< Ezekiel 24 >
1 And the word of the Lord was maad to me, in the nynthe yeer, and in the tenthe monethe, in the tenthe dai of the monethe,
A shekara ta tara, a wata na goma, a rana ta goma, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 and he seide, Thou, sone of man, write to thee the name of this dai, in which the king of Babiloyne is confermed ayens Jerusalem to dai.
“Ɗan mutum, ka rubuta wannan rana, wannan rana, domin sarkin Babilon ya yi ƙawanya wa Urushalima a wannan rana.
3 And thou schalt seie bi a prouerbe a parable to the hous, terrere to wraththe, and thou schalt speke to hem, The Lord God seith these thingis, Sette thou a brasun pot, sette thou sotheli, and putte thou watir in to it. Take thou a beeste ful fat;
Ka faɗa wa wannan gidan’yan tawaye wani misali ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka sa tukunyar dahuwa; ka sa ta a kan wuta ka kuma zuba ruwa a cikinta.
4 gadere thou togidere the gobetis therof in it, ech good part, and the hipe, and the schuldre, chosun thingis and ful of boonys.
Ka sa gunduwoyin nama a cikinta dukan gunduwoyi masu kyau, cinya da kafaɗa. Ka cika ta da waɗannan ƙasusuwa mafi kyau;
5 Also dresse thou heepis of boonys vndur it; and the sething therof buylide out, and the boonys therof weren sodun in the myddis therof.
ka kama mafi kyau daga cikin garken. Ka tara itace a ƙarƙashinta saboda ƙasusuwan; ka sa ta tafasa ka kuma dafa ƙasusuwan a cikinta.
6 Therfor the Lord God seith these thingis, Wo to the citee of bloodis, to the pot whos rust is ther ynne, and the rust therof yede not out of it; caste thou out it bi partis, and bi hise partis; lot felle not on it.
“‘Gama wannan shi ne abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini, ga tukunya wadda take da tsatsa, wadda tsatsarta ba za tă fita ba! Ka fitar da shi gunduwa-gunduwa ba tare da jefa ƙuri’a a kansu ba.
7 For whi the blood therof is in the myddis therof; he schede it out on a ful cleer stoon, he schedde not it out on erthe,
“‘Gama zubar da jini yana a tsakiyarta, ta zubar da shi a dutsen da yake a fili; ba tă zubar da shi a ƙasa ba, inda ƙura za tă rufe shi.
8 that it mai be hilid with dust, that Y schulde bringe in myn indignacioun, and `a venge bi veniaunce; Y yaf the blood therof on a ful cleer stoon, that it schulde not be hilid.
Don a zuga hasala a kuma yi sakayya na sa jininta a dutsen da ba a rufe ba, saboda kada a rufe.
9 Therfor the Lord God seith these thingis, Wo to the citee of bloodis, whos brennyng Y schal make greet;
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini! Ni ma zan jibge itace da yawa.
10 gadere thou togidire boonys, whiche Y schal kyndle with fier; fleischis schulen be wastid, and al the settyng togidere schal be sodun, and boonys schulen faile.
Ka tula gumagumai ka kuma ƙuna wuta. Ka dafa naman da kyau, kana haɗawa da yaji; ka kuma bar ƙasusuwan su ƙone.
11 Also sette thou it voide on coolis, that the metal therof wexe hoot, and be meltid, and that the filthe therof be wellid togidere in the myddis therof, and the rust therof be wastid.
Sa’an nan ka sa tukunyan nan da babu kome a kan garwashi sai ta yi zafi har darmarta ta yi ja wur domin dattinta ya narke tsatsarta kuma ta ƙone.
12 It was swat bi myche trauel, and the ouer greet rust therof yede not out therof, nether bi fier.
Ta gajiyar da dukan ƙoƙari; ba a fid da tsatsarta nan mai yawa ba, kai, ko a wuta ma.
13 Thin vnclennesse is abhomynable, for Y wolde clense thee, and thou art not clensid fro thi filthis; but nether thou schalt be clensid bifore, til Y make myn indignacioun to reste in thee.
“‘Yanzu ƙazantarki ita ce lalaci. Domin na yi ƙoƙari in tsabtacce ke amma ba ki tsabtattu daga ƙazantarki ba, ba za ki ƙara yin tsabta ba sai hasalata a kanki ya kwanta.
14 Y the Lord spak; it schal come, and Y schal make, Y schal not passe, nethir Y schal spare, nether Y schal be plesid; bi thi weies and bi thi fyndyngis Y schal deme thee, seith the Lord.
“‘Ni Ubangiji na faɗa. Lokaci ya zo da zan aikata. Ba zan janye ba; ba zan ji tausayi ba, ba kuwa zan bari ba. Za a hukunta ki bisa ga hali da ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
15 And the word of the Lord was maad to me,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
16 and he seide, Thou, sone of man, lo! Y take awei fro thee the desirable thing of thin iyen in veniaunce, and thou schalt not weile, nether wepe, nether thi teeris schulen flete doun.
“Ɗan mutum, da farat ɗaya ina gab da ɗauke abin da idanunka suke jin daɗin gani. Duk da haka kada ka yi makoki ko ka yi kuka ko ka zub da hawaye.
17 Weile thou beynge stille, thou schalt not make mourenyng of deed men; thi coroun be boundun aboute thin heed, and thi schoon schulen be in the feet, nether thou schalt hile the mouth with a cloth, nether thou schalt ete the metis of mourneris.
Ka yi nishi shiru; kada ka yi makoki saboda matacciyar. Ka naɗa rawaninka ka kuma sa takalmanka a ƙafa; kada ka rufe sashen fuskarka daga ƙasa ko ka ci abincin da masu kuka sukan ci.”
18 Therfor Y spak to the puple in the morewtid, and my wijf was deed in the euentid; and Y dide in the morewtid, as he hadde comaundid to me.
Da gari ya waye, sai na yi magana da mutane, da yamma kuwa matata ta rasu. Kashegari na yi yadda aka umarce ni.
19 And the puple seide to me, Whi schewist thou not to vs what these thingis signefien, whiche thou doist?
Sai mutane suka tambaye ni suka ce, “Ba za ka faɗa mana abin da waɗannan abubuwa suke nufi a gare mu ba?”
20 And Y seide to hem, The word of the Lord was maad to me,
Sai na ce musu, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
21 and he seide, Speke thou to the hous of Israel, The Lord God seith these thingis, Lo! Y schal defoule my seyntuarie, the pride of youre empire, and the desirable thing of youre iyen, and on which youre soule dredith; and youre sones and youre douytris, whiche ye leften, schulen falle bi swerd.
faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da ƙazantar da wuri mai tsarkina, kagarar da kuke taƙama, abin da idanunku suke jin daɗin gani, abin faranta zuciyarku.’Ya’yanku maza da mata waɗanda kun bari a baya za su mutu ta wurin takobi.
22 And ye schulen do, as Y dide; ye schulen not hile mouthis with cloth, and ye schulen not ete the mete of weileris.
Za ku kuma yi yadda na yi. Ba za ku rufe sashe ƙasa na fuskarku ko ku ci abinci da masu kuka sukan ci ba.
23 Ye schulen haue corouns in youre heedis, and schoon in the feet; ye schulen not weile, nether ye schulen wepe, but ye schulen faile in wretchidnesse, for youre wickidnessis; and ech man schal weile to his brother.
Za ku naɗa rawunanku a kai ku sa takalmanku a ƙafafunku. Ba za ku yi kuka ko makoki ba amma za ku lalace saboda zunubanku ku kuma yi ta yin nishi.
24 And Ezechiel schal be to you in to a signe of thing to comynge; bi alle thingis whiche he dide, ye schulen do, whanne this thing schal come; and ye schulen wite, that Y am the Lord God.
Ezekiyel zai zama alama gare ku; za ku yi daidai yadda ya yi. Sa’ad da wannan ya faru, za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’
25 And thou, sone of man, lo! in the dai in which Y schal take awei fro hem the strengthe of hem, and the ioie of dignyte, and the desire of her iyen, on whiche the soulis of hem resten, caste awei the sones and douytris of hem;
“Kai kuma ɗan mutum, a ranar da zan ɗauke musu kagararsu, farin cikinsu da darajarsu, abin da idanunsu ke jin daɗin gani, abin da yake faranta musu zuciya, da kuka’ya’yansu maza da mata,
26 in that dai whanne a man fleynge schal come to thee, to telle to thee;
a ranan nan wanda ya tsere zai zo don yă ba ka labari.
27 in that dai sotheli thou schalt opene thi mouth with hym that fledde; and thou schalt speke, and schalt no more be stille; and thou schalt be to hem in to a signe of thing to comynge, and ye schulen witen, that Y am the Lord.
A lokacin bakinka zai buɗe, za ka yi magana da shi ba kuwa za ka ƙara yin shiru ba. Ta haka za ka zama alama gare su, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.”