< Deuteronomy 34 >
1 Therfor Moyses stiede fro the feeldi places of Moab on the hil of Nebo, in to the cop of Fasga, ayens Gerico. And the Lord schewide to hym al the lond of Galaad `til to Dan,
Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
2 and al Neptalym, and the lond of Effraym and of Manasses, and al the lond of Juda, `til to the laste see; and the south part,
da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
3 and the breede of the feeld of Jerico, of the citee of Palmes `til to Segor.
da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
4 And the Lord seide to hym, This is the lond for which Y swoor to Abraham, Isaac, and Jacob; and Y seide, Y schal yyue it to thi seed; thou hast seyn it with thin iyen, and thou schalt not passe `to it.
Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
5 And Moyses, the seruaunt of the Lord, was deed there, in the lond of Moab, `for the Lord comaundide.
Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
6 And the Lord biriede hym in a valey of the lond of Moab, ayens Fegor, and no man knewe his sepulcre `til in to present day.
Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
7 Moises was of an hundrid and twenti yeer whanne he diede; his iye dasewide not, nethir hise teeth weren stirid.
Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
8 And the sones of Israel biwepten hym thretti daies in the feeldi places of Moab; and the daies of weilyng of men `bymorenynge Moises weren fillid.
Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
9 Forsothe Josue, the sone of Nun, was fillid with `the spyrit of wisdom, for Moises settide hise hondis on hym; and the sones of Israel obeieden to Josue, and diden as the Lord comaundide to Moises.
To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
10 And `a profete roos no more in Israel `as Moises, whom the Lord knewe face to face,
Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
11 in alle myraclis, and grete wondris, whiche the Lord sente bi hym, that he schulde do in the lond of Egipt to Farao, and alle hise seruauntis, and to al the lond `of hym,
wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
12 and al strong hond, and the `grete merueylis, whiche Moyses dide bifor al Israel.
Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.