< Exodus 31 >

1 And the Lord spak to Moyses, `and seide, Lo!
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Y haue clepid Beseleel bi name, the sone of Hury, sone of Hur, of the lynage of Juda;
“Duba, na zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuda,
3 and Y haue fillid hym with the spirit of God, with wisdom, and vndirstondyng, and kunnyng in al werk,
na kuma cika shi da Ruhun Allah, fasaha, azanci, da kuma sani cikin kowace irin sana’a,
4 to fynde out what euer thing may be maad suteli, of gold, and siluer, and bras, and marbil,
don yin zāne-zāne na aikin zinariya, azurfa da tagulla,
5 and gemmes, and dyuersite of trees.
don yanka da shirya duwatsu, yin aikin katako, da kuma yin kowane irin aikin sana’ar hannu.
6 And Y haue youe to hym a felowe, Ooliab, the sone of Achisameth, of the kynrede of Dan; and Y haue put in `the herte of hem the wisdom of ech lerned man, that thei make alle thingis, whiche Y comaundide to thee;
Ban da haka, na zaɓi Oholiyab ɗan Ahisamak, na kabilar Dan, don yă taimake shi. Na kuma ba da fasaha ga dukan masu aikin sana’ar hannu, don yin duk abin da na umarce ka.
7 the tabernacle of boond of pees, and the arke of witnessyng, and the propiciatorie, ether table, which is theronne, and alle the vessels of the tabernacle;
Tentin Sujada, akwatin Alkawari tare da murfin kafara a bisansa, da dukan kayan aiki na tentin,
8 also the bord, and vessels therof, the clenneste candilstike with hise vessels, and the auteris of encence,
tebur da kayansa, wurin ajiye fitila na zinariya zalla, da dukan kayansa, bagaden ƙona turare,
9 and of brent sacrifice, and alle the vessels of hem; the greet `waischyng vessel with his foundement;
bagaden hadaya ta ƙonawa da dukan kayansa, daro tare da mazauninsa,
10 hooli clothis in seruyce to Aaron prest, and to hise sones, that thei be set in her office in hooli thingis;
da kuma saƙaƙƙun riguna, tsarkakan riguna don Haruna firist da rigunan’ya’yansa maza, sa’ad da suke hidima a matsayin firistoci,
11 the oile of anoyntyng, and encence of swete smellynge spiceryes in the seyntuarie; thei schulen make alle thingis whiche Y comaundide to thee.
da man shafewa, da turare mai ƙanshi don Wuri Mai Tsarki. Za a yi su kamar yadda na umarce ka.”
12 And the Lord spak to Moises, `and seide, Speke thou to the sones of Israel,
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
13 and thou schalt seie to hem, Se ye that ye kepe my sabat, for it is a signe bytwixe me and you in youre generaciouns; that ye wite, that Y am the Lord, which halewe you.
“Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Dole ku kiyaye Asabbataina. Wannan zai zama alama tsakanina da ku daga tsara zuwa tsara, saboda ku sani ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.
14 Kepe ye my sabat, for it is hooli to you; he that defoulith it, schal die bi deeth, the soule of hym, that doith werk in the sabat, schal perische fro the myddis of his puple.
“‘Ku kiyaye Asabbaci, domin yă zama mai tsarki a gare ku. Duk wanda ya ƙazantar da shi, za a kashe shi; duk wanda ya yi wani aiki a ranar, za a ware shi daga mutane.
15 Sixe daies ye schulen do werk; in the seuenthe dai is sabat, hooli reste to the Lord; ech man that doith werk in this dai schal die.
Kwana shida, za a yi aiki, amma a rana ta bakwai, Asabbaci ne na hutu, mai tsarki ga Ubangiji. Duk wanda ya yi wani aiki a Asabbaci, za a kashe shi.
16 The sones of Israel kepe sabat, and halewe it in her generaciouns;
Isra’ilawa za su kiyaye Asabbaci, suna bikinsa daga tsara zuwa tsara a matsayin madawwamin alkawari.
17 it is a couenaunt euerlastinge bitwixe me and the sones of Israel, and it is `a signe euerlastynge; for in sixe daies God made heuene and erthe, and in the seuenthe day he ceessid of werk.
Zai zama alama tsakanina da Isra’ilawa har abada, gama cikin kwana shida Ubangiji ya yi sama da ƙasa, a rana ta bakwai kuma ya daina aiki, ya kuma huta.’”
18 And whanne siche wordis weren fillid, the Lord yaf to Moises, in the hil of Synay, twei stonun tablis of witnessyng, writun with the fyngur of God.
Sa’ad da Ubangiji ya gama yin wa Musa magana a kan Dutsen Sinai, sai ya ba shi alluna biyu na Alkawari, allunan duwatsu rubutattu da yatsan Allah.

< Exodus 31 >