< Acts 25 >

1 Therfor whanne Festus cam in to the prouynce, aftir the thridde dai he wente vp to Jerusalem fro Cesarie.
Da Festas ya shiga lardin, kuma bayan kwana uku, ya tashi daga Kaisariya ya tafi Urushalima.
2 And the princis of prestis, and the worthieste of the Jewis wenten to hym ayens Poul, and preieden hym,
Sai babban firist da manyan Yahudawa suka kawo wa Festas sara a kan Bulus.
3 and axiden grace ayens hym, that he schulde comaunde hym to be led to Jerusalem; and thei settiden aspies to sle hym in the weie.
Suka roki tagomashi wurin Festas ya kira Bulus zuwa Urushalima domin su kashe shi a hanya.
4 But Festus answerde, that Poul schulde be kept in Cesarie; sotheli that he hym silf schulde procede more auisili. Therfor he seide, Thei that in you ben myyti,
Amma Festas ya amsa masu cewa, Bulus dan sarka ne a Kaisariya, kuma ba da dadewa ba shi da kansa zai koma can.
5 come doun togidere; and if ony crime is in the man, accuse thei hym.
“Saboda haka duk wadanda za su iya, su biyo mu. Idan akwai wani laifi game da mutumin, sai ku zarge shi.”
6 And he dwellede among hem no more than eiyte ether ten daies, and cam doun to Cesarie; and the tother dai he sat for domesman, and comaundide Poul to be brouyt.
Bayan kwana takwas ko goma, sai ya gangara zuwa Kaisariya. Washegari ya zauna bisa kursiyin shari'a ya bada umarni a kawo Bulus a gabansa.
7 And whanne he was brouyt forth, Jewis stoden aboute hym, whiche camen doun fro Jerusalem, puttynge ayens hym many and greuouse causis, whiche thei miyten not preue.
Da Bulus ya iso, Yahudawa daga Urushalima suka tsaya kusa, suka yi ta kawo kararraki, amma basu iya tabbatar da su ba.
8 For Poul yeldide resoun in alle thingis, That nether ayens the lawe of Jewis, nether ayens the temple, nether ayens the emperoure, Y synnede ony thing.
Bulus ya kare kansa ya ce, “Ban yi wa kowa laifi ba, ko Yahudawa, ko haikali, ko kuma Kaisar.”
9 But Festus wolde do grace to the Jewis, and answeride to Poul, and seide, Wolt thou gon vp to Jerusalem, and there be demyd of these thingis bifore me?
Amma Festas yana neman farin jini wajen Yahudawa, sabo da haka ya tambayi Bulus ya ce, “Kana so ka je Urushalima in shari'anta ka a can game da wadannan abubuwa?”
10 And Poul seide, At the domplace of the emperour Y stonde, where it bihoueth me to be demed. Y haue not noied the Jewis, as thou knowist wel.
Bulus ya ce, “Ina tsaye a Ddakalin Shari'ar Kaisar inda dole a shari'anta ni. Ban yi wa Yahudawa laifi ba, kamar yadda ka sani sosai.
11 For if Y haue noyed, ether don ony thing worthi deth, Y forsake not to die; but if no thing of tho is, that thei accusen me, no man may yyue me to hem. Y appele to the emperour.
Idan lallai na yi laifi kuma na yi abin da ya chanchanci mutuwa, ban ki ba in mutu. Amma idan zarginsu karya ne, kada kowa ya bashe ni gare su. Ina daukaka kara zuwa ga Kaisar.”
12 Thanne Festus spak with the counsel, and answerde, To the emperoure thou hast appelid, to the emperoure thou schalt go.
Bayan Festas ya tattauna da majalisa ya amsa ya ce, “Kana kira ga Kaisar; za ka tafi wurin Kaisar.”
13 And whanne summe daies weren passid, Agrippa kyng, and Beronyce camen doun to Cesarie, to welcome Festus.
Bayan wadansu kwanaki, sarki Agaribas da Barniki suka iso Kaisariya domin su ziyarci Festas.
14 And whanne thei dwelliden there many daies, Festus schewide to the king of Poul, and seide, A man is left boundun of Felix,
Da ya kasance kwanaki da yawa, Festas ya fada wa sarki labarin Bulus ya ce, “Akwai wani mutum dan sarka da Filikus ya bari a kurkuku.
15 of which, whanne Y was at Jerusalem, princis of preestis and the eldre men of Jewis camen to me, and axiden dampnacioun ayens hym.
Sa'anda nake a Urushalima, babban firist da dattawan Yahudawa suka kawo kararsa gare ni, suka roka a kashe shi.
16 To whiche Y answeride, That it is not custom to Romayns, to dampne ony man, bifore that he that is accusid haue hise accuseris present, and take place of defending, to putte awei the crymes, that ben putte ayens hym.
Game da wannan na amsa na ce masu, ba al'adar Romawa ba ce a ba da mutum tagomashi; sai wanda ake kararsa an bashi zarafi ya kare kansa a gaban masu kararsa, ya kuma bada hujjojinsa game da kararakin.
17 Therfor whanne thei camen togidere hidir, withouten ony delaye, in the dai suynge Y sat for domesman, and comaundide the man to be brouyt.
Saboda haka, da duk suka taru ban bata lokaci ba, washegari na zauna a kujerar shari'a, na ba da umarni a kawo mutumin.
18 And whanne hise accuseris stoden, thei seiden no cause, of whiche thingis Y hadde suspicioun of yuel.
Da masu karar suka fadi kararsu, sai na fahimci karar ba wani muhimmin abu a cikinta.
19 But thei hadden ayens hym summe questiouns of her veyn worschiping, and of oon Jhesu deed, whom Poul affermyde to lyue.
Sai dai na ga cewa jayayya ce tsakanin su ta addini a kan wani Yesu da ya mutu, wanda Bulus ya ce yana da rai.
20 And Y doutide of siche maner questioun, and seide, Whether he wolde go to Jerusalem, and ther be demyd of these thingis?
Na rasa yadda zan bincike wannan al'amarin, sai na tambaye shi ko zai je Urushalima a shari'anta shi kan wadannan abubuwa.
21 But for Poul appelide, that he schulde be kept to the knowing of the emperoure, Y comaundide him to be kept, til Y sende hym to the emperoure.
Amma da Bulus ya nemi a lura da shi, Kaisar ya shari'anta shi, sai na ba da umarni a ajiye shi har sai na aika shi wurin Kaisar.”
22 And Agrippa seide to Festus, Y my silf wolde here the man. And he seide, To morew thou schalt here hym.
Agaribas yace wa Festas. “Zan so ni ma in saurari mutumin nan.” “Gobe za ka ji shi,” in ji Fostus.
23 And on the tother day, whanne Agrippa and Beronyce camen with greet desire, and entriden in to the auditorie, with tribunes and the principal men of the citee, whanne Festus bad, Poul was brouyt.
Washegari Agaribas da Barniki suka zo tare da kasaitaccen taro suka shiga dakin taro tare da hafsoshi da shugabanin gari. Da Festas ya ba da umarni, aka fito da Bulus wurinsu.
24 And Festus seide, King Agrippa, and alle men that ben with vs, ye seen this man, of which al the multitude of Jewis preyede me at Jerusalem, and axide, and criede, that he schulde lyue no lenger.
Festas ya ce, “Sarki Agaribas da dukanku da kuke tare da mu a nan, kun ga mutumin nan, dukan Yahudawa sun gana da ni a Urushalima da nan kuma. Suna mani ihu cewa, bai chanchanta a bar shi da rai ba.
25 But Y foond, that he hadde don no thing worthi of deth; and Y deme to sende hym to the emperoure, for he appelide this thing.
Na gane bai yi wani abin da ya chanchanci mutuwa ba; amma saboda ya daukaka kara zuwa Kaisar, na yanke shawara in aika shi.
26 Of which man Y haue not certeyne, what thing Y schal write to the lord. For which thing Y brouyte hym to you, and moost to thee, thou king Agrippa, that whanne axing is maad, Y haue what Y schal write.
Amma ba ni da wani dalili na musamman da zan rubuta wasika ga Kaisar. Saboda wannan dalili na kawo shi gabanku, masamman kai ya sarki Agaribas. Domin in sami karin abin da zan rubuta game da shi.
27 For it is seyn to me with out resoun, to sende a boundun man, and not to signifie the cause of hym.
Gama a ganina wauta ce in aika dan sarka ba tare da na rubuta laifi a kansa ba.”

< Acts 25 >