< Amos 3 >

1 Sones of Israel, here ye the word which the Lord spak on you, and on al the kynrede, which Y ledde out of the lond of Egipt,
Ku ji wannan maganar da Ubangiji ya yi game da ku, ya ku jama’ar Isra’ila, a kan dukan iyalin da na fitar daga Masar.
2 and seide, Oneli Y knewe you of alle the kynredis of erthe; therfor Y schal visite on you alle youre wickidnessis.
“Ku ne kaɗai na zaɓa cikin dukan al’umman duniya; saboda haka zan hukunta ku saboda dukan zunubanku.”
3 Whether tweyne schulen go togidere, no but it acorde to hem?
Mutum biyu za su iya yin tafiya tare in ba su yarda su yi haka ba?
4 Whether a lioun schal rore in a forest, no but he haue prey? Whether the whelp of a lioun schal yyue vois fro his denne, no but he take ony thing?
Zaki yakan yi ruri a jeji in bai sami kama nama ba? Zai yi gurnani a cikin kogonsa in bai kama kome ba?
5 Whether a brid schal falle in to a snare of erthe, with outen a foulere? Whether a snare schal be takun awei fro erthe, bifor that it tak sum thing?
Tsuntsu yakan fāɗa a tarko a ƙasa inda ba a sa tarko ba, ko tarko yakan zargu daga ƙasa in ba abin da ya taɓa shi?
6 Whether a trumpe schal sowne in a citee, and the puple schal not drede? Whether yuel schal be in a citee, which yuel the Lord schal not make?
Idan aka busa ƙaho a ciki birni mutane ba sa yin rawar jiki? Sa’ad da bala’i ya auko wa birni, ba Ubangiji ne ya sa a kawo shi ba?
7 For the Lord God schal not make a word, no but he schewe his priuyte to hise seruauntis profetis.
Ba shakka, Ubangiji Mai Iko Duka ba ya yin wani abu ba tare da ya sanar wa bayinsa annabawa ba.
8 A lioun schal rore, who schal not drede? the Lord God spak, who schal not profesie?
Zaki ya yi ruri, wa ba zai tsorata ba? Ubangiji Mai Iko Duka ya yi magana, wa ba zai yi annabci ba?
9 Make ye herd in the housis of Azotus, and in the housis of the lond of Egipt; and seie ye, Be ye gaderid togidere on the hillis of Samarye, and se ye many woodnessis in the myddis therof, and hem that suffren fals calenge in the priuy places therof.
Ku yi shela ga kagarun Ashdod da kuma ga kagarun Masar. “Ku tara kanku a tuddan Samariya; ku ga rashin jituwar da take a cikinta, da kuma zaluncin da ake yi a cikin mutanenta.”
10 And thei kouden not do riytful thing, seith the Lord, and tresouriden wickidnesse and raueyn in her housis.
“Ba su ma san yadda za su yi abin da yake daidai ba,” in ji Ubangiji, “sun ɓoye ganima da abubuwan da suka washe a cikin kagarunsu.”
11 Therfor the Lord God seith these thingis, The lond schal be troblid, and be cumpassid; and thi strengthe schal be drawun doun of thee, and thin housis schulen be rauyschid.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Abokin gāba zai ƙwace ƙasar, zai saukar da mafakarku, zai washe kagarunku.”
12 The Lord God seith these thingis, As if a schepherd rauyschith fro the mouth of a lioun tweyne hipis, ether the laste thing of the eere, so the children of Israel schulen be rauyschid, that dwellen in Samarie, in the cuntrei of bed, and in the bed of Damask.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci daga bakin zaki ƙasusuwa ƙafafu biyu kawai ko kunne ɗaya, haka za a ceci Isra’ilawa, masu zama a Samariya da kan gado kawai da kuma a ɗan ƙyalle a kan dogayen kujerunsu.”
13 Here ye, and witnesse ye in the hous of Jacob, seith the Lord God of oostis.
“Ku ji wannan ku kuma yi wa gidan Yaƙub gargaɗi,” in ji Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki.
14 For in the dai, whanne Y schal bigynne to visite the trespassyngis of Israel on hym, Y schal visite also on the auteris of Bethel; and the hornes of the auter schulen be kit awei, and schulen falle doun in to erthe.
“A ranar da zan hukunta Isra’ila saboda zunubanta, zan hallaka bagadan Betel; za a yayyanka ƙahonin bagadan za su fāɗa ƙasa
15 And Y schal smyte the wynter hous with the somer hous, and the housis of yuer schulen perische, and many housis schulen be distried, seith the Lord.
Zan rushe gidan rani da na damina; gidajen da aka yi musu ado da hauren giwa za a rushe su haka ma duk za a rurrushe manyan gidaje,” in ji Ubangiji.

< Amos 3 >