< Exodus 3 >
1 Forsothe Moises kepte the scheep of Jetro, `his wyues fadir, preest of Madian; and whanne he hadde dryue the floc to the ynnere partis of deseert, he cam to Oreb, the hil of God.
Ana nan wata rana Musa yana kiwon tumakin Yetro surukinsa, firist na Midiyan, sai ya bi da tumaki zuwa gefe mai nisa a cikin hamada, har ya zo Horeb, dutsen Allah.
2 Forsothe the Lord apperide to hym in the flawme of fier fro the myddis of the buysch, and he seiy that the buysch brente, and was not forbrent.
A can mala’ikan Ubangiji ya bayyana a gare shi cikin harshen wuta, a ƙaramin itace. Musa ya lura cewa ko da yake wuta na ci ƙaramin itacen, amma bai ƙone ba.
3 Therfor Moyses seide, Y schal go and schal se this greet siyt, whi the buysch is not forbrent.
Sai Musa ya ce, “Wannan abin mamaki ne, don me wannan itace bai ƙone ba? Bari in matso kusa in gani.”
4 Sotheli the Lord seiy that Moises yede to se, and he clepide Moises fro the myddis of the buysch, and seide, Moyses! Moises! Which answeride, Y am present.
Da Ubangiji ya ga Musa ya matso don yă duba, sai Allah ya yi kira daga cikin ƙaramin itacen ya ce, “Musa! Musa!” Sai Musa ya amsa ya ce, “Ga ni.”
5 And the Lord seide, Neiye thou not hidur, but vnbynde thou the scho of thi feet, for the place in which thou stondist is hooli lond.
Allah ya ce, “Kada ka zo kusa, tuɓe takalmanka, gama inda kake tsaye, wuri ne mai tsarki.”
6 And the Lord seide, Y am God of thi fadir, God of Abraham, and God of Isaac, and God of Jacob. Moises hidde his face, for he durste not biholde ayens God.
Sai Allah ya ce, “Ni ne Allah na kakanninka, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub.” Da jin wannan, sai Musa ya ɓoye fuskarsa, domin ya ji tsoro yă dubi Allah.
7 To whom the Lord seide, Y seiy the affliccion of my puple in Egipt, and Y herde the cry therof, for the hardnesse of hem that ben souereyns of werkis.
Ubangiji ya ce, “Tabbatacce na ga azabar mutanena a Masar. Na ji su suna kuka saboda matsin da shugabannin gandunsu suke musu, na kuma damu da wahalarsu.
8 And Y knew the sorewe of the puple, and Y cam down to delyuere it fro the hondis of Egipcians, and lede out of that lond in to a good lond and brood, into a lond that flowith with milk and hony, to the places of Cananey, and of Ethei, of Amorrey, and of Feresei, of Euey, and of Jebusei.
Saboda haka na sauko domin in cece su daga hannun Masarawa, in kuma fitar da su daga ƙasar Masar, in kai su ƙasa mai kyau mai fāɗi, ƙasa mai zub da madara da zuma, inda Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa suke.
9 Therfor the cry of the sones of Israel cam to me, and Y seiy the turment of hem, bi which thei ben oppressid of Egipcians.
Yanzu kukan Isra’ilawa ya kai gare ni, na kuma ga yadda Masarawa suke wulaƙanta su
10 But come thou, I schal sende thee to Farao, that thou lede out my puple, the sones of Israel, fro Egipt.
To, fa, sai ka tafi. Ina aikan ka wurin Fir’auna don ka fitar da mutanena Isra’ilawa daga Masar.”
11 And Moises seide to hym, Who am Y, that Y go to Farao, and lede out the sones of Israel fro Egipt?
Amma Musa ya ce wa Allah, “Wane ni in tafi wurin Fir’auna, in kuma fitar da Isra’ilawa daga Masar?”
12 And the Lord seide to Moises, Y schal be with thee, and thou schalt haue this signe, that Y haue sent thee, whanne thou hast led out my puple fro Egipt, thou schalt offre to God on this hil.
Sai Allah ya ce, “Zan kasance da tare kai. Wannan kuwa za tă zama alama a gare ka cewa Ni na aike ka. Bayan ka fitar da mutanen daga Masar, za ku yi sujada ga Allah a kan dutsen nan.”
13 Moises seide to God, Lo! Y schal go to the sones of Israel, and Y schal seie to hem, God of youre fadris sente me to you; if thei schulen seie to me, what is his name, what schal Y seie to hem?
Musa ya ce wa Allah, “A ce ma na tafi wurin Isra’ilawa na ce musu, ‘Allah na kakanninku ya aiko ni wurinku,’ in suka tambaye ni, ‘Mene ne sunansa?’ Me zan ce?”
14 The Lord seide to Moises, Y am that am. The Lord seide, Thus thou schalt seie to the sones of Israel, He that is sente me to you.
Allah ya ce wa Musa, “NI NE wanda NINE. Abin da za ka faɗa wa Isra’ilawa ke nan cewa, ‘NI NE, ya aiko ni wurinku.’”
15 And eft God seide to Moises, Thou schalt seie these thingis to the sones of Israel, The Lord God of youre fadris, God of Abraham, and God of Isaac, and God of Jacob, sente me to you; this name is to me with outen ende, and this is my memorial in generacioun and in to generacioun.
Allah ya kuma ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ubangiji, Allah na kakanninka, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub, ya aiko ni wurinku.’ Wannan shi ne sunana har abada, sunan da za a tuna da ni daga tsara zuwa tsara ke nan.
16 Go thou, gadere thou the eldere men, that is, iugis, of Israel, and thou schalt seie to hem, The Lord God of youre fadris apperide to me, God of Abraham, and God of Ysaac, and God of Jacob, and seide, Y visitynge haue visitid you, and Y seiy alle thingis that bifelden to you in Egipt;
“Tafi ka tattara dattawan Isra’ila, ka ce musu, ‘Ubangiji, Allah na kakanninku, Allah na Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, ya bayyana a gare ni ya ce, Na lura da ku, na kuma ga abubuwan da ake yi muku a Masar.
17 and Y seide, that Y lede out you fro the affliccioun of Egipt in to the lond of Cananey, and of Ethei, and of Amorrei, and of Ferezei and of Euei, and of Jebusei, to the lond flowynge with mylk and hony.
Na kuma yi alkawari, zan fitar da ku daga azabarku a Masar zuwa ƙasar Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa, ƙasa mai zub da madara da zuma.’
18 And thei schulen here thi vois; and thou schalt entre, and the eldere men of Israel to the kyng of Egipt, and thou schalt seie to hym, The Lord God of Ebrews clepide vs; we schulen go the weie of thre daies in to wildirnesse, that we offre to oure Lord God.
“Dattawan Isra’ila za su saurare ka. Sa’an nan da kai da dattawan Isra’ila, za ku tafi wurin sarkin Masar, ku ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya sadu da mu. Bari mu yi tafiyar kwana uku zuwa cikin hamada domin mu yi hadaya wa Ubangiji Allahnmu.’
19 But Y woot, that the kyng of Egipt schal not delyuere you that ye go, but bi strong hond;
Amma na san cewa sarkin Masar ba zai yarda ku tafi ba, sai hannu mai ƙarfi ya tilasta shi.
20 for Y schal holde forthe myn hond, and I schal smyte Egipt in alle my marueils, whiche Y schal do in the myddis of hem; aftir these thingis he schal delyuere you.
Saboda haka zan miƙa hannuna in bugi Masarawa da duk al’ajaban da zan aikata a cikinsu. Bayan haka zai bar ku, ku tafi.
21 And Y schal yyue grace to this puple bifore Egipcians, and whanne ye schulen go out, ye schulen not go out voide;
“Zan kuma sa mutanen su sami tagomashi daga wurin Masarawa, saboda sa’ad da za ku fita, ba za ku fita hannu wofi ba.
22 but a womman schal axe of hir neiyboresse and of her hoosteesse siluerne vesselis, and goldun, and clothis, and ye schulen putte tho on youre sones and douytris, and ye schulen make nakid Egipt.
Kowace mace ta tambayi maƙwabciyarta, da kuma duk wata macen da take cikin gidanta, kayayyakin azurfa da na zinariya da kuma na riguna, waɗanda za ku sa wa’ya’yanku maza da mata. Ta haka nan za ku washe Masarawa.”