< Exodus 8 >

1 Also the Lord seide to Moises, Entre thou to Farao, and thou schalt seie to hym, The Lord seith these thingis, Delyuere thou my puple, that it make sacrifice to me; sotheli if thou nylt delyuere, lo!
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
2 Y schal smyte alle thi termys with paddoks;
In ka ƙi barinsu, zan hore ka da annoban kwaɗi a dukan ƙasarka.
3 and the flood schal buyle out paddokis, that schulen stie, and schulen entre in to thin hows, and in to the closet of thi bed, and on thi bed, and in to `the hous of thi seruauntis, and in to thi puple, and in to thin ouenes, and in to the relyues of thi metis;
Nilu zai cika da kwaɗi. Za su haura zuwa cikin fadanka da kan gadonka, cikin gidajen bayinka da kan mutanenka, cikin kwanonin toye-toyenka da na cin abincinka.
4 and the paddoks schulen entre to thee, and to thi puple, and to alle thi seruauntis.
Kwaɗin nan za su yi ta tsalle a kanka, da kan mutanenka, da kuma kan dukan bayinka.’”
5 And the Lord seide to Moises, Seie thou to Aaron, Hold forth thin hond on the floodis, and on the streemes, and mareis; and bryng out paddoks on the lond of Egipt.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka miƙa hannunka da sandanka bisa koguna da rafuffuka da kuma kududdufai, ka sa kwaɗi su fito su mamaye ƙasar Masar.’”
6 And Aaron helde forth the hond on the watris of Egipt; and paddoks stieden, and hileden the lond of Egipt.
Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwan Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka mamaye ƙasar Masar.
7 Forsothe and the witchis diden in lijk maner bi her enchauntementis; and thei brouyten forth paddoks on the lond of Egipt.
Amma bokaye ma suka yi abubuwan nan ta wurin sihirinsu; suka sa kwaɗi suka fito suka mamaye ƙasar Masar.
8 Forsothe Farao clepide Moises and Aaron, and seide to hem, Preie ye the Lord, that he do a wei the paddoks fro me, and fro my puple; and Y schal delyuere the puple, that it make sacrifice to the Lord.
Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Yi addu’a ga Ubangiji yă ɗauke kwaɗi daga gare ni da mutanena, zan kuwa bar mutanenku su tafi su yi hadaya ga Ubangiji.”
9 And Moises seide to Farao, Ordeyne thou a tyme to me, whanne Y schal preie for thee, and for thi seruauntis, and for thi puple, that the paddokis be dryuun awei fro thee, and fro thin hows, and fro thi seruauntis, and fro thi puple; and dwelle oneli in the flood.
Musa ya ce wa Fir’auna, “Na ba ka dama ka ba da lokacin da zan yi addu’a dominka da kuma bayinka da mutanenka, gidajenku kuwa za su rabu da kwaɗi, amma ban da waɗanda suke cikin Nilu.”
10 And he answeride, To morewe. And Moises seide, Y schal do bi thi word, that thou wite, that noon is as oure Lord God; and the paddoks schulen go awei fro thee,
Fir’auna ya ce, “Gobe.” Musa ya amsa, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani kamar Ubangiji, Allahnmu.
11 and fro thin hous, and fro thi children, and fro thi seruauntis, and fro thi puple; and tho schulen dwelle oneli in the flood.
Kwaɗin za su bar ka da gidajenka, bayinka da mutanenka; za su kasance a Nilu ne kaɗai.”
12 And Moises and Aaron yeden out fro Farao. And Moises criede to the Lord, for the biheest of paddoks, which he hadde seid to Farao.
Bayan Musa da Haruna sun bar Fir’auna, Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji saboda kwaɗin da ya kawo a bisa Fir’auna.
13 And the Lord dide bi the word of Moises; and the paddoks weren deed fro housis, and fro townes, and fro feeldis;
Sai Ubangiji ya yi abin da Musa ya nema. Kwaɗin suka mutu a gidaje, da filaye, da kuma gonaki.
14 and thei gaderiden tho in to grete heepis, and the lond was rotun.
Aka jibga su tsibi-tsibi, ƙasar ta yi ɗoyi saboda su.
15 Sotheli Farao seiy that reste was youun, and he made greuous his herte, and herde not hem, as the Lord comaundide.
Amma da Fir’auna ya ga an sami sauƙi, sai ya taurare, ya ƙi yă saurari Musa da Haruna kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
16 And the Lord seide to Moises, Spek thou to Aaron, Holde forth thi yerde, and smyte the dust of erthe, and litle flies, ether gnattis, be in al the lond of Egipt.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Miƙa hannunka ka bugi ƙurar ƙasa,’ dukan ƙurar ƙasar Masar kuwa za tă zama ƙwari masu cizo.”
17 And thei diden so; and Aaron helde forth the hond, and helde the yerde, and smoot the duste of erthe; and gnattis weren maad in men, and in werk beestis; al the dust of erthe was turned in to gnattis bi al the lond of Egipt.
Suka yi haka, da Haruna ya miƙa hannunsa da sandan, ya bugi ƙurar ƙasa, sai ƙwari masu cizo suka fito a kan mutane da dabbobi. Dukan ƙurar, ko’ina a ƙasar Masar ta zama cinnaku.
18 And witchis diden in lijk maner bi her enchauntementis, that thei schulden brynge forth gnattis, and thei miyten not; and gnattis weren as wel in men as in werk beestis.
Sa’ad da bokayen Fir’auna suka yi ƙoƙari yin sihiri iri na rufe ido domin su fito da kwari, sai suka kāsa. Ƙwari masu cizo kuwa suka rufe mutane da dabbobi.
19 And the witchis seiden to Farao, This is the fyngur of God. And the herte of Farao was maad hard, and he herde not hem, as the Lord comaundide.
Sai bokaye suka ce wa Fir’auna, “Wannan fa da hannun Allah a ciki.” Amma zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
20 And the Lord seide to Moises, Rise thou eerli, and stonde bifore Farao, for he schal go out to the watris; and thou schalt seie to hym, The Lord seith these thingis, Delyuere thou my puple, that it make sacrifice to me;
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tashi da sassafe ka sadu da Fir’auna a lokacin da za shi kogi, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, bari mutanena su tafi, don su yi mini sujada.
21 that if thou schalt not delyuere the puple, lo! Y schal sende in to thee, and in to thi seruauntis, and in to thi puple, and in to thin housis, al the kynde of flies; and the housis of Egipcians schulen be fillid with flies of dyuerse kyndis, and al the lond in which thei schulen be.
In ba ka bar mutanena suka tafi ba, zan turo da tarin ƙuda a kanka da bayinka, a kan mutanenka da cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da ƙudaje, har ma da ƙasa inda za su taka.
22 And in that dai Y schal make wondurful the lond of Gessen, in which my puple is, that flies be not there; and that thou wite that Y am the Lord in the myddis of erthe;
“‘Amma zan keɓe yankin Goshen, inda mutanena suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, domin ka sani cewa Ni, Ubangiji, ina cikin wannan ƙasa.
23 and Y schal sette departyng bitwixe my puple and thi puple; this signe schal be to morewe.
Zan sa iyaka tsakanin jama’ata da jama’arka. Gobe ne wannan mu’ujiza za tă auku.’”
24 And the Lord dide so. And a moost greuouse flie cam in to the hows of Farao, and of hise seruauntis, and in to al the lond of Egipt; and the lond was corrupt of siche flies.
Ubangiji kuwa ya yi haka. Tarin ƙuda suka zubo a fadar Fir’auna da cikin gidajen bayinsa, da ko’ina a Masar, ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje.
25 And Farao clepide Moises and Aaron, and seide to hem, Go ye, make ye sacrifice to `youre Lord God in this lond.
Sai Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tafi, ku miƙa hadaya ga Allahnku, a nan a cikin ƙasar.”
26 And Moises seide, It may not be so, for `we schulen offre to oure God the abhomynaciouns of Egipcians; that if we schulen sle bifore Egipcians tho thingis whiche thei worschipen, thei schulen `ouerleie vs with stoonus.
Amma Musa ya ce, “Wannan ba zai yiwu ba. Hadayun da mukan miƙa wa Ubangiji, Allahnmu haram ne ga Masarawa. In kuwa muka miƙa hadayun da suke haram a idanunsu, ba za su jajjefe mu ba?
27 We schulen go the weie of thre daies in to wildirnesse, and we schulen make sacrifice to oure Lord God, as he comaundide vs.
Dole mu yi tafiya kwana uku cikin hamada domin miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnmu, yadda ya umarce mu.”
28 And Farao seide, Y schal delyuere you, that ye make sacrifice to `youre Lord God in deseert; netheles go ye not ferthere; preie ye for me.
Fir’auna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, don ku miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnku, a cikin hamada, amma ba za ku tafi da nisa ba. Yanzu ku yi mini addu’a.”
29 And Moises seide, Y schal go out fro thee, and Y schal preie the Lord; and the fli schal go awei fro Farao, and fro hise seruauntis, and puple to morewe; netheles nyle thou more disseyue me, that thou delyuere not the puple to make sacrifice to the Lord.
Musa ya amsa, “Da zarar na bar ka, zan yi addu’a ga Ubangiji, gobe kuwa ƙudaje za su bar Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa. Sai dai a tabbata Fir’auna bai sāke yin ruɗi ta wurin ƙin barin mutane su tafi su miƙa hadayu ga Ubangiji ba.”
30 And Moises yede out fro Farao, and preiede the Lord, whiche dide bi the word of Moyses,
Sa’an nan Musa ya rabu da Fir’auna, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
31 and took awei flies fro Farao, and fro hise seruauntis, and puple; noon lefte, `sotheli nether oon.
Ubangiji kuwa ya yi abin da Musa ya roƙa. Ƙudaje suka rabu da Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa; ba ƙudan da ya rage.
32 And the herte of Farao was maad hard, so that he delyueride not the puple, sothli nethir in this tyme.
Amma a wannan lokaci ma, Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai kuma bar mutanen suka tafi ba.

< Exodus 8 >