< 2 Samuel 6 >

1 Forsothe Dauid gaderide eft alle the chosun men of Israel, thritti thousynde.
Dawuda ya sāke tattara zaɓaɓɓun mutanen Isra’ila, dubu talatin.
2 And Dauid roos, and yede, and al the puple that was with hym of the men of Juda, to brynge the arke of God, on which the name of the Lord of oostis, sittynge in cherubyn on that arke, was clepid.
Shi, da dukan mutanensa suka tashi daga Ba’ala-Yahuda don su hauro da akwatin alkawarin Allah, wanda ake kira da SunanUbangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a tsakanin kerubobin da suke a kan akwatin alkawarin.
3 And thei puttiden the arke of God on a newe wayn, and thei token it fro the hows of Amynadab, that was in Gabaa. Forsothe Oza and Haio, the sons of Amynadab, dryueden the newe wayn.
Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah a sabuwar keken yaƙi, suka kawo shi daga gidan Abinadab, wanda yake bisa tudu. Uzza da Ahiyo,’ya’yan Abinadab maza, suka bi da keken yaƙin da akwatin alkawarin Allah yake ciki suka bi da keken yaƙin
4 And whanne thei hadden take it fro the hows of Amynadab, that was in Gabaa, and kepte the arke of God, Haio yede bifor the arke.
da akwatin alkawarin Allah yake ciki. Ahiyo kuwa yana tafiya a gaban Abinadab.
5 Forsothe Dauid and al Israel pleieden byfor the Lord, in alle `trees maad craftili, and harpis, and sitols, and tympans, and trumpis, and cymbalis.
Dawuda da dukan gidan Isra’ila suka yi biki sosai da dukan ƙarfinsu a gaban Ubangiji, da waƙoƙi, da molaye, da garayu, da ganguna, da kacau-kacau da kuma kuge.
6 Forsothe after that thei camen to the corn floor of Nachor, Oza helde forth the hond to the arke of God, and helde it, for the oxun kikiden, and bowiden it.
Da suka kai masussukar Nakon, sai Uzza ya miƙa hannu don yă riƙe akwatin alkawarin Allah, gama shanun sun yi tuntuɓe.
7 And the Lord was wrooth bi indignacioun ayens Oza, and smoot hym on `the foli; and he was deed there bisidis the arke of God.
Fushin Ubangiji kuwa ya ƙuna a kan Uzza domin aikin rashin bangirma, saboda haka Allah ya buge shi ya kuma mutu a can kusa da akwatin alkawarin Allah.
8 Forsothe Dauid was sori, for the Lord hadde smyte Oza; and the name of that place was clepid the Smytyng of Oza `til in to this dai.
Ran Dawuda ya ɓace gama fushin Ubangiji ya ɓarke a kan Uzza. Shi ya sa har wa yau ana kira wurin Ferez Uzza.
9 And Dauid dredde the Lord in that dai, and seide, Hou schal the arke of the Lord entre to me?
Dawuda ya ji tsoron Ubangiji a ranar, sai ya ce, “Yaya akwatin alkawarin Ubangiji zai iya zuwa wurina?”
10 And he nolde turne the arke of the Lord to hym silf in to the citee of Dauid, but he turnede it in to the hows of Obethedom of Geth.
Bai so yă ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji yă kasance tare da shi a Birnin Dawuda ba. A maimakon haka sai ya kai shi gidan Obed-Edom mutumin Gat.
11 And the arke of the Lord dwellide in the hows of Obethedom of Geth thre monethis; and the Lord blessid Obethedom, and al his hows.
Akwatin Alkawarin Ubangiji ya kasance a gidan Obed-Edom mutumin Gat har tsawon wata uku, Ubangiji kuwa ya albarkace shi da dukan iyalinsa.
12 And it was teld to kyng Dauid, that the Lord hadde blessid Obethedom, and alle `thingis of hym, for the arke of God. And Dauid seide, Y schal go, and brynge the arke with blessyng in to myn hows. Therfor Dauid yede, and brouyte the arke of God fro the hows of Obethedom in to the citee of Dauid with ioye; and ther weren with Dauid seuen cumpanyes, and the slain sacrifice of a calff.
To, sai aka faɗa wa Sarki Dawuda cewa, “Ubangiji ya sa wa gidan Obed-Edom albarka da dukan abin da yake da shi, saboda akwatin alkawarin Allah.” Saboda haka sai Dawuda ya gangara ya hauro da akwatin alkawarin Allah daga gidan Obed-Edom zuwa Birnin Dawuda da farin ciki.
13 And whanne thei, that baren the arke of the Lord, hadden stied six paaces, thei offriden an oxe and a ram. And Dauid smoot in organs boundun to the arm;
Sa’ad da waɗanda suke ɗaukan akwatin alkawarin Ubangiji suka yi tafiya taki shida, sai yă yi hadayar bijimi da saniya mai ƙiba.
14 and daunside with alle strengthis bifor the Lord; sotheli Dauid was clothid with a lynnun surplis.
Dawuda, sanye da efod lilin, ya yi ta rawa a gaban Ubangiji da dukan ƙarfinsa,
15 And Dauid, and al the hows of Israel, ledden forth the arke of testament of the Lord in hertli song, and in sown of trumpe.
yayinda shi da dukan gidan Isra’ila suka hauro da akwatin alkawarin Ubangiji da sowa da kuma busar ƙahoni.
16 And whanne the arke of the Lord hadde entride in to the citee of Dauid, Mychol, the douytir of Saul, bihelde bi a wyndow, and sche siy the kyng skippynge and daunsynge bifor the Lord; and sche dispiside hym in hir herte.
Sa’ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga Birnin Dawuda, sai Mikal’yar Shawulu ta leƙa ta taga ta ga Dawuda sarki yana tsalle, yana rawa a gaban Ubangiji, sai ta rena shi a zuciyarta.
17 And thei brouyten in the arke of the Lord, and settiden it in his place, in the myddis of tabernacle, which tabernacle Dauid hadde maad `redy therto; and Dauid offride brent sacrifices and pesible bifor the Lord.
Suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, aka ajiye shi a inda aka shirya masa a cikin tentin da Dawuda ya shirya dominsa. Dawuda kuma ya miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama a gaban Ubangiji.
18 And whanne Dauid hadde endid tho, and hadde offrid brent sacrifices and pesible, he blesside the puple in the name of the Lord of oostis.
Bayan ya gama yin hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki.
19 And he yaf to al the multitude of Israel, as wel to man as to womman, to ech `o thinne loof, and o part rostid of bugle fleisch, and flour of wheete fried with oile; and al the puple yede, ech man in to his hows.
Sa’an nan ya rarraba abinci, da ƙosai, dabino, da waina ga kowane mutum a cikin dukan jama’ar Isra’ila, maza da mata. Dukan mutane kuwa suka watse zuwa gidajensu.
20 And Dauid turnede ayen to blesse his hows, and Mychol, the douytir of Saul, yede out in to the comyng of Dauid, and seide, Hou glorious was the kyng of Israel to day vnhilynge hym silf bifor the handmaidis of hise seruauntis, and he was maad nakid, as if oon of the harlotis be maad nakid?
Da Dawuda ya koma gida don yă sa wa gidansa albarka, sai Mikal’yar Shawulu ta fito don tă tarye shi, sai ta ce, “Tabbas sarkin Isra’ila ya fiffita kansa yau, ya tuɓe a gaban bayinsa’yan mata, kamar yadda duk marar kunya yakan yi!”
21 And Dauid seide to Mychol, The Lord lyueth, for Y schal pley bifor the Lord, that chees me rathere than thi fadir, and than al the hows of hym, and comaundide to me, that Y schulde be duyk on the puple `of the Lord of Israel;
Dawuda ya ce wa Mikal, “Na yi rawana domin in girmama Ubangiji ne, wanda ya zaɓe ni a maimakon mahaifinki ko wani daga cikin dukan gidansa, shi ne kuma ya sa ni sarki a kan Isra’ila, mutanen Ubangiji, zan yi biki a gaban Ubangiji.
22 and Y schal pleie, and Y schal be maad `vilere more than Y am maad, and Y schal be meke in myn iyen, and Y schal appere gloriousere with the handmaydys, of whiche thou spakist.
Zan ma mai da kaina abin reni fiye da haka, za a kuma zama abin reni a gare ki. Amma waɗannan bayi’yan matan da kika yi magana a kai, za su gan ni da martaba.”
23 Therfor a sone was not borun to Mychol, the douytir of Saul, til in to the dai of hir deeth.
Mikal’yar Shawulu kuwa ba tă haifi ɗa ba har mutuwarta.

< 2 Samuel 6 >