< Amos 5 >
1 Here ye this word, for Y reise on you a weilyng.
Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
2 The hous of Israel felle doun, he schal not put to, that it rise ayen; the virgyn of Israel is cast doun in to hir lond, noon is that schal reise hir.
“Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
3 For the Lord God seith these thingis, The citee of which a thousynde wenten out, an hundrid schulen be left ther ynne; and of which an hundrid wenten out, ten schulen be left ther ynne, in the hous of Israel.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
4 For the Lord seith these thingis to the hous of Israel, Seke ye me, and ye schulen lyue;
Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
5 and nyle ye seke Bethel, and nyle ye entre in to Galgala, and ye schulen not passe to Bersabee; for whi Galgal schal be led caitif, and Bethel schal be vnprofitable.
kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
6 Seke ye the Lord, and lyue ye, lest perauenture the hous of Joseph be brent as fier; and it schal deuoure Bethel, and there schal not be, that schal quenche.
Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
7 Whiche conuerten doom in to wermod, and forsaken riytwisnesse in the lond,
Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
8 and forsaken hym that makith Arture and Orion, and hym that turneth derknessis in to the morewtid, and him that chaungith dai in to niyt; which clepith watris of the see, and heldith out hem on the face of erthe; the Lord is name of hym.
(Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
9 Which scorneth distriyng on the stronge, and bringith robbyng on the myyti.
yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
10 Thei hatiden a man repreuynge in the yate, and thei wlatiden a man spekynge perfitli.
Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
11 Therfor for that that ye robbiden a pore man, and token fro hym the chosun prey, ye schulen bilde housis with square stoon, and ye schulen not dwelle in hem; ye schulen plaunte moost louyd vyneyerdis, and ye schulen not drynke the wyn of hem.
Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
12 For Y knew youre grete trespassis many, and youre stronge synnes; enemyes of `the riytwis man, takynge yifte, and berynge doun pore men in the yate.
Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
13 Therfor a prudent man schal be stille in that time, for the time is yuel.
Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
14 Seke ye good, and not yuel, that ye lyue, and the Lord God of oostis schal be with you, as ye seiden.
Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
15 Hate ye yuel, and loue ye good, and ordeyne ye in the gate doom; if perauenture the Lord God of oostis haue merci on the remenauntis of Joseph.
Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
16 Therfor the Lord God of oostis, hauynge lordschipe, seith these thingis, Weilyng schal be in alle stretis, and in alle thingis that ben withoutforth it schal be seid, Wo! wo! and thei schulen clepe an erthe tilier to mourenyng, and hem that kunnen weile, to weilyng.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
17 And weilyng schal be in alle weies, for Y schal passe forth in the myddil of `the see, seith the Lord.
Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
18 Wo to hem that desiren the dai of the Lord; wher to desiren ye it to you? This dai of the Lord schal be derknessis, and not liyt.
Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
19 As if a man renne fro the face of a lioun, and a bere renne to hym; and he entre in to the hous, and lene with his hond on the wal, and a serpent dwellynge in schadewe bite hym.
Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
20 Whether the dai of the Lord schal not be derknessis, and not liyt; and myist, and not schynyng ther ynne?
Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
21 Y hatide and castide awei youre feeste daies, and Y schal not take the odour of youre cumpenyes.
“Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
22 That if ye offren to me youre brent sacrifices, and yiftis, Y schal not resseyue, and Y schal not biholde avowis of youre fatte thingis.
Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
23 Do thou awei fro me the noise of thi songis, and Y schal not here the songis of thin harpe.
Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
24 And doom schal be schewid as watir, and riytfulnesse as a strong streem.
Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
25 Whether ye, the hous of Israel, offriden to me sacrifices for enemyes to be ouercomun, and sacrifice in desert fourti yeeris?
“Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
26 And ye han bore tabernaclis to Moloch, youre god, and ymage of youre idols, the sterre of youre god, which ye maden to you.
Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
27 And Y schal make you for to passe ouer Damask, seide the Lord; God of oostis is the name of him.
Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.