< Acts 17 >

1 And whanne thei hadden passid bi Amfipolis and Appollonye, thei camen to Thessolonyk, where was a synagoge of Jewis.
Da suka bi ta Amfifolis da Afolloniya, sai suka isa Tessalonika, inda akwai majami’ar Yahudawa.
2 And bi custom Poul entride to hem, and bi thre sabatis he declaride to hem of scripturis,
Kamar yadda ya saba, Bulus ya shiga majami’ar, ranakun Asabbaci uku ya yi ta yin muhawwara da su daga cikin Nassosi,
3 and openyde, and schewide that it bihofte Crist to suffre, and rise ayen fro deth, and that this is Jhesus Crist, whom Y telle to you.
yana musu bayani da tabbatarwa cewa dole Kiristi ya sha wahala ya kuma tashi daga matattu. Ya kuma ce, “Wannan Yesu da nake sanar muku shi ne Kiristi.”
4 And summe of hem bileueden, and weren ioyned to Poul and to Silas; and a greet multitude of hethene men worschipide God, and noble wymmen not a fewe.
Waɗansu Yahudawa suka amince suka kuma bi Bulus da Sila, haka ma Hellenawa da yawa masu tsoron Allah da kuma manyan mata ba kaɗan ba.
5 But the Jewis hadden enuye, and token of the comyn puple summe yuele men, and whanne thei hadden maad a cumpenye, thei moueden the citee. And thei camen to Jasouns hous, and souyten hem to brynge forth among the puple.
Amma Yahudawa suka yi kishi; saboda haka suka tattara’yan iska daga kasuwa, suka shirya wata ƙungiya, suka tā da tarzoma a birni. Suka ruga zuwa gidan Yason suna neman Bulus da Sila don su kawo su a gaban taron.
6 And whanne thei founden hem not, thei drowen Jasoun and summe britheren to the princis of the citee, and crieden, That these it ben, that mouen the world, and hidir thei camen,
Amma da ba su same su ba, sai suka ja Yason da waɗansu’yan’uwa zuwa gaban mahukuntan birnin, suna ihu suna cewa, “Waɗannan mutanen da suke tā da fitina ko’ina a duniya sun iso nan,
7 whiche Jason resseyuede. And these alle don ayens the maundementis of the emperour, and seien, that Jhesu is anothir king.
Yason kuwa ya karɓe su a gidansa. Dukansu suna karya dokokin Kaisar, suna cewa akwai wani sarki, wanda ake kira Yesu.”
8 And thei moueden the puple, and the princis of the citee, herynge these thingis.
Da suka ji haka, sai hankalin taron da na mahukuntan birnin ya tashi.
9 And whanne satisfaccioun was takun of Jason, and of othere, thei leten Poul and Silas go.
Sai suka sa Yason da sauran su biya kuɗin saki sa’an nan suka sallame su.
10 And anoon bi niyt britheren leten Silas go in to Beroan. And whanne thei camen thidur, thei entriden in to the synagoge of the Jewis.
Da dare ya yi, sai’yan’uwa suka sallami Bulus da Sila su tafi Bereya. Da suka isa can, sai suka shiga majami’ar Yahudawa.
11 But these weren the worthier of hem that ben at Thessolonik, whiche resseyueden the word with al desire, eche dai sekinge scripturis, if these thingis hadden hem so.
Bereyawa kuwa sun fi Tessalonikawa hankali, gama sun karɓi saƙon da marmari ƙwarai, suka kuma yi ta yin bincike Nassosi kowace rana su ga ko abin da Bulus ya faɗa gaskiya ne.
12 And manye of hem bileueden and of hethen wymmen onest and men not a fewe.
Yahudawa da yawa suka gaskata, haka ma waɗansu manyan matan Hellenawa da kuma mazan Hellenawa da yawa.
13 But whanne the Jewis in Tessalonyk hadden knowe, that also at Bero the word of God was prechid of Poul, thei camen thidir, mouynge and disturblynge the multitude.
Da Yahudawan da suke a Tessalonika suka ji cewa Bulus yana wa’azin maganar Allah a Bereya, sai suka je can ma, suna zuga taro suna kuma tā da hankalinsu.
14 And tho anoon britheren delyuerden Poul, that he schulde go to the see; but Sylas and Tymothe dwelten there.
Nan da nan’yan’uwa suka sa Bulus yă tafi bakin teku, amma Sila da Timoti suka dakata a Bereya.
15 And thei that ledden forth Poul, ledden hym to Atenes. And whanne thei hadden take maundement of him to Silas and to Tymothe, that ful hiyyngli thei schulden come to hym, thei wenten forth.
Mutanen da suka raka Bulus kuwa suka kawo shi Atens sa’an nan suka dawo da umarnai wa Sila da Timoti cewa su zo wurinsa da gaggawa.
16 And while Poul abood hem at Atenys, his spirit was moued in him, for he saiy the citee youun to ydolatrie.
Yayinda Bulus yake jiransu a Atens, ya damu ƙwarai da ya ga birnin cike da gumaka.
17 Therfor he disputide in the synagoge with the Jewis, and with men that worschipiden God, and in the dom place, by alle daies to hem that herden.
Saboda haka ya yi ta muhawwara a majami’a da Yahudawa da kuma Hellenawa masu tsoron Allah, haka kuma da waɗanda yake tararwa a bakin kasuwa.
18 And summe Epeicureis, and Stoisens, and filosofris disputiden with hym. And summe seiden, What wole this sowere of wordis seie? And othere seiden, He semeth to be a tellere of newe fendis; for he telde to hem Jhesu, and the ayenrisyng.
Wata ƙungiyar Afikuriya da kuma masu bin ussan ilimin Sitoyik suka fara gardama da shi. Waɗansunsu suka ce, “Mene ne mai surutun nan yake ƙoƙarin faɗi?” Waɗansu suka ce, “Kamar yana wa’azin baƙin alloli ne.” Sun faɗa haka ne domin Bulus yana wa’azin labari mai daɗi game da Yesu da kuma tashin matattu.
19 And thei token, and ledden hym to Ariopage, and seide, Moun we wite, what is this newe doctryne, that is seid of thee?
Sai suka ɗauke shi suka kawo shi wurin taron Areyofagus, inda suka ce masa, “Ko za mu san mene ne sabon koyarwan nan ya ƙunsa da kake yi?
20 For thou bringist ynne summe newe thingis to oure eeris; therfor we wolen wite, what these thingis wolen be.
Kana kawo mana ra’ayoyin da suke baƙo a gare mu, kuma muna so mu san mene ne suke nufi.”
21 For alle men of Athenys and comlingis herborid yauen tent to noon other thing, but ether to seie, ethir to here, sum newe thing.
(Duk Atenawa da baƙin da suke zama a can suna zaman kashe wando ne kawai kuma ba abin da suke yi sai dai taɗi da kuma jin sababbin ra’ayoyi.)
22 And Poul stood in the myddil of Ariopage, and seide, Men of Athenys, bi alle thingis Y se you as veyn worschipers.
Sai Bulus ya miƙe tsaye a tsakiyar taron Areyofagus ya ce, “Ya ku mutanen Atens! Na dai lura cewa ta kowace hanya ku masu addini ne ƙwarai.
23 For Y passide, and siy youre maumetis, and foond an auter, in which was writun, To the vnknowun God. Therfor which thing ye vnknowynge worschipen, this thing Y schew to you.
Gama sa’ad da nake zagawa, na lura da kyau da abubuwan da kuke bauta wa, har ma na tarar da wani bagade da wannan rubutu, Ga Allahn da ba a sani ba. To, abin nan da kuke yi wa sujada a matsayin abin da ba ku sani nan ba shi ne zan sanar da ku.
24 God that made the world and alle thingis that ben in it, this, for he is Lord of heuene and of erthe, dwellith not in templis maad with hoond,
“Allahn da ya halicci duniya da kome da yake cikinta shi ne Ubangijin sama da ƙasa, ba ya kuma zama a haikalin da aka gina da hannuwa.
25 nethir is worschipid bi mannus hoondis, nether hath nede of ony thing, for he yyueth lijf to alle men, and brethinge, and alle thingis;
Ba a kuma yin masa hidima da hannun mutum, sai ka ce mai bukatan wani abu, domin shi kansa ne ke ba wa dukan mutane rai da numfashi da kuma kome.
26 and made of oon al the kinde of men to enhabite on al the face of the erthe, determynynge tymes ordeyned, and termes of the dwellynge of hem,
Daga mutum ɗaya, ya halicci kowace al’ummar mutane, don su zauna a duk duniya; shi ne kuma ya ƙaddara lokuta bisa ga tsarinsu da kuma inda za su kasance.
27 to seke God, if perauenture thei felen hym, ether fynden, thouy he be not fer fro eche of you.
Allah ya yi wannan domin mutane su neme shi mai yiwuwa kuma su lalluba su same shi, ko da yake ba shi da nisa daga kowannenmu.
28 For in hym we lyuen, and mouen, and ben. As also summe of youre poetis seiden, And we ben also the kynde of hym.
‘Gama a cikinsa ne muke rayuwa muke motsi muka kuma kasance.’ Yadda waɗansu mawaƙanku suka ce, ‘Mu zuriyarsa ce.’
29 Therfor sithen we ben the kynde of God, we schulen not deme, that godli thing is lijk gold, and siluer, ethir stoon, ethir to grauyng of craft and thouyt of man.
“Saboda haka da yake mu zuriyar Allah ce, kada mu yi tsammani cewa kamannin Allah yana kama da zinariya ko azurfa ko dutse, siffar da mutum ya ƙago ta wurin dabararsa.
30 For God dispisith the tymes of this vnkunnyng, and now schewith to men, that alle euery where doon penaunce; for that he hath ordeyned a dai,
A dā Allah ya kawar da Allah ya kawar da kai ga zamanin jahilci, amma yanzu ya umarci dukan mutane a ko’ina su tuba.
31 in which he schal deme the world in equite, in a man in which he ordeynede, and yaf feith to alle men, and reiside hym fro deth.
Gama ya sa ranar da zai yi wa duniya shari’a da adalci ta wurin mutumin da ya naɗa. Ya riga ya ba da tabbacin wannan ga dukan mutane ta wurin tā da shi daga matattu.”
32 And whanne thei hadden herd the ayenrysing of deed men, summe scorneden, and summe seiden, We schulen here thee eft of this thing.
Sa’ad da suka ji maganar tashin matattu, waɗansunsu suka yi tsaki, amma waɗansu suka ce, “Muna so mu ƙara jin ka a kan wannan batu.”
33 So Poul wente out of the myddil of hem.
Da wannan, Bulus ya bar Majalisar.
34 But summen drowen to hym, and bileueden. Among whiche Dynyse Aropagite was, and a womman, bi name Damaris, and othere men with hem.
Waɗansu mutane kima suka zama mabiyan Bulus suka kuwa gaskata. A cikinsu kuwa akwai Diyonasiyus ɗan Majalisar Areyofagus, haka kuma wata mace mai suna Damaris, da waɗansu dai haka.

< Acts 17 >