< Ezekiel 5 >

1 And thou, sone of man, take to thee a scharp swerd, schauynge heeris; and thou schalt take it, and schalt leede it bi thin heed, and bi thi berd. And thou schalt take to thee a balaunce of weiyte, and thou schalt departe tho.
“Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki takobi mai kaifi ka kuma yi amfani da shi kamar rezan mai aski don askin kanka da gemunka. Sa’an nan ka ɗauki ma’auni ka kuma raba gashin.
2 Thou schalt brenne the thridde part with fier in the myddis of the citee, bi the fillyng of daies of bisegyng. And thou schalt take the thridde part, and schalt kitte bi swerd in the cumpas therof. But thou schalt scatere `the tother thridde part in to the wynd; and Y schal make nakid a swerd aftir hem.
Sa’ad da kwanakin ƙawanyarka sun ƙare, sai ka ƙone kashi ɗaya bisa uku na gashin da wuta a cikin birnin. Ka ɗauki kashi ɗaya bisa uku ka yayyanka shi da takobi kewaye da birnin. Ka kuma watsar da kashi ɗaya bisa uku a iska. Gama zan fafare su da takobin da aka zāre.
3 And thou schalt take therof a litil noumbre, and thou schalt bynde tho in the hiynesse of thi mentil.
Amma ka ɗibi gashi kaɗan ka daure a shafin rigarka.
4 And eft thou schalt take of hem, and thou schalt caste forth hem in to the myddis of the fier. And thou schalt brenne hem in fier; and fier schal go out of that in to al the hous of Israel.
Har yanzu, ka ɗibi kaɗan na waɗannan ka zuba su cikin wuta su kuma ƙone. Wuta zai bazu daga nan zuwa dukan gidan Isra’ila.
5 The Lord God seith these thingis, This is Jerusalem; Y haue sette it in the myddis of hethene men, and londis in the cumpas therof.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Urushalima ce wannan, wadda na kafa a tsakiyar al’ummai, da ƙasashe kewaye da ita a ko’ina.
6 And it dispiside my domes, that it was more wickid than hethene men; and it dispiside my comaundementis more than londis that ben in the cumpas therof. For thei han cast awei my domes, and thei yeden not in my comaundementis.
Duk da haka cikin muguntarta ta yi tayarwa a kan dokokina da ƙa’idodina fiye da al’ummai da ƙasashe kewaye da ita. Ta ƙi dokokina ba tă kuwa bi ƙa’idodina ba.
7 Therfor the Lord God seith these thingis, For ye `han passid hethene men that ben in youre cumpas, and ye yeden not in my comaundementis, and ye diden not my domes, and ye wrouyten not bi the domes of hethene men that ben in youre cumpas;
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce kin yi ƙin ji fiye da al’umman da suke kewaye da ke ba ki kuma bi ƙa’idodina ko ki kiyaye dokokina ba. Ba ki ma dace da matsayin al’umman da suke kewaye da ke ba.
8 therfor the Lord God seith these thingis, Lo! Y to thee, and Y my silf schal make domes in the myddis of thee, bifor the iyen of hethene men; and Y schal do thingis in thee,
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Ni kaina ina gāba da ke, Urushalima, kuma zan hukunta ki a gaban al’ummai.
9 whiche Y dide not, and to whiche Y schal no more make lijk thingis, for alle thin abhomynaciouns.
Saboda dukan gumakan banƙyamarki, zan yi abin da ban taɓa yi ba, ba kuwa zan ƙara yinsa ba.
10 Therfor fadris schulen ete sones in the myddis of thee, and sones schulen ete her fadris; and Y schal make domes in thee, and Y schal wyndewe alle thin remenauntis in to ech wynd.
Saboda haka a cikinki ubanni za su ci’ya’yansu,’ya’ya kuma za su ci ubanninsu. Zan hukunta ki zan kuma watsar da dukan waɗanda suke tsira da suke naki a iska.
11 Therfor Y lyue, seith the Lord God, no but for that that thou defoulidist myn hooli thing in alle thin offenciouns, and in alle thin abhomynaciouns; and Y schal breke, and myn iye schal not spare, and Y schal not do merci.
Saboda haka muddin ina a raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin kin ƙazantar da wuri mai tsarkina da dukan mugayen siffofinki da kuma ayyukanki masu banƙyama, ni kaina zan janye alherina; ba zan ji tausayinki ko in haƙura da ke ba.
12 The thridde part of thee schal die bi pestilence, and schal be wastid bi hungur in the middis of thee; and the thridde part of thee schal falle doun bi swerd in thi cumpas; forsothe Y schal scatere thi thridde part in to ech wynd, and Y schal drawe out a swerd after hem.
Kashi ɗaya bisa uku na mutanenki za su mutu da annoba ko su mutu da yunwa a cikinki; kashi ɗaya bisa uku takobi ne zai kashe su a waje da katangarki; kashi ɗaya bisa uku kuma zan watsar a iska in kuma fafare su da takobin da aka zāre.
13 And Y schal fille my stronge veniaunce, and Y schal make myn indignacioun to reste in hem, and Y schal be coumfortid. And thei schulen wite, that Y the Lord spak in my feruent loue, whanne Y schal fille al myn indignacioun in hem.
“Sa’an nan ne fushina zai huce hasalata a kanki kuma ta lafa, in kuma wartsake. Kuma sa’ad da na zuba fushina a kansu, a sa’an nan ne za su san cewa Ni Ubangiji na yi magana a cikin fushin kishina a kansu.
14 And Y schal yyue thee in to desert, in to schenschipe to hethene men that ben in thi cumpas, in the siyt of ech that passith forth.
“Zan mai da ki kufai da kuma abin dariya a cikin al’ummai kewaye da ke, a gaban dukan waɗanda suke wucewa.
15 And thou schalt be schenschipe `and blasfemye, ensaumple and wondryng, among hethene men that ben in thi cumpas, whanne Y schal make domes in thee, in strong veniaunce, and indignacioun, and in blamyngis of ire.
Za ki zama abin dariya da abin ba’a, kashedi da abin banrazana ga al’ummai kewaye da ke sa’ad da na hukunta ki cikin fushi da cikin hasala da kuma tsawatawa mai zafi. Ni Ubangiji na faɗa.
16 Y the Lord haue spoke, whanne Y schal sende in to hem the worste arowis of hungur, that schulen bere deth; and whiche Y schal sende, that Y leese you. And Y schal gadere hungur on you, and Y schal al to-breke in you the sadnesse of breed.
Sa’ad da na harbe ki da mugayen kibiyoyina da kuma kibiyoyi masu hallakarwa na yunwa, zan yi harbi don in kashe ki. Zan kawo ƙarin yunwa a kanki in kuma yanke tanadin abincinki.
17 And Y schal sende in to you hungur, and worste beestis, til to the deth; and pestilence and blood schulen passe bi thee, and Y schal bringe in swerd on thee; Y the Lord spak.
Zan aika da yunwa da namun jeji a kanki, za su kuma bar ku ba’ya’ya. Annoba da zub da jini za su ratsa cikinki, zan kuma kawo takobi a kanki. Ni Ubangiji na faɗa.”

< Ezekiel 5 >