< Ezekiel 34 >

1 And the word of the Lord was maad to me,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 and he seide, Sone of man, profesie thou of the schepherdis of Israel, profesie thou; and thou schalt seie to the schepherdis, The Lord God seith these thingis, Wo to the schepherdis of Israel, that fedden hym silf; whether flockis ben not fed of schepherdis?
“Ɗan mutum, ka yi annabci a kan makiyayan Isra’ila; ka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton makiyayan Isra’ila waɗanda suke kula da kansu ne kawai! Ashe, bai kamata makiyaya ne su lura da tumaki ba?
3 Ye eeten mylk, and weren hilid with wollis, and ye killiden that that was fat; but ye fedden not my floc.
Kuna cin kitsensu, kuna yi wa kanku tufafi da gashinsu, kukan yanka turkakkun, amma ba ku yi kiwon tumakin ba.
4 Ye maden not sad that that was vnstidfast, and ye maden not hool that that was sijk; ye bounden not that that was brokun, and ye brouyten not ayen that that was cast awei, and ye souyten not that that perischide; but ye comaundiden to hem with sturnenesse, and with power.
Ba ku ƙarfafa marasa ƙarfi ba, ko ku warkar da marasa lafiya ko ku ɗaura waɗanda suka ji rauni. Ba ku dawo da waɗanda suka yi makuwa ko ku nemi waɗanda suka ɓace ba. Amma sai kuka mallake su ƙarfi da yaji.
5 And my scheep weren scaterid, for no sheepherde was; and thei weren maad in to deuouryng of alle beestis of the feeld, and thei weren scaterid.
Saboda haka suka warwatse domin babu makiyayi, kuma da suka warwatsu sai suka zama abincin namun jeji.
6 My flockis erriden in alle mounteyns, and in ech hiy hil, and my flockis weren scaterid on al the face of erthe, and noon was that souyte.
Tumakina suna ta yawo a kan dukan duwatsu da kuma kowane tudu. Sun watsu a dukan duniya, kuma ba wanda ya neme su.
7 Therfor, scheepherdis, here ye the word of the Lord;
“‘Saboda haka, ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
8 Y lyue, seith the Lord God, for whi for that that my flockis ben maad in to raueyn, and my scheep in to deuouryng of alle beestis of the feeld, for that that no scheepherde was, for the scheepherdis souyten not my floc, but the scheepherdis fedden hem silf, and fedden not my flockis; therfor,
Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin tumaki sun rasa makiyayi ta haka aka washe su suka kuma zama abincin dukan namun jeji, kuma domin makiyayana ba su nemi tumakina ba amma suka kula da kansu a maimakon tumakina,
9 scheepherdis, here ye the word of the Lord,
saboda haka, ya ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
10 The Lord God seith these thingis, Lo! Y my silf am ouer scheepherdis; Y schal seke my floc of the hond of hem, and Y schal make hem to ceesse, that thei fede no more my flok, and that the scheepherdis feede no more hem silf. And Y schal delyuere my floc fro the mouth of hem, and it schal no more be in to mete to hem.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da makiyaya kuma zan nemi hakkin tumakina daga gare su. Zan hana su yin kiwon tumakin don kada makiyayan su ƙara yin kiwon kansu. Zan ƙwace tumakina daga bakunansu, ba kuwa za su ƙara zama abincinsu.
11 For the Lord God seith these thingis, Lo! Y my silf schal seke my scheep, and Y schal visite hem.
“‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan nemi tumakina.
12 As a scheepherde visitith his floc, in the dai whanne he is in the myddis of hise scheep `that ben scaterid, so Y schal visite my scheep; and Y schal delyuere hem fro alle places in whiche thei weren scaterid, in the dai of cloude, and of derknesse.
Kamar yadda makiyayi yakan lura da tumakinsa da suka watse sa’ad da yake tare da su, haka zan lura da tumakina. Zan cece su daga dukan wuraren da aka watsar da su a ranar gizagizai da baƙin duhu.
13 And Y schal leede hem out of puplis, and Y schal gadere hem fro londis, and Y schal brynge hem in to her lond, and Y schal feede hem in the hillis of Israel, in ryueris, and in alle seetis of erthe.
Zan dawo da su daga al’ummai in kuma tattara su daga ƙasashe, zan kuma kawo su cikin ƙasarsu. Zan yi kiwonsu a kan duwatsun Isra’ila, a maɓulɓulai da kuma cikin wuraren zamansu a ƙasar.
14 Y schal feede hem in moost plenteouse pasturis, and the lesewis of hem schulen be in the hiy hillis of Israel; there thei schulen reste in greene eerbis, and in fatte lesewis thei schulen be fed on the hillis of Israel.
Zan kula da su a wurin kiwo mai kyau, kuma ƙwanƙolin duwatsun Isra’ila ne zai zama wurin kiwonsu. Za su kwanta a wurin kiwo mai kyau, a can kuma za su yi kiwo a wurin kiwo mai kyau a kan duwatsun Isra’ila.
15 Y schal fede my scheep, and Y schal make hem to ligge, seith the Lord God.
Ni kaina zan lura da tumakina in kuma sa su kwanta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
16 I schal seke that that perischide, and Y schal brynge ayen that that was cast awei; and Y schal bynde that that was brokun, and Y schal make sad that that was sijk; and Y schal kepe that that was fat and strong; and Y schal feede hem in doom;
Zan nemi ɓatattuna in kuma dawo da waɗanda suka yi makuwa. Zan ɗaura raunin waɗanda suka ji ciwo in kuma ƙarfafa marasa ƙarfi, amma zan hallaka ƙarfafa da kuma masu ƙiba. Zan yi kiwo tumaki da adalci.
17 forsothe ye ben my flockis. The Lord God seith these thingis, Lo! Y deme bitwixe beeste and beeste, and a wethir and a buc of geet.
“‘Game da ku, tumakina, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya, da tsakanin raguna da awaki.
18 Whether it was not enowy to you to deuoure good pasturis? Ferthermore and ye defouliden with youre feet the remenauntis of youre lesewis, and whanne ye drunken clereste watir, ye disturbliden the residue with youre feet.
Bai isa ba a ce kun yi kiwo a wuri mai kyau? Sai kun tattake sauran wurin kiwonku da ƙafafunku tukuna? Bai isa ba a ce kun sha ruwa mai tsabta? Sai kun kuma gurɓata sauran da ƙafafunku?
19 And my scheep weren fed with tho thingis that weren defoulid with youre feet; and thei drunken these thingis, that youre feet hadden troblid.
Dole ne tumakina su ci abin da kuka tattake su kuma sha abin da kuka gurɓata da ƙafafunku?
20 Therfor the Lord God seith these thingis to you, Lo! Y my silf deme bitwixe a fat beeste and a leene beeste.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce musu, duba, ni kaina zan hukunta tsakanin turkakkun tumaki da ramammun tumaki.
21 For that that ye hurliden with sidis, and schuldris, and wyndewiden with youre hornes alle sike beestis, til tho weren scaterid withoutforth, I schal saue my floc,
Domin kun tunkuɗe marasa ƙarfi da kafaɗunku, kun kuma tunkuye su da ƙahoninku sai da suka gudu,
22 and it schal no more be in to raueyn. And Y schal deme bitwixe beeste and beeste;
zan cece tumakina ba za su ƙara zama ganima ba. Zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya.
23 and Y schal reise on tho o sheepherde, my seruaunt Dauid, that schal fede tho; he schal fede tho, and he schal be `in to a sheepherde to hem.
Zan sa musu makiyaya guda, bawana Dawuda, zai kuwa lura da su; zai kula da su ya kuma zama makiyayinsu.
24 Forsothe Y the Lord schal be in to God to hem, and my seruaunt Dauid schal be prince in the myddis of hem; Y the Lord spak.
Ni Ubangiji zan zama Allahnsu, bawana kuma Dawuda zai zama yerima a cikinsu. Ni Ubangiji na faɗa.
25 And Y schal make with hem a couenaunt of pees, and Y schal make worste beestis to ceesse fro erthe; and thei that dwellen in desert, schulen slepe sikur in forestis.
“‘Zan yi alkawarin salama da su in kuma kawar wa ƙasar da namun jeji domin su zauna a hamada su kuma kwana a kurmi lafiya lau.
26 And Y schal sette hem blessyng in the cumpas of my litle hil, and Y schal lede doun reyn in his tyme. And reynes of blessyng schulen be,
Zan albarkace su in kuma sa tuduna kewaye da su. Zan zubo yayyafi a lokacinsa; za a kasance da yayyafin albarka.
27 and the tre of the feeld schal yyue his fruyt, and the erthe schal yyue his seed. And thei schulen be in her lond with out drede; and thei schulen wite, that Y am the Lord, whanne Y schal al to-breke the chaynes of her yok, and schal delyuere hem fro the hond of hem that comaunden to hem.
Itatuwan gona za su ba da’ya’yansu, ƙasa kuma za tă ba da amfaninta; mutane za su zauna lafiya a ƙasarsu. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na karya karkiyarsu, na cece su daga hannun waɗanda suka bautar da su.
28 And thei schulen no more be in to raueyn in to hethene men, nether the beestis of erthe schulen deuoure hem, but thei schulen dwelle tristili with outen ony drede.
Ba za su ƙara zama ganimar al’ummai ba, ba kuwa namun jeji za su cinye su ba. Za su zauna lafiya, kuma babu wani da zai sa su ji tsoro.
29 And Y schal reise to hem a iust buriownyng named; and thei schulen no more be maad lesse for hunger in erthe, and thei schulen no more bere the schenschipis of hethene men.
Zan tanada musu ƙasar da aka sani don hatsinta, ba za su kuma ƙara zama abin da yunwa za tă fara musu a ƙasa ba ko su sha zargin sauran al’ummai.
30 And thei schulen wite, that Y am her Lord God with hem, and thei ben my puple, the hous of Israel, seith the Lord God.
Sa’an nan za su san cewa ni, Ubangiji Allahnsu, ina tare da su kuma cewa su, gidan Isra’ila, mutanena ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
31 Forsothe ye my flockis ben men, the flockis of my lesewe; and Y am youre Lord God, seith the Lord God.
Ku tumakina, tumakin wurin kiwona, mutanena ne, ni kuwa Allahnku ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”

< Ezekiel 34 >