< Acts 23 >
1 And Poul bihelde in to the counsel, and seide, Britheren, Y with al good conscience haue lyued bifore God, `til in to this dai.
Bulus ya zuba wa Majalisar ido ya ce, “’Yan’uwana, na cika aikina ga Allah cikin lamiri mai kyau har yă zuwa yau.”
2 And Anany, prince of prestis, comaundide to men that stoden nyy hym, that thei schulden smyte his mouth.
Da jin wannan Ananiyas babban firist ya umarci waɗanda suke tsaye kusa da Bulus su buge bakinsa.
3 Thanne Poul seide to hym, Thou whitid wal, God smyte thee; thou sittist, and demest me bi the lawe, and ayens the law thou comaundist me to be smytun.
Sai Bulus ya ce masa, “Allah zai buge ka, kai farin bango! Ka zauna a can kana hukunta ni bisa ga doka, ga shi kai kanka kana ƙetare dokar ta wurin ba da umarni a buge ni!”
4 And thei that stoden niy, seiden, Cursist thou the hiyest prest of God?
Waɗanda suke tsaye kusa da Bulus kuwa suka ce masa, “Babban firist na Allah za ka zaga?”
5 And Poul seide, Britheren, Y wiste not, that he is prince of preestis; for it is writun, Thou schalt not curse the prince of thi puple.
Bulus ya amsa ya ce, “’Yan’uwa, ai, ban san cewa shi ne babban firist ba; gama yana a rubuce cewa, ‘Kada ka yi mugun magana game da mai mulkin mutanenka.’”
6 But Poul wiste, that o parti was of Saduceis, and the othere of Fariseis; and he criede in the counsel, Britheren, Y am a Farisee, the sone of Farisees; Y am demyd of the hope and of the ayen rising of deed men.
Bulus, da ya gane cewa waɗansu daga cikinsu Sadukiyawa ne sauran kuma Farisiyawa ne, sai ya ɗaga murya a Majalisar ya ce, “’Yan’uwana, ni Bafarisiye ne, ɗan Farisiyawa. Ana mini shari’a saboda begen da nake da shi a kan tashin matattu.”
7 And whanne he hadde seid this thing, dissencioun was maad bitwixe the Fariseis and the Saduceis, and the multitude was departid.
Da ya faɗi haka, sai gardama ta tashi tsakanin Farisiyawa da Sadukiyawa, taron kuwa ya rabu biyu.
8 For Saduceis seien, that no `rysing ayen of deed men is, nether aungel, nether spirit; but Fariseis knowlechen euer eithir.
(Sadukiyawa suna cewa babu tashin matattu, babu mala’iku ko ruhohi. Amma Farisiyawa kuwa sun tsaya a kan cewa duk akwai.)
9 And a greet cry was maad. And summe of Farisees rosen vp, and fouyten, seiynge, We fynden no thing of yuel in this man; what if a spirit, ether an aungel spak to hym?
Aka yi babbar hayaniya. Waɗansu daga cikin malaman dokokin da suke Farisiyawa suka miƙe tsaye suka yi gardama mai ƙarfi suna cewa, “Ba mu sami wani laifi a wurin mutumin nan ba. A ce wani ruhu ko mala’ika ne ya yi masa magana fa?”
10 And whanne greet discencioun was maad, the tribune dredde, lest Poul schulde be to-drawun of hem; and he comaundide knyytis to go doun, and to take hym fro the myddil of hem, and to lede hym in to castels.
Gardamar kuwa ta yi tsanani har shugaban ƙungiyar sojan ya ji tsoro za su yayyage Bulus. Ya umarci sojoji su tafi su ƙwace shi ƙarfi da yaji daga wurinsu su kawo shi cikin barikin soja.
11 And in the niyt suynge the Lord stood niy to hym, and seide, Be thou stidfast; for as thou hast witnessid of me in Jerusalem, so it bihoueth thee to witnesse also at Rome.
Kashegari da dare Ubangiji ya tsaya kusa da Bulus ya ce, “Ka yi ƙarfin hali! Don kamar yadda ka yi shaida game da ni a Urushalima, haka kuma lalle, za ka yi shaidata a Roma.”
12 And whanne the dai was come, summe of the Jewis gaderiden hem, and maden `avow, and seiden, that thei schulden nether eete, ne drinke, til thei slowen Poul.
Kashegari, Yahudawa suka ƙulla makirci suka kuma yi rantsuwa cewa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe Bulus.
13 And there weren mo than fourti men, that maden this sweryng togider.
Fiye da mutane arba’in ne suka ƙulla wannan makirci.
14 And thei wenten to the princis of prestis, and eldre men, and seiden, With deuocioun we han a vowid, that we schulen not taste ony thing, til we sleen Poul.
Suka je wajen manyan firistoci da dattawa suka ce, “Mun yi babbar rantsuwa cewa ba za mu ci kome ba sai mun kashe Bulus.
15 Now therfor make ye knowun to the tribune, with the counsel, that he bringe hym forth to you, as if ye schulden knowe sum thing more certeynli of hym; and we ben redi to sle hym, bifor that he come.
Saboda haka, sai ku da Majalisa sai ku roƙi shugaban ƙungiyar sojan yă kawo shi a gabanku kamar kuna so ku ƙara samun cikakken bayani game da zancensa. Mu kuwa muna a shirye mu kashe shi kafin yă iso nan.”
16 And whanne the sone of Poulis sister hadde herd the aspies, he cam, and entride in to the castels, and telde to Poul.
Amma da ɗan’yar’uwar Bulus ya ji wannan makirci, sai ya tafi cikin barikin soja ya gaya wa Bulus.
17 And Poul clepide to hym oon of the centuriens, and seide, Lede this yonge man to the tribune, for he hath sum thing to schewe to hym.
Sai Bulus ya kira ɗaya daga cikin jarumawan ya ce, “Ka kai wannan saurayi wurin shugaban ƙungiyar soja; yana da wani abin da zai faɗa masa.”
18 And he took hym, and ledde to the tribune, and seide, Poul, that is boundun, preide me to lede to thee this yonge man, that hath sum thing to speke to thee.
Saboda haka ya ɗauke shi ya kai wajen shugaban ƙungiyar sojan. Jarumin ya ce, “Bulus, ɗan kurkukun nan ya kira ni, ya roƙe ni in kawo wannan saurayi a wurinka domin yana da wani abin da zai faɗa maka.”
19 And the tribune took his hoond, and wente with hym asidis half, and axide hym, What thing is it, that thou hast to schewe to me?
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya kama hannun saurayin ya ja shi gefe, ya tambaye shi cewa, “Mene ne kake so ka gaya mini?”
20 And he seide, The Jewis ben acordid to preye thee, that to morewe thou brynge forth Poul in to the counsel, as if thei schulden enquere sum thing more certeynli of hym.
Saurayin ya ce, “Yahudawa sun ƙulla za su roƙe ka ka kawo Bulus a gaban Majalisa gobe kamar suna neman ƙarin cikakken bayani game da Bulus.
21 But bileue thou not to hem; for mo than fourti men of hem aspien hym, which han a vowid, that thei schulen not eete nether drynke, til thei sleen hym; and now thei ben redi, abidinge thi biheest.
Kada ka yarda da su, domin fiye da mutum arba’in daga cikinsu suna fakonsa. Sun yi rantsuwa ba za su ci ko sha ba sai sun kashe shi. Suna nan a shirye yanzu, suna jira ka amince da roƙonsu.”
22 Therfor the tribune lefte the yonge man, and comaundide, that he schulde speke to no man, that he hadde maad these thingis knowun to hym.
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya sallami saurayin ya kwaɓe shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa cewa ka faɗa mini wannan.”
23 And he clepide togidre twei centuriens, and he seide to hem, Make ye redi twei hundrid knyytis, that thei go to Cesarie, and horse men seuenti, and spere men twey hundrid, fro the thridde our of the nyyt.
Sai ya kira biyu daga cikin jarumawansa, ya umarce su cewa, “Ku shirya sojoji ɗari biyu, da masu hawan dawakai saba’in da kuma masu māsu ɗari biyu su tafi Kaisariya da ƙarfe tara na daren nan.
24 And make ye redy an hors, for Poul to ride on, to lede hym saaf to Felix, the presydent.
Ku shirya wa Bulus dawakai da zai hau don a kai shi wurin Gwamna Felis lafiya.”
25 For the tribune dredde, lest the Jewis wolden take hym bi the weie, and sle hym, and aftirward he miyte be chalengid, as he hadde take money.
Ya kuma rubuta wasiƙa kamar haka,
26 And wroot hym `a pistle, conteynynge these thingis. Claudius Lisias to the beste Felix, president, heelthe.
Kalaudiyus Lisiyas. Zuwa ga Mai Girma, Gwamna Felis. Gaisuwa.
27 This man that was take of the Jewis, and bigan to be slayn, Y cam vpon hem with myn oost, and delyuerede hym fro hem, whanne Y knewe that he was a Romayn.
Yahudawa sun kama wannan mutum suna kuma dab da kashe shi, amma na zo da sojojina na ƙwato shi, saboda na ji shi ɗan ƙasar Roma ne.
28 And Y wolde wite the cause, which thei puttiden ayens hym; and Y ledde hym to the counsel of hem.
Na so in san abin da ya sa suke zarginsa, saboda haka na kawo shi a gaban Majalisarsu.
29 And Y foond, that he was accusid of questiouns of her lawe, but he hadde no cryme worthi the deth, ethir boondis.
Na tarar cewa zargin da ake masa ya shafi waɗansu abubuwan da suka shafi dokarsu ne, amma ba wani zargi a kansa da ya isa kisa ko a daure shi.
30 And whanne it was teeld me of the aspies, that thei arayden for hym, Y sente hym to thee, and Y warnede also the accuseris, that thei seie at thee. Fare wel.
Sa’ad da na sami labari cewa akwai wani makircin da aka ƙulla masa, sai na aika shi wurinka nan da nan. Na kuma umarci masu zarginsa su kai ƙararsu gare ka.
31 And so the knyytis, as thei weren comaundid, token Poul, and ledde hym bi nyyt into Antipatriden.
Saboda haka sojojin, don cika umarni, suka ɗauki Bulus da dad dare suka kawo shi har Antifatiris.
32 And in the dai suynge, whanne the horsmen weren left, that schulden go with hym, thei turneden ayen to the castels.
Kashegari suka bar masu hawan dawakai suka ci gaba da shi, yayinda sojojin suka koma barikin soja.
33 And whanne thei camen to Cesarie, thei token the pistle to the president, and thei setten also Poul byfore him.
Sa’ad da masu hawan dawakai suka isa Kaisariya, sai suka ba wa gwamna wasiƙar suka kuma miƙa masa Bulus.
34 And whanne he hadde red, and axide, of what prouynce he was, and knewe that he was of Cilicie,
Gwamna ya karanta wasiƙar ya kuma tambaya ko daga wanda lardi ne ya fito. Da ya ji cewa shi daga Silisiya ne,
35 Y schal here thee, he seide, whanne thin accuseris comen. And he comaundide hym to be kept in the moot halle of Eroude.
sai ya ce, “Zan ji batunka lokacin da masu zarginka suka iso.” Sa’an nan ya ba da umarni a kai Bulus a tsare shi a fadar Hiridus.