of Josedech, and hise britheren, Maasie, and Eliezer, and Jarib, and Godolie.
A cikin zuriyar firistoci, ga waɗanda suka auri mata baƙi. Daga zuriyar Yeshuwa ɗan Yozadak da’yan’uwansa, akwai Ma’asehiya, da Eliyezer, da Yarib, da Gedaliya.
19 And thei yauen her hondis, that thei schulden caste out her wyues, and offre for her trespas a ram of the scheep.
(Su ne suka miƙa hannuwansu suka nuna sun yarda su kori matansu baƙi, kowannensu kuma ya ba da rago daga cikin garkensa don a miƙa hadaya don zunubi.)
20 And of the sones of Semmer; Anam, and Zebedie.
Daga zuriyar Immer, akwai Hanani da Zebadiya.
21 And of the sones of Serym; Maasie, and Helie, and Semeie, and Jehiel, and Ozie.
Daga zuriyar Harim, akwai Ma’asehiya, Iliya, Shemahiya, Yehiyel da Uzziya.
22 And of the sones of Phessur; Helioneai, Maasie, Hismael, Nathanael, and Jozabet, and Elasa.
Daga zuriyar Fashhur, akwai Eliyohenai, Ma’asehiya, Ishmayel, Netanel, Yozabad da Eleyasa.
23 And of the sones of dekenes; Josabeth, and Semey, and Elaie; he is Calithaphataie; Juda, and Elezer.
Cikin Lawiyawa, akwai Yozabad, Shimeyi, Kelaya (wato, Kelita), Fetahahiya, Yahuda, Eliyezer.
24 And of syngeris, Eliazub; and of porteris, Sellum, and Thellem, and Vry.
Daga mawaƙa, akwai Eliyashib. Daga masu tsaron ƙofofin haikali, akwai Shallum, Telem da Uri.
25 And of Israel, of the sones of Pharos; Remea, and Ezia, and Melchia, and Vnanym, and Eliezer, and Melchia, and Banea.
Ga sunayen sauran mutanen Isra’ilan da suke da wannan laifi. Daga zuriyar Farosh, akwai Ramiya, da Izziya, Malkiya, Miyamin, Eleyazar, Malkiya da Benahiya.
26 And of the sones of Elam; Mathanye, and Zacharie, and Jehil, and Abdi, and Rymoth, and Helia.
Daga zuriyar Elam, akwai Mattaniya, Zakariya, Yehiyel, Abdi, Yeremot, da Iliya.
27 And of the sones of Zechua; Helioneay, Heliasib, Mathanye, and Jerymuth, and Zaeth, and Aziza.
Daga iyalin Zattu, akwai Eliyohenai, Eliyashib, Mattaniya Yeremot da Zabad da Aziza.
28 And of the sones of Bebai; Johannan, Ananye, Zabbai, Athalia.
Daga zuriyar Bebai, akwai Yehohanan, Hananiya, Zabbai, da Atlai.
29 And of the sones of Beny; Mosallam, and Melue, and Azaie, Jasub, and Saal, and Ramoth.
Daga zuriyar Bani, akwai Meshullam, Malluk, Adahiya, Yashub, Sheyal, da Ramot.
30 And of the sones of Phaeth; Moab, Edua, and Calal, Banaie, and Massie, Mathanye, Beseleel, and Bennun, and Manasse.
Daga zuriyar Fahat-Mowab, akwai Adna, Kelal, Benahiya, Ma’asehiya, Mattaniya, Bezalel, Binnuyi, da Manasse.
31 And of the sones of Erem; Elieer, Jesue, Melchie, Semeye, Symeon,
Daga zuriyar Harim, akwai Eliyezer, Isshiya, Malkiya, Shemahiya, Simeyon,
32 Beniamyn, Maloth, Samarie.
Benyamin, Malluk da Shemariya.
33 And of the sones of Asom; Mathanai, Mathetha, Zabeth, Eliphelech, Jermai, Manasse, Semei.
Daga zuriyar Hashum, akwai Mattenai, da Mattatta, Zabad, Elifelet, Irmai, Manasse, da Shimeyi.
34 Of the sones of Bany; Maddi, Amram, and Huel,
Daga zuriyar Bani, akwai Ma’adai, Amram, Yuwel,
35 Baneas, and Badaie, Cheilian,
Benahiya, Bedeya, Keluhi,
36 Biamna, Marymuth, and Eliasiph,
Baniya, Meremot, Eliyashib,
Mattaniya, Mattenai da Ya’asu.
38 and Bany, and Bennan, and Semei,
Daga zuriyar Binnuyi, akwai Shimeyi,
39 and Salymas, and Nathan, and Daias,
Shelemiya, Natan, Adahiya,
40 Metuedabai, Sisai, Sarai,
Maknadebai, Shashai, Sharai,
41 Ezrel, and Seloman, Semerie,
Azarel, Shelemiya, da Shemariya,
42 Sellum, Amarie, Joseph.
Shallum da Amariya da Yusuf.
43 Of the sones of Nebny; Aiel, Mathatie, Zabed, Zabina, Jebdu, and Johel, Banai.
Daga zuriyar Nebo, akwai Yehiyel, Mattitiya, Zabad, Zebina, Yaddai, Yowel da Benahiya.
44 Alle these hadden take `wyues aliens, and of hem weren wymmen, that hadden bore children.
Dukan waɗannan sun auri baƙin mata, waɗansunsu suna da’ya’ya.