< Exodus 6 >

1 And the Lord seide to Moises, Now thou schalt se, what thingis Y schal do to Farao; for bi strong hond he schal delyuere hem, and in myyti hond he schal caste hem out of his lond.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Yanzu za ka gan abin da zan yi da Fir’auna. Zan sa shi dole yă bar su su tafi, har ma yă iza ƙyeyarsu don su bar ƙasarsa!”
2 And the Lord spak to Moises,
Allah ya kuma ce wa Musa, “Ni ne Ubangiji.
3 and seide, Y am the Lord, that apperide to Abraham, and to Isaac, and to Jacob in Almyyti God; and Y schewide not to hem my greet name Adonai;
Na bayyana ga Ibrahim, ga Ishaku da kuma ga Yaƙub a matsayin Allah Maɗaukaki, amma sunan nan nawa Ubangiji, ban bayyana kaina a gare su ba.
4 and Y made couenaunt with hem, that Y schulde yyue to hem the lond of Canaan, the lond of her pilgrymage, in which thei weren comelyngis.
Na kuma kafa alkawari da su don in ba su ƙasar Kan’ana, inda suka yi zaman baƙunci.
5 Y herde the weilyng of the sones of Israel, in which the Egipcians oppresseden hem, and Y hadde mynde of my couenaunt.
Ban da haka ma, na ji nishe-nishen Isra’ilawa, waɗanda Masarawa suka bautar, na kuma tuna da alkawarina.
6 Therfor seie thou to the sones of Israel, Y am the Lord, that schal lede out you of the prisoun of Egipcians; and Y schal delyuere fro seruage; and Y schal ayen bie in `an hiy arm, and in grete domes;
“Saboda haka, ka ce wa Isra’ilawa, ‘Ni ne Ubangiji, zan kuma fitar da ku daga bauta ta Masarawa. Zan’yantar da ku daga zama bayinsu, da ƙarfina zan fanshe ku, in kawo hukunci mai zafi a kansu, don in cece ku.
7 and Y schal take you to me in to a puple, and Y schal be youre God; and ye schulen wite, for Y am youre Lord God, `which haue led you out of the prisoun of Egipcians,
Zan ɗauke ku tamƙar mutanena, in kuma zama Allahnku. Sa’an nan za ku sani Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga wahalar Masarawa.
8 and haue led you in to the lond, on which Y reiside myn hond, that Y schulde yyue it to Abraham, and to Ysaac, and to Jacob; and Y schal yyue to you that lond to be weldid; I the Lord.
Zan kuwa kawo ku a ƙasar da na rantse da hannun da na ɗaga sama, cewa zan ba wa Ibrahim, wa Ishaku, da kuma wa Yaƙub. Zan ba da ita gare ku gādo. Ni ne Ubangiji.’”
9 Therfor Moises telde alle thingis to the sones of Irael, whiche assentide not to hym for the angwisch of spirit, and for the hardest werk.
Musa ya faɗa wa Isra’ilawa wannan magana, amma ba su kasa kunne a gare shi ba, don ɓacin rai saboda tsananin aikin bauta.
10 And the Lord spak to Moises,
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
11 and seide, Entre thou, and speke to Farao, kyng of Egipt, that he delyuere the children of Israel fro his lond.
“Koma ka ce wa Fir’auna sarkin Masar, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.”
12 Moises answeride bifore the Lord, Lo! the children of Israel here not me, and hou schal Farao here, moost sithen Y am vncircumcidid in lippis?
Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “In Isra’ilawa ba su ji ni ba, yaya Fir’auna zai ji ni, da yake ina magana da ƙyar?”
13 And the Lord spak to Moises and to Aaron, and yaf comaundementis to the sones of Israel, and to Farao, kyng of Egipt, that thei schulden lede out the sones of Israel fro the lond of Egipt.
Ubangiji ya yi magana da Musa da Haruna game da Isra’ilawa da Fir’auna sarkin Masar, ya umarce su su fitar da Isra’ilawa daga Masar.
14 These ben the princis of housis bi her meynees. The sones of Ruben, the firste gendrid of Israel, Enoch, and Fallu, Esrom, and Charmy; these ben the kynredis of Ruben.
Waɗannan su ne shugabannin iyalansu.’Ya’yan Ruben maza ɗan farin Isra’ila su ne, Hanok da Fallu, Hezron da Karmi. Waɗannan su ne dangin Ruben.
15 The sones of Symeon, Jamuel, and Jamyn, and Aod, and Jachym, and Soer, and Saul, the sone of a womman of Canaan; these ben the kynretis of Symeon.
’Ya’yan Simeyon maza su ne, Yemuwel, Yamin, Ohad, Yakin, Zohar da Sha’ul ɗan mutuniyar Kan’ana. Waɗannan su ne dangin Simeyon.
16 And these ben the names of the sones of Leuy by her kynredis, Gerson, and Caath, and Merary. Forsothe the yeeris of lijf of Leuy weren an hundrid and seuene and thretti.
Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Lawi maza bisa ga abin da aka rubuta, Gershon, Kohat da Merari. Lawi ya yi shekara 137.
17 The sones of Gerson, Lobny and Semei, bi her kynredis.
’Ya’yan Gershon maza, bisa ga dangi su ne, Libni da Shimeyi.
18 The sones of Caath, Amram, and Isuar, and Hebron, and Oziel; and the yeeris of lijf of Caath weren an hundrid and thre and thretti.
’Ya’yan Kohat maza, su ne, Amram, Izhar, Hebron da Uzziyel. Kohat ya yi shekara 133.
19 The sones of Merari weren Mooli and Musi. These weren the kynredis of Leuy bi her meynees.
’Ya’yan Merari maza, su ne, Mali da Mushi. Waɗannan su ne dangin Lawi bisa ga abin da aka rubuta.
20 Forsothe Amram took a wijf, Jocabed, douytir of his fadris brother, and sche childide to hym Aaron, and Moises, and Marie; and the yeeris of lijf of Amram weren an hundred and seuene and thretti.
Amram ya auri’yar’uwar mahaifinsa Yokebed, wadda ta haifa masa Haruna da Musa. Amram ya yi shekara 137.
21 Also the sones of Isuar weren Chore, and Nafeg, and Zechry.
’Ya’yan Izhar maza, su ne, Kora, Nefeg da Zikri.
22 Also the sones of Oziel weren Misael, and Elisaphan, and Sechery.
’Ya’yan Uzziyel maza, su ne, Mishayel, Elzafan da Sitri.
23 Sotheli Aaron took a wijf, Elizabeth, the douytir of Amynadab, the sistir of Naason, and sche childide to hym Nadab, and Abyu, and Eleazar, and Ythamar.
Haruna ya auri Elisheba,’yar Amminadab,’yar’uwar Nashon, sai ta haifa masa Nadab da Abihu, Eleyazar da Itamar.
24 Also the sones of Chore weren Aser, and Elcana, and Abiasab; thes weren the kinredis of Chore.
’Ya’yan Kora maza, su ne, Assir, Elkana da Abiyasaf. Waɗannan su ne dangin Kora.
25 And sotheli Eleazar, sone of Aaron, took a wijf of the douytris of Phatiel, and sche childide Fynees to hym. These ben the princis of the meynees of Leuy bi her kynredis.
Eleyazar ɗan Haruna, ya auri ɗaya daga cikin’yan matan Futiyel, sai ta haifa masa Finehas. Waɗannan su ne shugabannin iyalan Lawi, dangi, dangi.
26 This is Aaron and Moises, to whiche the Lord comaundide, that thei schulden lede out of the lond of Egipt the sones of Israel by her cumpanyes;
Wannan Haruna da Musa ne, waɗanda Ubangiji ya yi musu magana ya ce, “Ku fitar da Isra’ilawa daga Masar ɓangare-ɓangare.”
27 these it ben, that speken to Pharao king of Egipt, that thei lede the sones of Israel out of Egipt;
Su ne suka yi magana da Fir’auna sarkin Masar game da fitar da Isra’ilawa daga Masar, wannan Musa da Haruna.
28 this is Moises and Aaron, in the dai in which the Lord spak to Moises in the lond of Egipt.
Ana nan, sa’ad da Ubangiji ya yi magana da Musa a Masar,
29 And the Lord spak to Moises, and seide, Y am the Lord; spek thou to Farao, kyng of Egipt, alle thingis whiche Y speke to thee.
ya ce masa, “Ni ne Ubangiji. Sai ka faɗa wa Fir’auna sarkin Masar kome da na faɗa maka.”
30 And Moises seide bifore the Lord, Lo! Y am vncircumcidid in lippis; hou schal Farao here me?
Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “Ni mai nauyin baki ne, ina magana da ƙyar, ƙaƙa Fir’auna zai kasa kunne gare ni?”

< Exodus 6 >