< Exodus 24 >

1 Also he seide to Moises, `Stie thou to the Lord, thou, and Aaron, and Nadab, and Abyu, and seuenti eldere men of Israel; and ye schulen worschipe afer,
Ana nan sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ku hauro zuwa wurina, kai da Haruna, Nadab da Abihu, da kuma dattawa saba’in a cikin Isra’ila. Za ku yi sujada da ɗan nisa,
2 and Moises aloone stie to the Lord, and thei schulen not neiye, nether the puple schal stie with hym.
sai Musa kaɗai zai kusaci Ubangiji. Amma sauran kada su zo kusa, kada kuma jama’a su hau tare da shi.”
3 Therfore Moises cam, and telde to the puple alle the wordis and domes of the Lord; and al the puple answeride with o vois, We schulen do alle the wordis of the Lord, whiche he spak.
Sa’ad da Musa ya tafi ya faɗa wa mutanen duk kalmomin Ubangiji da dokokinsa, sai suka amsa da murya ɗaya suna cewa, “Duk abin da Ubangiji ya faɗa, za mu yi.”
4 Forsothe Moises wroot alle the wordis of the Lord; and he roos eerli, and bildide an auter to the Lord at the rootis of the hil, and he bildide twelue titlis bi twelue lynagis of Israel.
Sai Musa ya rubuta duk abin da Ubangiji ya faɗa. Ya tashi kashegari da sassafe ya gina bagade kusa da dutsen, ya aza al’amudai goma sha biyu bisa ga kabilu goma sha biyu na Isra’ila.
5 And he sente yonge men of the sones of Israel, and thei offriden brent sacrifices, and `thei offriden pesible sacrifices `to the Lord, twelue calues.
Sai ya aiki samarin Isra’ilawa, suka miƙa hadaya ta ƙonawa, suka kuma miƙa ƙananan bijimai don hadaya ta salama ga Ubangiji.
6 And so Moises took half the part of the blood, and sente in to grete cuppis; forsothe he schedde the residue part on the auter.
Musa ya ɗauki rabin jinin ya zuba a cikin kwanoni, rabin kuma ya yayyafa a kan bagaden.
7 And he took the book of the boond of pees, and redde, while the puple herde; whiche seiden, We schulen do alle thingis which the Lord spak, and we schulen be obedient.
Sa’an nan ya ɗauki Littafin Alkawari ya karanta wa mutane. Suka amsa suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa; za mu yi biyayya.”
8 Forsothe he took, and sprengide `the blood on the puple, and seide, This is the blood of the boond of pees, which the Lord couenauntide with yow on alle these wordis.
Musa ya kuma ɗauki jinin, ya yayyafa a kan mutanen ya ce, “Wannan shi ne jinin alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, bisa ga dukan waɗannan kalmomi.”
9 And Moises, and Aaron, and Nadab, and Abyu, and seuenti of the eldere men of Israel stieden,
Musa da Haruna, Nadab da Abihu, da dattawa saba’in, Allah na Isra’ila suka haura
10 and seiyen God of Israel, vndur hise feet, as the werk of safire stoon, and as heuene whanne it is cleer.
suka kuma ga Allah na Isra’ila. A ƙarƙashin ƙafafunsa akwai wani abu wanda aka yi da saffaya, mai haske kuma kamar sararin sama kansa.
11 And he sente not his hond on hem of the sones of Israel, that hadden go fer awei; and thei sien God, and eeten and drunkun.
Amma Allah bai yi wa shugabannin Isra’ila wani abu ba; suka ga Allah, suka ci suka kuma sha.
12 Forsothe the Lord seide to Moises, `Stie thou to me in to the hil, and be thou there, and Y schal yyue to thee tablis of stoon, and the lawe, and comaundementis, whiche Y haue write, that thou teche the children of Israel.
Ubangiji ya ce wa Musa, “Hauro wurina a kan dutse, ka tsaya a nan, zan ba ka allunan dutsen, da doka da umarnan da na rubuta don koyonsu.”
13 Moises and Josue his mynystre risen, and Moises stiede in to the hil of God,
Sa’an nan Musa ya fita tare da Yoshuwa mataimakinsa, ya kuwa hau kan dutsen Allah.
14 and seide to the eldere men, Abide ye here, til we turnen ayen to you; ye han Aaron and Hur with you, if ony thing of questioun is maad, ye schulen telle to hem.
Ya ce wa dattawan, “Ku jira mu a nan, sai mun dawo wurinku. Haruna da Hur suna tare da ku, in wani yana da wata damuwa, sai yă je wurinsu.”
15 And whanne Moises hadde stied,
Da Musa ya hau dutsen, sai girgije ya rufe dutsen,
16 a cloude hilide the hil, and the glorie of the Lord dwellide on Synai, and kyueride it with a cloude sixe daies; forsothe in the seuenthe dai the Lord clepide hym fro the myddis of the cloude; forsothe the licnesse of glorie of the Lord
sai ɗaukakar Ubangiji ta sauka a kan Dutsen Sinai, kwana shida girgije ya rufe dutsen, a rana ta bakwai, sai Ubangiji ya kira Musa daga cikin girgijen.
17 was as fier brennynge on the cop of the hil in the siyt of the sones of Israel.
Ga Isra’ilawa dai, ɗaukakar Ubangiji ta yi kamar wuta mai ci a kan dutse.
18 And Moises entride into the myddis of the cloude, and stiede in to the hil, and he was there fourti daies and fourti nyytis.
Sa’an nan Musa ya shiga girgijen ya hau kan dutsen. Ya zauna a kan dutsen yini arba’in da dare arba’in.

< Exodus 24 >