< Ezekiel 12 >
1 And the word of the Lord was maad to me,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
2 and he seide, Sone of man, thou dwellist in the myddis of an hous terrynge to wraththe, which han iyen to se, and seen not, and eeris to here, and heren not; for it is an hous terrynge to wraththe.
ɗan mutum, kana zama a cikin mutane masu tawaye, Suna da idanun gani amma ba sa gani, suna da kunnuwan ji amma ba sa ji, gama’yan tawaye ne.
3 Therfor thou, sone of man, make to thee vessels of passing ouer, and thou schalt passe ouer bi dai bifor hem; forsothe thou schalt passe ouer fro thi place to another place, in the siyt of hem, if perauenture thei biholden, for it is an hous terrynge to wraththe.
“Saboda haka ɗan mutum, ka tattara kayanka don zuwa zaman bauta, ka tashi da rana suna gani ka ƙaura a inda kake zuwa wani wuri. Mai yiwuwa za su gane, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
4 And thou schalt bere withoutforth thi vessels, as the vessels of a man passynge ouer bi dai, in the siyt of hem; sotheli thou schalt go out in the euentid bifore hem, as a man passynge forth goith out.
Da rana, yayinda suke kallo, ka fid da kayanka da ka tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma, yayinda suke kallo, ka fita kamar yadda mutane masu tafiyar zaman bauta sukan yi.
5 Bifore the iyen of hem digge the wal to thee, and thou
Yayinda suke kallo, ka huda katanga ka fitar da kayanka daga ciki.
6 schalt go out thorouy it in the siyt of hem. Thou schalt be borun on schuldris, thou schalt be borun out in derknesse; thou schalt hile thi face, and thou schalt not se the erthe, for Y haue youe thee a signe
Ka sa su a kafaɗarka yayinda suke kallo ka kuma fitar da su da dare. Ka rufe fuskarka don kada ka ga ƙasar, gama na mai da kai alama ga gidan Isra’ila.”
7 of thing to comynge to the hous of Israel. Therfor Y dide as the Lord comaundide to me; Y brouyte forth my vessels, as the vessels of a man passynge ouer bi dai, and in the euentid Y diggide a wal to me with hond; Y yede out in derknesse, and Y was borun on schuldris,
Sai na yi kamar yadda aka umarce ni. Da rana na fitar da kayana da na tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma na huda katanga da hannuwana. Na kwashe kayana da dare, na ɗauke su a kafaɗuna yayinda suke kallo.
8 in the siyt of hem. And the word of the Lord was maad eerli to me,
Da safe maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
9 and he seide, Sone of man, whether the hous of Israel, the hous terrynge to wraththe, seiden not to thee, What doist thou?
“Ɗan mutum, gidan’yan tawayen nan na Isra’ila ba su tambaye ka, ‘Me kake yi ba?’
10 Seie thou to hem, The Lord God seith these thingis, This birthun is on the duyk, which is in Jerusalem, and on al the hous of Israel, which is in the myddis of hem.
“Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan abin da Allah ya yi magana a kai ya shafi sarki a Urushalima da kuma dukan gidan Isra’ila waɗanda suke a can.’
11 Seie thou, Y am youre signe of thing to comynge; as Y dide, so it schal be don to hem; thei schulen go in to passynge ouer, and in to caitifte.
Ka ce musu, ‘Ni alama ne a gare ku.’ “Kamar yadda na yi, haka za a yi da su. Za a kai su zaman bauta kamar kamammu.
12 And the duyk which is in the myddis of hem, schal be borun out on schuldris, and he schal go out in derknesse; thei schulen digge the wal, and lede hym out; his face schal be hilid, that he se not with iye the erthe.
“Sarkin da yake a cikinsu zai ɗauki kayansa ya saɓa a kafaɗarsa da dare ya tafi, za a huda masa rami a katanga ya fita. Zai rufe fuskarsa don kada yă ga ƙasar.
13 And Y schal stretche forth my net on hym, and he schal be takun in my net; and Y schal lede hym in to Babiloyne, in to the lond of Caldeis, and he schal not se that lond, and he schal die there.
Zan shimfiɗa masa ragata, za a kuwa kama shi da tarkona; zan kawo shi Babiloniya, ƙasar Kaldiyawa, amma ba zai gan ta ba, a can kuwa zai mutu.
14 And Y schal scatere in to ech wynd alle men that ben aboute hym, his help, and hise cumpenyes; and Y schal draw out the swerd aftir hem.
Zan warwatsa dukan waɗanda suke kewaye da shi a dukan fuskokin iska, ma’aikatansa da dukan rundunoninsa, zan fafare su da takobin da aka zāre.
15 And thei schulen wite, that Y am the Lord, whanne Y schal scatere hem among hethene men, and schal sowe hem abrood in londis.
“Za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na watsar da su a cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe.
16 And Y schal leue of hem a fewe men fro swerd, and hungur, and pestilence, that thei telle out alle the grete trespassis of hem among hethene men, to which thei schulen entre; and thei schulen wite, that Y am the Lord.
Amma zan bar kaɗan daga cikinsu su tsere wa takobi, yunwa da annoba, saboda a cikin al’umman da suka tafi su furta dukan ayyukansu masu banƙyama. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
17 And the word of the Lord was maad to me,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 and he seide, Thou, sone of man, ete thi breed in disturblyng, but also drynke thi water in haaste and mourening.
“Ɗan mutum, ka yi rawar jiki yayinda kake cin abincinka, ka kuma yi makyarkyata don tsoro yayinda kake shan ruwanka.
19 And thou schalt seie to the puple of the lond, The Lord God seith these thingis to hem that dwellen in Jerusalem, in the lond of Israel, Thei schulen ete her breed in angwisch, and thei schulen drynke her watir in desolacioun; that the lond be desolat of his multitude, for the wickidnesse of alle men that dwellen ther ynne.
Ka faɗa wa mutanen ƙasar cewa, ‘Ga abin Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da waɗanda suke zama a Urushalima da kuma cikin ƙasar Isra’ila. Za su ci abincinsu da razana, su sha ruwansu da tsoro, gama za a washe dukan abin da yake ƙasarsu saboda hargitsin dukan waɗanda suna zama a can.
20 And citees that ben now enhabitid, shulen be desolat, and the lond schal be forsakun; and ye schulen wite, that Y am the Lord.
Garuruwan da mutane suna ciki za su zama kufai ƙasar kuma za tă zama kango. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
21 And the word of the Lord was maad to me,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
22 and he seide, Sone of man, what is this prouerbe to you, of men seiynge in the lond of Israel, Daies schulen be differrid in to long tyme, and ech visioun shal perische?
“Ɗan mutum, mene ne wannan karin magana da kuke da shi a ƙasar Isra’ila mai cewa, ‘Kwanaki suna ta wucewa, wahayi bai gudana ba’?
23 Therfor seie thou to hem, The Lord God seith these thingis, Y schal make this prouerbe to ceesse, and it schal no more be seid comynli in Israel; and speke thou to hem, that the daies han neiyid, and ech word of profesie.
Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo ƙarshen wannan karin magana, ba za su ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.’ Ka ce musu, ‘Kwanaki sun gabato da za a tabbatar da kowane wahayi.
24 For whi ech visioun schal no more be voide, nether bifor tellyng of thing to comynge schal be douteful in the myddis of the sones of Israel;
Gama ba za a ƙara ganin wahayin ƙarya ko a yi duba na daɗin baki a cikin mutanen Isra’ila ba.
25 for Y the Lord schal speke what euer word Y schal speke, and it schal be don; it schal no more be delaied, but in youre daies, ye hous terrynge to wraththe, Y schal speke a word, and Y schal do that word, seith the Lord God.
Amma Ni Ubangiji zan yi magana abin da na nufa, za tă kuwa tabbata ba tare da jinkiri ba. Gama cikin kwanakinku, kai gidan’yan tawaye, zan cika duk abin da na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
26 And the word of the Lord was maad to me, and he seide, Thou,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
27 sone of man, lo! the hous of Israel, of hem that seien, The visioun which this man seeth, is in to manye daies, and this man profesieth in to longe tymes.
“Ɗan mutum, gidan Isra’ila suna cewa, ‘Wahayin da yake gani na shekaru masu yawa ne nan gaba, yana kuma annabce-annabce game da wani zamani ne can.’
28 Therfor seie thou to hem, The Lord God seith these thingis, Ech word of me schal no more be deferrid; the word which Y schal speke, schal be fillid, seith the Lord God.
“Saboda haka ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa ba wata maganata da za tă ƙara yin jinkiri; duk abin da na faɗa zai cika, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”