< Deuteronomy 9 >

1 Here thou, Israel; thou schalt passe Jordan to dai, that thou welde mooste naciouns, and strengere than thou; grete citees, and wallid `til to heuene;
Ku ji, ya Isra’ila. Kuna gab da haye Urdun, ku shiga, ku kuma kori al’ummai da suka fi ku yawa, suka kuma fi ku ƙarfi, masu manyan biranen da suke da katangar da suka yi tsaye zuwa sama.
2 a greet puple, and hiy; the sones of Enachym, whiche thi silf `siest, and herdist, whiche no man may ayenstonde in the contrarie part.
Mutane ne masu ƙarfi, kuma dogaye, zuriyar Anakawa! Ai, kun ji akan ce, “Wa zai iya tsayayya da Anakawa?”
3 Therfor thou schalt wite to dai, that thi Lord God hym silf schal passe bifor thee; he is a fier deuourynge and wastynge, that schal al to breke hem, and schal do awei, and destrie bifor thi face swiftli, as he spak to thee.
Amma ku zauna da sani a yau, cewa Ubangiji Allahnku, shi ne wanda ya ƙetare ya sha gabanku kamar wuta mai cinyewa. Zai hallaka su, zai rinjaye su a gabanku. Za ku kore su, ku kuma hallaka su nan da nan, yadda Ubangiji ya yi muku alkawari.
4 Seie thou not in thin herte, whanne thi Lord God hath do hem awey in thi siyt, For my riytfulnesse the Lord brouyte me yn, that Y schulde welde this lond; sithen these naciouns ben doon awey for her wickidnessis.
Bayan Ubangiji Allahnku ya kore su a gabanku, kada ku faɗa a zuciyarku, “Ubangiji ya kawo mu a nan, mu mallaki wannan ƙasa saboda adalcinmu ne.” A’a, saboda muguntar waɗannan al’umma ne ya sa Ubangiji ya kore su a gabanku.
5 For not for thi riytfulnessis, and equyte of thin herte thou schalt entre that thou welde the lond `of hem; but for thei diden wickidli, thei weren doon awey, whanne thou entridist, and that the Lord schulde fille his word which he bihiyte vndur an ooth to thi fadris, to Abraham, Isaac, and Jacob.
Ba domin adalci ko mutuncinku ba ne ya sa za ku mallaki ƙasarsu; sai dai saboda muguntar al’umman nan ne ya sa Ubangiji Allahnku yana korinsu a gabanku don yă cika abin da ya rantse wa kakanninku, wato, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
6 Therfor wite thou that not for thi riytfulnesses thi Lord God yaf to thee this beste lond in to possessioun, sithen thou art a puple of hardeste nol.
Ku gane wannan, cewa ba domin adalcinku ba ne ya sa Ubangiji Allahnku yana ba ku wannan ƙasa mai kyau, ku mallaki, gama ku mutane masu taurinkai ne.
7 Haue thou mynde, and foryete not, hou in the wildirnesse thou terridist thi Lord God to greet wraththe; fro that dai in which thou yedist out of Egipt `til to this place, thou striuedist euere ayens the Lord.
Ku tuna da wannan, kada kuma ku manta yadda kuka tsokane Ubangiji Allahnku, har ya yi fushi a hamada. Daga ranar da kuka bar Masar har sai da kuka isa nan, kuna ta tawaye wa Ubangiji.
8 For whi also in Oreb thou terridist hym, and he was wrooth, and wolde do thee awei, whanne Y stiede in to the hil,
A Horeb, kun tayar wa Ubangiji har ya yi fushin da ya isa yă hallaka ku.
9 that Y schulde take two tablis of stoon, the tablis of couenaunt which the Lord made with you, and Y continuede in the hil fourti daies and nyytis, and Y eet not breed, and Y drank not watir.
Sa’ad da na hau kan dutse don in karɓi allunan dutse, allunan alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, na zauna a kan dutse yini arba’in da dare arba’in; ban ci abinci ba, ban sha ruwa ba.
10 And the Lord yaf to me, twey tablis of stoon, euer either wrytun with Goddis fyngur, and conteynynge alle the wordis whiche he spak to you in the hil, fro the myddis of the fier, whanne the cumpany of puple was gaderid togidere.
Ubangiji ya ba ni alluna biyu wanda shi kansa ya yi rubutu da yatsarsa. A kansu akwai dukan umarnan Ubangiji da an furta muku a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar taron jama’a.
11 And whanne fourti daies and so many nyytis hadden passid, the Lord yaf to me twei tablis of stoon, tablis of boond of pees;
A ƙarshen yini arba’in da dare arba’in ɗin, Ubangiji ya ba ni alluna biyu na dutse, allunan alkawari.
12 and he seide to me, Rise thou, and go doun for hennys soone, for thi puple, which thou leddist out of Egipt, han forsake swiftli the weie which thou schewidist to hem, and thei han maad to hem a yotun calf.
Sa’an nan Ubangiji ya faɗa mini, “Sauka daga nan da sauri, domin mutanenka waɗanda ka fitar da su daga Masar sun lalace. Sun juye da sauri daga abin da na umarce su, suka kuma yi zubin gunki wa kansu.”
13 And eft the Lord seide to me, `Y se that this puple is of hard nol;
Sai Ubangiji ya ce mini, “Na ga mutanen nan, su masu taurinkai ne sosai!
14 suffre thou me, that I alto breke hym, and do awey the name `of hym fro vndur heuene; and Y schal ordeyne thee on a folk which is grettere and strongere than this folk.
Bar ni kawai, in hallaka su, in kuma shafe sunansu daga ƙarƙashin sama. Zan kuwa yi maka wata al’umma mafi ƙarfi da kuma masu yawa fiye da su.”
15 And whanne Y cam doun fro the hil brennynge, and helde with euer either hond twei tablis of boond of pees, and Y seiy,
Saboda haka na juya, na sauko daga dutsen yayinda yake cin wuta. Allunan biyu na alkawarin kuma suna a hannuwana.
16 that ye hadde synned to youre Lord God, and hadden maad to you a yotun calf, and hadden forsake swiftli the weie of God which he schewide to you,
Sa’ad da na duba, sai na ga cewa kun yi zunubi wa Ubangiji Allahnku; kun yi wa kanku gunkin da kuka yi zubi a siffar ɗan maraƙi. Kun kauce da sauri daga hanyar da Ubangiji ya umarce ku.
17 Y castide doun the tablis fro myn hondis, and brak tho tablis in youre siyt.
Saboda haka na ɗauko alluna biyun na jefar da su daga hannuwana, na farfashe su a idanunku.
18 And Y felde doun bifor the Lord as `biforto, in fourti daies and fourti nyytis, and Y eet not breed, `and drank not watir, for alle youre synnes whiche ye diden ayens the Lord, and terriden hym to `greet wraththe;
Sai nan da nan kuma na fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji, yini arba’in da dare arba’in; ban ci ba, ban sha ba, kamar yadda dā na yi, duka saboda zunubin da kuka aikata a gaban Ubangiji. Ta haka kuka tsokane shi don yă yi fushi.
19 for Y dredde the indignacioun and yre of hym, by which he was stirid ayens you, and wolde do you awey. And the Lord herde me also in this tyme.
Na ji tsoron fushi da hasalar Ubangiji, gama ya yi fushin da ku da ya isa yă hallaka ku. Amma na yi roƙo a lokacin, Ubangiji kuwa ya saurare ni.
20 Also the Lord was wrooth greteli ayens Aaron, and wolde alto breke hym, and Y preiede in lijk maner for hym.
Ubangiji ya yi fushi sosai da Haruna, har ya yi niyya yă hallaka shi, amma a wannan lokaci, na yi addu’a saboda Haruna shi ma.
21 `Forsothe Y took youre synne which ye maden, that is, the calf, and brente it in fier, and Y alto brak in gobetis, and droof outerli in to dust, and castide forth in to the stronde, that cam doun fro the hil.
Sa’an nan na ɗauki kayan zunubin da kuka yi, wato, gunkin ɗan bijimi, na ƙone shi da wuta, na farfashe shi, na niƙa shi liɓis, sai da ya zama kamar ƙura mai laushi, na zubar da ƙurar a cikin ruwan rafin da yake gangarowa daga dutse.
22 Also in the brennyng, and in the temptacioun at the watris of ayenseiyng, and in the Sepulcris of Coueytise, ye terriden the Lord;
Kun kuma sa Ubangiji ya yi fushi a Tabera, a Massa da kuma a Kibrot Hatta’awa.
23 and whanne Y sente you fro Cades Barne, and seide, `Stye ye, and welde the lond which Y yaf to you, and ye dispisiden the comaundement of youre Lord God, and ye bileueden not to him, nether ye wolden here his vois;
Sa’ad da Ubangiji ya aike ku daga Kadesh Barneya ya ce, “Ku haura ku mallaki ƙasar da na ba ku.” Amma kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji Allahnku. Ba ku amince da shi, ko ku yi masa biyayya ba.
24 but euere ye weren rebel, fro the day in which Y bigan to knowe you.
Kun yi ta tawaye wa Ubangiji tun ran da na san ku.
25 And Y lay byfore the Lord fourti daies and fourti nyytis, in whiche Y bisouyte hym mekeli, that he schulde not `do awey you, as he manaasside.
Na kwanta rubda ciki a gaban Ubangiji waɗannan yini arba’in da dare arba’in domin Ubangiji ya ce zai hallaka ku.
26 And Y preiede, and seide, Lord God, distrye not thi puple, and thin eritage, which thou `ayen bouytist in thi greetnesse, which thou leddist out of Egipt in strong hond.
Na yi addu’a ga Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kada ka hallaka mutanenka, gādon kanka, da ka fansa ta wurin ikonka mai girma, ka kuma fitar da su daga Masar da hannu mai ƙarfi.
27 Haue thou mynde of thi seruauntis, of Abraham, Isaac, and Jacob; biholde thou not the hardnesse of this puple, and the wickidnesse, and the synne therof,
Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Kada ka kula da taurinkan, mugunta da kuma zunubin wannan mutane.
28 lest perauenture the dwelleris of the lond, out of which thou leddist vs, seien, The Lord myyte not bryng hem in to the lond which he bihiyte to hem, and he hatide hem; therfor he ledde hem out that he schulde sle hem in wildirnesse;
In ba haka ba, ƙasar da ka fitar da mu, za tă ce, ‘Domin Ubangiji bai iya kai su cikin ƙasar da ya yi musu alkawari ba ne, kuma domin ya ƙi su, shi ya sa ya fitar da su ya kashe su a hamada.’
29 and thei ben thi puple and thin eritage, which thou leddist out in thi greet strengthe, and in thin arm holdun forth.
Amma su mutanenka ne, gādonka da ka fitar ta wurin ikonka mai girma, da kuma hannunka mai ƙarfi.”

< Deuteronomy 9 >