< Acts 1 >
1 Theofle, first `Y made a sermoun of alle thingis, that Jhesu bigan to do and to teche,
Littafin da na rubuta da farko, Tiyofilos, ya fadi abubuwan da Yesu ya fara yi ya kuma koyar,
2 in to the daie of his ascencioun, in which he comaundide bi the Hooli Goost to hise apostlis, whiche he hadde chosun;
har zuwa ranar da aka karbe shi zuwa sama. Wannan kuwa bayan da ya ba da umarni ga zababbun manzanninsa ta wurin Ruhu Mai Tsarki.
3 to whiche he schewide hym silf `alyue aftir his passioun, by many argumentis, apperinge to hem fourti daies, and spekinge of the rewme of God.
Bayan ya sha wahala, ya bayyana kan sa da rai a garesu, da alamu da dama masu gamsarwa. Kwana arba'in ya baiyana kansa a garesu yana yi masu magana game da mulkin Allah.
4 And he ete with hem, and comaundide, that thei schulden not departe fro Jerusalem, but abide the biheest of the fadir, which ye herden, he seide, bi my mouth;
Yayin da yana zaune tare da su ya basu umarni cewa kada su bar Urushalima, amma su jira alkawarin Uban, wanda ya ce, ''Kun ji daga gare ni,
5 for Joon baptiside in watir, but ye schulen be baptisid in the Hooli Goost, aftir these fewe daies.
cewa Yahaya babu shakka ya yi baftisma da ruwa, amma ku za a yi maku baftisma da Ruhu Mai Tsarki nan da kwanaki kadan.''
6 Therfor thei that weren come to gidere, axiden hym, and seiden, Lord, whether in this time thou schalt restore the kingdom of Israel?
Sa'adda suna tare suka tambaye shi, ''Ubangiji, a wannan lokaci ne za ka maido da mulki ga Isra'ila?”
7 And he seide to hem, It is not youre to knowe the tymes ether momentis, whiche the fadir hath put in his power;
Ya ce masu, ''Ba naku bane ku san lokaci ko sa'a wanda Uba ya shirya ta wurin ikonsa.
8 but ye schulen take the vertu of the Hooli Goost comynge fro aboue in to you, and ye schulen be my witnessis in Jerusalem, and in al Judee, and Samarie, and to the vtmeste of the erthe.
Amma za ku karbi iko, idan Ruhu Mai Tsarki ya zo bisanku, sa'annan za ku zama shaidu na cikin Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya da Samariya, har ya zuwa karshen duniya.”
9 And whanne he had seid these thingis, in her siyt he was lift vp, and a cloude resseyuede him fro her iyen.
Lokacin da Ubangiji Yesu ya fadi wadannan abubuwa, yayin da suna kallon sama, sai aka dauke shi zuwa sama, kuma girgije ya boye shi daga idanunsu.
10 And whanne thei biheelden hym goynge in to heuene, lo! `twei men stoden bisidis hem in white clothing, and seiden,
Da suka dinga kallon sama yayin da ya tafi, nan da nan, mazaje biyu suka tsaya a gabansu cikin fararen tufafi.
11 Men of Galile, what stonden ye biholdinge in to heuene? This Jhesu, which is takun vp `fro you in to heuene, schal come, as ye seyn hym goynge in to heuene.
Suka ce, ''Ku mazajen Galili me yasa ku ke tsaye a nan kuna kallon sama? Wannan Yesu wanda ya hau zuwa sama zai dawo kamar yadda kuka gan shi yana tafiya zuwa sama.''
12 Thanne thei turneden ayen to Jerusalem, fro the hille that is clepid `the hille of Olyuete, which is bisidis Jerusalem an halidaies iourney.
Da suka dawo Urushalima daga dutsen Zaitun, wanda ke kusa da Urushalima, tafiyar Asabaci daya ne.
13 And whanne thei weren entrid in to the hous, where thei dwelliden, thei wenten vp in to the soler, Petir and Joon, James and Andreu, Philip and Thomas, Bartholomew and Matheu, James of Alphei, and Symount Zelotes, and Judas of James.
Da suka iso, sai suka haye zuwa cikin bene inda suke da zama. Sune su Bitrus, Yahaya, Yakubu, Andarawus, Filibus, Toma, Bartalamawus, Matiyu, Yakubu dan Alfa, Siman mai tsattsauran ra'ayi, kuma da Yahuza dan Yakubu.
14 Alle these weren lastingli contynuynge with o wille in preier, with wymmen, and Marie, the moder of Jhesu, and with hise britheren.
Dukansu kuwa suka hada kai gaba daya, yayin da suka ci gaba da naciya cikin addu'a. Tare da su kuma akwai mata, Maryamu mahaifiyar Yesu, da kuma 'yan'uwansa.
15 In tho daies Petre roos vp in the myddil of the britheren, and seide; and ther was a company of men togidere, almest an hundrid and twenti;
A cikin wadannan kwanaki Bitrus ya tashi tsaye a tsakiyar 'yan'uwa, kimanin mutane dari da ashirin, ya ce,
16 Britheren, it bihoueth that the scripture be fillid, whiche the Hooly Goost bifore seide bi the mouth of Dauith, of Judas that was ledere of hem that token Jhesu;
'' 'Yan'uwa, akwai bukatar Nassi ya cika, wanda Ruhu Mai Tsarki ya fada a baya ta bakin Dauda game da Yahuza, wanda ya jagoranci wadanda suka kama Yesu
17 and was noumbrid among vs, and gat a part of this seruyce.
Domin yana daya daga cikinmu kuma ya karbi rabonsa na ladan wannan hidima,”
18 And this Judas hadde a feeld of the hire of wickidnesse, and he was hangid, and `to-brast the myddil, and alle hise entrailes weren sched abrood.
(Wannan mutum fa ya sai wa kansa fili da cinikin da ya yi na muguntarsa, kuma a nan ya fado da ka, cikinsa ya fashe, hanjinsa suka zubo waje.
19 And it was maad knowun to alle men that dwelten in Jerusalem, so that the ilke feeld was clepid Acheldemak in the langage of hem, that is, the feeld of blood.
Duka mazaunan Urushalima suka ji wannan, saboda haka suka kira wannan fili da harshensu “Akeldama'' wato, “Filin Jini.”)
20 And it is writun in the book of Salmes, The abitacioun of hem be maad desert, and be ther noon that dwelle in it, and an other take his bishopriche.
“Domin an rubuta a littafin Zabura, 'Bari filinsa ya zama kufai, kada a bar kowa ya zauna wurin,'kuma, 'Bari wani ya dauki matsayinsa na shugabanci.'
21 Therfor it bihoueth of these men, that ben gaderid togidere with vs in al the tyme, in which the Lord Jhesu entride, and wente out among vs,
Saboda haka ya zama dole, daya daga cikin wadanda suke tare da mu tun lokacin da Ubangiji Yesu yana shiga da fita, a tsakaninmu,
22 and bigan fro the baptym of Joon til in to the dai in which he was takun vp fro vs, that oon of these be maad a witnesse of his resurreccioun with vs.
farawa daga baftismar yahaya har zuwa ranar da aka dauke shi daga wurinmu zuwa sama, ya zama daya daga cikin mu wurin shaidar tashinsa.”
23 And thei ordeyneden tweyn, Joseph, that was clepid Barsabas, that was named Just, and Mathie.
Suka gabatar da mutum biyu, Yusufu wanda ake kira Barsabbas, wanda kuma aka yiwa suna Justus, da kuma Matayas.
24 And thei preieden, and seiden, Thou, Lord, that knowist the hertis of alle men, schewe whom thou hast chosun of these tweyne,
Su ka yi addu'a suka ce, ''Ubangiji, kai ka san zuciyar dukan mutane, ka bayyana mana wanda ka zaba cikin su biyun nan
25 that oon take the place of this seruyce and apostlehed, of which Judas trespasside, that he schulde go in to his place.
Domin ya dauki gurbin da kuma manzancin daga inda Yahuza ya kauce zuwa nashi waje''
26 And thei yauen lottis to hem, and the lot felde on Mathie; and he was noumbrid with enleuen apostlis.
suka jefa kuri'a a kansu; zabe ya fada kan Matayas kuma suka lissafta shi tare da manzanni sha dayan.