< Deuteronomy 32 >

1 Ye heuenes, here what thingis Y schal speke; the erthe here the wordis of my mouth.
Ku saurara, ya ku sammai, zan yi magana; bari duniya ta ji maganar bakina.
2 My techyng wexe togidere as reyn; my speche flete out as dew, as lytil reyn on eerbe, and as dropis on gras.
Bari koyarwata tă zubo kamar ruwan sama kalmomina kuma su sauko kamar raɓa, kamar yayyafi a kan sabuwar ciyawa, kamar ruwan sama mai yawa a kan tsirai marasa ƙarfi.
3 For Y schal inwardli clepe the name of the Lord; yyue ye glorie to oure God.
Zan yi shelar sunan Ubangiji. Ku yabi girman Allahnmu!
4 The werkis of God ben perfit, and alle hise weies ben domes; God is feithful, and without ony wickidnesse; God is iust and riytful.
Shi Dutse ne, ayyukansa cikakku ne, dukan hanyoyinsa kuwa masu adalci ne. Allah mai aminci, wanda ba ya yin rashi gaskiya, shi mai adalci ne, nagari ne kuma.
5 Thei synneden ayens hym, and not hise sones in filthis, `that is, of idolatrie; schrewid and waiward generacioun.
Sun aikata mugunta a gabansa; saboda abin kunyarsu, su ba’ya’yansa ba ne, amma wata muguwar tsara ce, karkatacciya.
6 Whether thou yeldist these thingis to the Lord, thou fonned puple and vnwijs? Whether he is not thi fadir, that weldide thee, and made, `and made thee of nouyt?
Haka za ku biya Ubangiji, Ya ku wawaye da kuma mutane marasa hikima? Shi ba Ubanku ba ne, Mahaliccinku, wanda ya yi ku, ya kuma siffanta ku?
7 Haue thou minde of elde daies, thenke thou alle generaciouns; axe thi fadir, and he schal telle to thee, axe thi grettere men, and thei schulen seie to thee.
Ku tuna da kwanakin dā, ku tuna da tsararrakin da suka wuce tun tuni, Ku tambayi iyayenku, za su faɗa muku, dattawanku, za su kuma bayyana muku.
8 Whanne the hiyeste departide folkis, whanne he departide the sones of Adam, he ordeynede the termes of puplis bi the noumbre of the sones of Israel.
Sa’ad da Mafi Ɗaukaka ya ba da al’ummai gādonsu, sa’ad da ya raba dukan’yan adam, ya kafa iyakoki wa mutane bisa ga yawan’ya’yan Isra’ila maza.
9 Forsothe the part of the Lord is his puple; Jacob is the litil part of his eritage.
Gama rabon Ubangiji shi ne mutanensa, Yaƙub shi ne rabon gādonsa.
10 The Lord foond hym in a deseert lond, `that is, priued of Goddis religioun, in the place of orrour `ethir hidousnesse, and of wast wildirnesse; the Lord ledde hym aboute, and tauyte hym, and kepte as the apple of his iye.
A cikin hamada ya same shi, a jeji marar amfani, inda namomi suke kuka. Ya tsare shi, ya kuma lura da shi; ya bi da shi kamar ƙwayar idonsa,
11 As an egle stirynge his briddis to fle, and fleynge on hem, he spredde forth his wyngis, and took hem, and bar in hise schuldris.
kamar gaggafar da take yawo a kan sheƙarta tana rufe’ya’yanta, ta buɗe fikafikanta don tă kwashe su tă ɗauke su a kafaɗunta.
12 The Lord aloone was his ledere, and noon alien god was with hym.
Ubangiji kaɗai ya jagorance shi; babu wani baƙon gunkin da yake tare da shi.
13 The Lord ordeynede hym on an hiy lond, that he schulde ete the fruytis of feeldis, that he schulde souke hony of a stoon, and oile of the hardeste roche;
Ya sa shi ya hau ƙwanƙolin dutse ya ciyar da shi da amfanin gona. Ya shayar da shi da zuma daga dutse, da kuma mai daga dutsen ƙanƙara,
14 botere of the droue, and mylke of scheep, with the fatnesse of lambren and of rammes, of the sones of Basan; and that he schulde ete kydis with the merowe of wheete, and schulde drynke the cleereste blood of grape.
da kindirmo da madara daga shanu da tumaki da ƙibabbun tumaki da awaki, da zaɓaɓɓun ragunan Bashan da kuma ƙwayoyin alkama mafi kyau. Ka sha ruwan inabi ja wur mai kumfa.
15 The louede puple was `maad fat, and kikide ayen; maad fat withoutforth, maad fat with ynne, and alargid; he forsook God his makere, and yede awei fro `God his helthe.
Yeshurun ya yi ƙiba, ya yi kauri; cike da abinci, ya zama da nauyi, ya kuma zama sumul. Ya yashe Allahn da ya yi shi, ya ƙi Dutse Cetonsa.
16 Thei terriden hym to ire in alien goddis, and thei excitiden to wrathfulnesse in abhomynaciouns.
Suka sa shi kishi saboda baƙin allolinsu, suka husata shi da gumakan banƙyamarsu.
17 Thei offriden to feendis, and not to God, to goddis whiche thei knewen not, newe goddis, and freische camen, whiche `the fadris of hem worschipiden not.
Suka yi hadaya ga aljanu, waɗanda ba Allah ba, ga allolin da ba su sani ba, ga allolin da aka shigo da su daga baya, allolin da kakanninku ba su ji tsoronsu ba.
18 Thou hast forsake God that gendride thee, and thou hast foryete `thi Lord creatour.
Kuka rabu da Dutsen da ya zama mahaifi gare ku; kuka manta da Allahn da ya haife ku.
19 The Lord siy, and was stirid to wrathfulnesse; for hise sones and douytris terriden hym.
Ubangiji ya ga wannan ya kuma ƙi su, domin’ya’yansa maza da mata sun husata shi.
20 And the Lord seide, Y schal hyde my face fro hem, and Y schal biholde `the laste thingis of hem; for it is a waiward generacioun, and vnfeithful sones.
Ya ce, “Zan ɓoye fuskata daga gare su, in ga ƙarshensu; gama su muguwar tsara ce,’ya’ya ne marasa aminci.
21 Thei terriden me in hym that was not God, and thei `terriden to ire in her vanytees; and Y schal terre hem in hym, that is not a puple, and Y schal terre hem `to yre in a fonned folk.
Sun sa ni kishi ta wurin abin da ba allah ba, suka kuma husata ni da gumakansu na wofi. Zan sa su yi kishi ta wurin waɗanda ba mutane ba; zan sa su yi fushi ta wurin al’ummar da ba ta da sani.
22 Fier, that is, peyne maad redi to hem, is kyndlid in my stronge veniaunce, and it schal brenne `til to the laste thingis of helle; and it schal deuoure the lond with his fruyt, and it schal brenne the foundementis of hillis. (Sheol h7585)
Gama fushina ya kama wuta, tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za tă cinye duniya da girbinta, tă kuma sa wuta a tussan duwatsu. (Sheol h7585)
23 Y schal gadere `yuels on hem, and Y schal fille myn arewis in hem.
“Zan tula masifu a kansu in kuma gama kibiyoyina a kansu.
24 Thei schulen be waastid with hungur, and briddis schulen deuoure hem with bitteriste bityng; Y schal sende in to hem the teeth of beestis, with the woodnesse of wormes drawynge on erthe, and of serpentis.
Zan aika da yunwa mai tsanani a kansu, zazzaɓi mai zafi da muguwar annoba; zan aika da haƙoran namun jeji a kansu, da dafin mesa masu ja da ciki.
25 Swerd with outforth and drede with ynne schal waaste hem; a yong man and a virgyn togidre, a soukynge child with an elde man.
Waɗanda suke a waje, takobi zai kashe su, a cikin gidajensu kuma tsoro zai mamaye su.’Yan maza da’yan mata za su hallaka, haka ma jarirai da maza masu furfura.
26 And Y seide, Where ben thei? Y schal make the mynde of hem to ceesse of men.
Na ce zan watsar da su in sa a manta da su a tunanin’yan adam.
27 But Y delayede for the yre of enemyes, lest perauenture `the enemyes of hem shulden be proude, and seie, Oure hiy hond, and not the Lord, dide alle these thingis.
Amma ina tsoron tsokanar abokin gāba, don kada abokan gāba su kāsa ganewa har su ce, ‘Hannunmu ne ya yi nasara; ba Ubangiji ne ya aikata dukan wannan ba.’”
28 It is a folk with out counsel, and with out prudence;
Al’ummai ne marasa azanci, babu ganewa a cikinsu.
29 Y wolde that thei saueriden, and `vnderstoden, and purueiden the laste thingis.
A ce su masu hikima ne har su gane wannan su gane abin da ƙarshensu zai zama!
30 How pursuede oon of enemyes a thousynde of Jewis, and tweyne dryuen awey ten thousynde? Whether not therfore for her God selde hem, and the Lord closide hem togidere?
Yaya mutum guda zai kore dubu, mutum biyu su sa dubu goma su gudu, sai ko Dutsensu ya sayar da su, sai ko Ubangiji ya bashe su.
31 For oure God is not as the goddis of hem, and oure enemyes ben iugis.
Gama dutsensu ba kamar Dutsenmu ba ne, abokan gābanmu sun san da haka.
32 The vyner of hem is of the vyner of Sodom, and of the subarbis of Gomorre; the grape of hem is the grape of galle, and the clustre is most bittir.
Kuringarsu ta fito daga kuringar Sodom ne, daga gonakin Gomorra kuma.’Ya’yan inabinsu dafi ne, nonnansu masu ɗaci ne.
33 The galle of dragouns is the wyn of hem, and the venym of eddris, that may not be heelid.
Ruwan inabinsu dafin macizai ne, mugun dafin gamshaƙa ne.
34 Whether these thingis ben not hid at me, and ben seelid in myn tresouris?
“Ban jibge wannan a ma’ajiya na kuma yimƙe shi a taskokina ba?
35 Veniaunce is myn, and Y schal yelde to hem in tyme, that the foot of hem slide; the dai of perdicioun is nyy, and tymes hasten to be present.
Sakayya nawa ne, zan kuwa ɗau fansa. A cikin lokaci, ƙafarsu za tă yi santsi; ranar masifarsu ta yi kusa hallakarsu kuma tana gaggautawa a kansu.”
36 The Lord schal deme his puple, and he schal do merci in hise seruauntis; the puple schal se that the hond of fiyteres is sijk, and also men closid failiden, and the residues ben waastid.
Ubangiji zai shari’anta mutanensa yă kuma ji tausayin bayinsa sa’ad da ya ga ƙarfinsu ya ƙare babu kowa kuma da ya rage, bawa ko’yantacce.
37 And thei schulen seie, Where ben `the goddis of hem, in whiche thei hadden trust?
Zai ce, “To, ina allolinsu, dutsen da suka yi mafaka a ciki,
38 Of whos sacrifices thei eeten fatnessis, and drunkun the wyn of fletynge sacrifices, rise thei and helpe you, and defende thei you in nede.
allolin da suka ci kitsen hadayunsu suka kuma sha ruwan inabin hadayunsu? Ku sa su tashi su taimake ku mana! Bari su ba ku mafaka!
39 Se ye that Y am aloone, and noon other God is outakun me; Y schal sle, and Y schal make to lyue; Y schal smyte, and Y schal make hool; and noon is that may delyuere fro myn hond.
“Ku duba yanzu cewa ni ne Shi! Ba wani allah in ban da ni. Nakan kashe in kuma rayar, nakan sa rauni in kuma warkar, ba wanda yake da iko yă cece wani daga hannuna.
40 And Y schal reise myn hond to heuene, and Y schal seie, Y lyue with outen ende.
Na ɗaga hannu sama na kuma furta. Muddin ina raye har abada,
41 If Y schal whette my swerd as leit, and myn hond schal take doom, Y schal yelde veniaunce to myn enemyes, and Y schal quyte to hem that haten me.
sa’ad da na wasa takobi mai walƙiya hannuna kuwa ya cafke shi don yin hukunci, zan ɗau fansa a kan abokan gābana in sāka wa waɗanda suke ƙina.
42 Y schal fille myn arewis with blood, and my swerd schal deuoure fleischis of the blood of hem that ben slayn, and of the caitifte of the heed of enemyes maad nakid.
Zan sa kibiyoyina su bugu da jini, yayinda takobina yana cin nama, jinin kisassu da na kamammu, kawunan shugabannin abokan gāba.”
43 Folkis, preise ye the puplis of hym, for he schal venie the blood of hise seruauntis, and he schal yelde veniaunce in to the enemyes of hem; and he schal be merciful to the lond of his puple.
Ku yi farin ciki, ya ku al’ummai, tare da mutanensa, gama zai rama ɗau fansar jinin bayinsa; zai ɗau fansa a kan abokan gābansa yă kuma yi kafara domin ƙasarsa da mutanensa.
44 Therfor Moises cam, and spak alle the wordis of this song in the eeris of the puple; bothe he and Josue, the sone of Nun.
Sai Musa ya zo da Yoshuwa ɗan Nun suka faɗa dukan waɗannan kalmomi wannan waƙa a kunnen mutane.
45 And `he fillide alle these wordis, and spak to alle Israel, and seide to hem,
Sa’ad da Musa ya gama karanta waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila,
46 Putte ye youre hertis in to alle the wordis whiche Y witnesse to you to day, that ye comaunde to youre sones, to kepe, and do tho, and to fulfille alle thingis that ben writun in the book of this lawe;
ya ce musu, “Ku riƙe dukan kalmomin da na furta muku a yau, don ku umarce’ya’yanku su lura, su yi biyayya da dukan kalmomin wannan doka.
47 for not in veyn tho ben comaundid to you, but that alle men schulden lyue in tho; whiche wordis ye schulen do, and schulen contynue in long tyme in the lond, to which ye schulen entre to welde, whanne Jordan is passid.
Ba kalmomi kurum ba ne dominku, amma har ranku ma. Ta wurinsu za ku yi tsawon rai a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
48 And the Lord spak to Moises in the same day,
A wannan rana Ubangiji ya ce wa Musa,
49 and seide, Stie thou in to this hil Abirym, that is, passyng, in to the hil of Nebo, which is in the lond of Moab, ayens Jerico; and se thou the lond of Canaan, which Y schal yyue to the sones of Israel to holde, and die thou in the hil.
“Ka hau Duwatsun Abarim zuwa Dutsen Nebo a Mowab, tsallake daga Yeriko, ka hangi Kan’ana, ƙasar da nake ba wa Isra’ilawa gādo.
50 In to which hil thou schalt stie, and schalt be ioyned to thi puplis, as Aaron, thi brother, was deed in the hil of Hor, and was put to his puplis.
A can kan dutsen da ka hau za ka mutu a kuma tara ka ga mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya mutu a Dutsen Hor aka kuma tara shi ga mutanensa.
51 For ye trespassiden ayens me, in the myddis of the sones of Israel, at the Watris of Ayenseiyng, in Cades of deseert of Syn; and ye halewiden not me among the sones of Israel.
Wannan kuwa domin ku biyu kun fid da aminci gare ni a gaban Isra’ilawa a ruwan Meriba ta Kadesh, a Hamadar Zin kuma saboda ba ku riƙe tsarkina a cikin Isra’ilawa ba.
52 Ayenward thou schalt se the lond, and schalt not entre in to it, which Y schal yyue to the sones of Israel.
Saboda haka, za ka ga ƙasar daga nesa kawai; ba za ka shiga ƙasar da nake ba wa mutanen Isra’ila ba.”

< Deuteronomy 32 >