< Ezekiel 23 >
1 And the word of the Lord was maad to me,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 and he seide, Thou, sone of man, twei wymmen weren the douytris of o modir, and diden fornycacioun in Egipt;
“Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
3 in her yonge wexynge age thei diden fornicacioun; there the brestis of hem weren maad low, and the tetis of the tyme of mariage of hem weren brokun.
Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
4 Forsothe the names of hem ben, Oolla, the more sistir, and Ooliba the lesse sistir of hir. And Y hadde hem, and thei childiden sones and douytris; certis the names of hem ben Samarie Oolla, and Jerusalem Ooliba.
Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
5 Therfor Oolla dide fornicacioun on me, and was wood on hir louyeris, on Assiriens neiyinge,
“Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
6 clothid with iacinct, princes, and magistratis, yonge men of coueytise, alle kniytis, and stieris of horsis.
waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
7 And sche yaf hir fornicaciouns on hem, on alle the chosun sones of Assiriens; and in alle on whiche sche was wood, sche was defoulid in the vnclennessis of hem.
Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
8 Ferthermore and sche lefte not hir fornicaciouns, whiche sche hadde in Egipt; for whi and thei slepten with hir in the yongthe of hir, and thei braken the tetis of the tyme of mariage of hir, and thei scheden out her fornicacioun on hir.
Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
9 Therfor Y yaf hir in to the hondis of hir louyeris, in to the hondis of the sones of Assur, on whos letcherie sche was wood.
“Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
10 Thei diskyueriden the schenschipe of hir; thei token awei the sones and the douytris of hir, and killiden hir with swerd; and the wymmen weren maad famouse, that is, sclaundrid, and thei diden domes in hir.
Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
11 And whanne hir sistir Ooliba hadde seyn this, sche was wood in letcherie more than that sistre, and yaf vnschamefastli hir fornicacioun on the fornicacioun of hir sistre,
“Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
12 to the sones of Assiriens, to duykis and magistratis comynge to hir, that weren clothid with dyuerse cloth, to knyytis that weren borun on horsis, and to yonge men with noble schap, to alle men.
Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
13 And Y siy that o weie of both sistris was defoulid,
Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
14 and sche encreesside hir fornycaciouns. And whanne sche hadde seyn men peyntid in the wal, the ymagis of Caldeis expressid with colouris,
“Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
15 and gird on the reynes with kniytis girdlis, and cappis peyntid in the heedis of hem, the foormes of alle duykis, the licnesse of the sones of Babiloyne, and of the lond of Caldeis, in which thei weren borun;
da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
16 sche was wood on hem bi coueitise of hir iyen, and sche sente messangeris to hem in to Caldee.
Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
17 And whanne the sones of Babiloyne weren comun to hir, to the bed of tetis, thei defouliden hir in her letcheries of virgyns; and sche was defoulid of hem, and the soule of hir was fillid of hem.
Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
18 Also sche made nakid hir fornicaciouns, and diskyuered hir schenschipe; and my soule yede awei fro hir, as my soule hadde go awei fro hir sistir.
Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
19 For sche multiplied hir fornicaciouns, and hadde mynde on the daies of hir yongthe, in whiche sche dide fornicacioun in the lond of Egipt.
Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
20 And sche was wood in letcherie on the liggyng bi of hem, whos fleischis ben as the fleischis of assis, and as the membris of horsis ben the membris of hem.
A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
21 And thou visitidist the grete trespas of thi yongthe, whanne thi brestis weren maad low in Egipt, and the tetis of the tyme of thi mariage weren brokun.
Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
22 Therfor, thou Ooliba, the Lord God seith these thingis, Lo! Y schal reise alle thi louyeris ayens thee, of whiche thi soule was fillid, and Y schal gadere hem ayens thee in cumpas;
“Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
23 the sones of Babiloyne, and alle Caldeis, noble and miyti men, and princes, alle the sones of Assiriens, and yonge men of noble foorme, duykis, and magistratis, alle princes of princes, and named stieris of horsis.
Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
24 And thei araied with chare and wheel schulen come on thee, the multitude of puplis schulen be armed with haburioun, and scheeld, and basynet, ayens thee on ech side; and Y schal yyue doom bifor hem, and thei schulen deme thee bi her domes.
Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
25 And Y schal sette my feruour in thee, which thei schulen vse with thee in woodnesse; thei schulen kitte awei thi nose and thin eeris, and thei schulen sle with swerd tho thingis that weren left; thei schulen take thi sones and thi douytris, and thi laste thing schal be deuourid bi fier.
Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
26 And thei schulen make thee nakid of thi clothis, and thei schulen take awei the vessels of thi glorie.
Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
27 And Y schal make thi greet trespasse to reste fro thee, and thi fornicacioun fro the lond of Egipt; and thou schalt not reise thin iyen to hem, and thou schalt no more haue mynde on Egipt.
Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
28 For the Lord God seith these thingis, Lo! Y schal yyue thee in to the hondis of hem whiche thou hatist, `in to the hondis of hem of whiche thi soule was fillid,
“Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
29 and thei schulen do with thee in hatrede. And thei schulen take awei alle thi trauels, and thei schulen leeue thee nakid, and ful of schenschipe; and the schenschipe of thi fornicaciouns schal be schewid. Thi greet
Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
30 trespas and thi fornycaciouns han do these thingis to thee; for thou didist fornicacioun aftir hethene men, among whiche thou were defoulid in the idols of hem.
sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
31 Thou yedist in the weie of thi sister, and Y schal yyue the cuppe of hir in thin hond.
Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
32 The Lord God seith these thingis, Thou schalt drinke the cuppe of thi sistir, the depthe, and the broodnesse; thou that art most able to take, schalt be in to scornyng, and in to mouwyng.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
33 Thou schalt be fillid with drunkenesse and sorewe, with the cuppe of mourenyng and of heuynesse, with the cuppe of thi sister Samarie.
Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
34 And thou schalt drynke it, and thou schalt drinke of til to the drastis, and thou schalt deuoure the relifs therof, and thou schalt to-reende thi brestis, for Y the Lord spak, seith the Lord God.
Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
35 Therfor the Lord God seith these thingis, For thou hast foryete me, and hast cast forth me bihynde thi bodi, bere thou also thi greet trespas and thi fornicaciouns.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
36 And the Lord God seide to me, and spak, Sone of man, whether thou demest Ooliba and Oolla, and tellist to hem the grete trespassis of hem?
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
37 For thei diden auowtrie, and blood was in the hondis of hem, and thei diden fornicacioun with her idols; ferthermore and thei offriden to tho the sones whiche thei gendriden to me, for to be deuourid.
gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
38 But also thei diden this to me, thei defouleden my seyntuarie in that dai, and maden vnhooli my sabatis.
Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
39 And whanne thei sacrifisiden her sones to her idols, and entriden in to my seyntuarie in that dai, that thei schulden defoule it, thei diden also these thingis in the myddis of myn hous.
A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
40 Thei senten to men comyng fro fer, to whiche thei hadden sent messangeris. Therfor lo! thei camen, to whiche thou waischidist thee, and anoyntidist thin iyen with oynement of wymmen, and thou were ourned with wymmens atier.
“Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
41 Thou satist in a ful fair bed, and a boord was ourned bifor thee; thou settidist myn encense and myn oynement on it.
Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
42 And a vois of multitude makynge ful out ioye was ther ynne; and in men that weren brouyt of the multitude of men, and camen fro desert, thei settiden bies in the hondis of hem, and faire corouns on the heedis of hem.
“Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
43 And Y seide to hir, that was defoulid in auoutries, Now also this schal do fornycacioun in hir fornicacioun.
Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
44 And thei entriden to hir; as to a womman, an hoore, so thei entriden to Oolla and to Ooliba, cursid wymmen.
Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
45 Therfor these men ben iust, these schulen deme thilke wymmen bi the doom of auoutressis, and bi the doom of hem that scheden out blood; for thei ben auoutressis, and blood is in the hondis of hem, and thei diden fornicacioun with her idols.
Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
46 For the Lord God seith these thingis, Bringe thou multitudis to hem, and yyue thou hem in to noise, and in to raueyn;
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
47 and be thei stoonyd with the stoonys of puplis, and be thei stikid togidere with the swerdis of hem. Thei schulen sle the sones and the douytris of hem, and thei schulen brenne with fier the housis of hem.
Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
48 And Y schal do awei greet trespas fro the lond; and alle wymmen schulen lerne, that thei do not aftir the greet trespas of hem.
“Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
49 And thei schulen yyue youre grete trespas on you; and ye schulen bere the synnes of youre idols, and ye schulen wite, that Y am the Lord God.
Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”