< 2 Samuel 8 >

1 Forsothe it was doon aftir these thingis, Dauid smoot Filisteis, and made low hem; and Dauid took awei the bridil of tribute fro the hond of Filisteis.
Ana nan, sai Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya kawo ƙarshen mulkinsu a ƙasar, ya kuma ƙwace ƙasar Meteg Amma daga hannun Filistiyawa.
2 And Dauid smoot Moab, and mat hem with a coorde, and made euene to the erthe; forsothe `he mat twey cordis, oon to sle, and oon to quikene. And Moab seruyde Dauid vndur tribute.
Haka kuma Dawuda ya ci Mowabawa. Ya sa suka kwanta a ƙasa, ya kuma auna su da igiya. Kowane awo biyu ya sa a kashe su, amma awo na uku sai yă sa a bar su da rai. Saboda haka Mowabawa suka zama bayin Dawuda, suka kuma kawo masa haraji.
3 And Dauid smoot Adadezer, sone of Roob, kyng of Soba, whanne he yede forth to be lord ouer the flood Eufrates.
Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba. Wannan ya faru a lokacin da Hadadezer yake kan hanyarsa zuwa Kogin Yuferites don yă sāke mai da wurin a ƙarƙashin ikonsa.
4 And whanne a thousynde and seuene hundrid kniytis of his part weren takun, and twenti thousynde of foot men, Dauid hoxide alle `drawynge beestis in charis; but Dauid lefte of tho an hundrid charis, that is, the horsis of an hundrid charis.
Dawuda ya kame keken yaƙinsa guda dubu, mahayan keken yaƙinsa dubu bakwai, da sojojin ƙasa dubu ashirin. Ya yayyanke agaran dawakan duka amma ya bar dawakai kekunan yaƙi ɗari.
5 Also Sirie of Damask cam, that it schulde bere help to Adadezer, kyng of Soba; and Dauid smoot of Sirie two and twenti thousynde of men.
Sa’ad da Arameyawan Damaskus suka zo don su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya karkashe dubu ashirin da biyunsu.
6 And Dauid settide strengthe in Sirie of Damask, and Sirie was maad seruynge Dauid vndur tribute. And the Lord kepte Dauid in alle thingis, to what euer thingis he yede forth.
Ya ajiye ƙungiyoyi sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus, Arameyawa kuwa suka zama bayinsa, suka biya shi haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
7 And Dauid took goldun armeris and bies, whiche the seruauntis of Adadezer hadden, and he brouyte tho in to Jerusalem.
Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariya na shugabannin sojojin Hadadezer ya kawo Urushalima.
8 And of Bethe, and of Beroth, citees of Adadezer, Dauith the kyng took ful myche metal; `of the whiche Salomon made alle the brasen vessels in the temple, and the brasen see, and the pilers, and the auter.
Daga Teba da Berotai, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Sarki Dawuda ya kwashe tagulla masu yawan gaske.
9 Forsothe Thou, kyng of Emath, herde that Dauid hadde smyte al the strengthe of Adadezer.
Da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci dukan rundunar Hadadezer,
10 And Thou sente Joram, his sone, to `kyng Dauid, that he schulde grete hym, and thanke, and do thankyngis, for he hadde ouercome Adadezer, and hadde smyte hym; for Thou was enemy to Adadeser; and vessels of silver, and vessels of gold, and vessels of bras weren in his hond.
sai ya aiki ɗansa Yoram wurin Sarki Dawuda yă gaishe, yă kuma yi masa barka saboda nasarar da ya yi a kan Hadadezer, gama Hadadezer nan ya hana Towu sakewa. Yoram ya tafi ɗauke da kayan azurfa, da na zinariya, da na tagulla.
11 And the same vessels kyng Dauid halewid `to the Lord, with the siluer and gold, whiche he hadde halewid of alle hethene men, whiche `hethene men he made suget of Sirye,
Sarki Dawuda kuwa ya keɓe waɗannan kayayyaki wa Ubangiji, yadda ya yi da zinariya, da kuma azurfa daga dukan al’umman da ya mallaka,
12 and Moab, and the sones of Amon, and Filisteis, and Amalech, and of the spuylis of Adadezer, sone of Roob, kyng of Soba.
wato, azurfa da zinariyan mutanen Edom, da na Mowabawa, da na Ammonawa, da na Filistiyawa, da na Amalekawa, da ganimar Hadadezer ɗan Rehob, sarkin Zoba.
13 Also Dauid made to hym a name, whanne he turnede ayen, whanne Sirie was takun, for eiytene thousynde weren slayn in the valey, where salt is maad, and in Gebelem, to thre and twenti thousynde.
Dawuda kuwa ya ƙara zama shahararre bayan ya dawo daga kai wa ƙasar Aram hari, daga nan sai ya je ya karkashe mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
14 And he settide keperis in Ydumee, and ordeinede strong hold, and al Ydumee was maad seruynge to Dauid; and the Lord kepte Dauid in alle thingis, to whateuer thingis he yede forth.
Ya ajiye rundunar sojoji ko’ina a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba wa Dawuda nasara a duk inda ya tafi.
15 And Dauid regnede on al Israel, and Dauid dide doom, and riytfulnesse to al his puple.
Dawuda ya yi mulkin dukan ƙasar Isra’ila, yana yin wa dukan jama’arsa shari’ar gaskiya da adalci.
16 Forsothe Joab, the sone of Saruy, was ouer the oost; sotheli Josaphat, sone of Achilud, was chaunceler; and Sadoch,
Yowab ɗan Zeruhiya ya zama shugaban sojoji; Yehoshafat ɗan Ahilud kuwa shi ne marubucin tarihi;
17 sone of Achitob, and Achymelech, sone of Abiathar, weren preestis; and Saraye was scryuyn.
Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyatar, su ne firistoci; Serahiya kuma sakatare;
18 Forsothe Bananye, sone of Joiada, was ouer Cerethi and Pherethi, that is, ouer archeris and arblasteris; sotheli the sones of Dauid weren prestis.
Benahiya ɗan Yehohiyada ne shugaban Keretawa da Feletiyawa, wato, sojoji masu gadin Dawuda, sa’an nan’ya’yan Dawuda maza su ne mashawartan sarki.

< 2 Samuel 8 >