< 2 Samuel 21 >

1 Also hungur was maad in the lond of Israel in the daies of Dauid, bi thre yeer contynueli. And Dauid counselide the answere of the Lord; and the Lord seide, For Saul, and his hows, and blood, for he killide men of Gabaon.
Lokacin da Dawuda yake mulki, an yi yunwa shekara uku a jere; saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji. Ubangiji ya ce, “Saboda Shawulu ne da alhakin jinin gidansa; domin ya kashe Gibeyonawa.”
2 Therfor whanne Gabaonytis weren clepid, the kyng seide to hem; sotheli Gabaonytis ben not of the sones of Israel, but thei ben the relikys of Ammorreis; and the sones of Israel hadden swore to hem, `that is, that thei schulden not `be slayn, and Saul wolde smyte hem for feruent loue, as for the sones of Israel and of Juda;
Sai sarki ya tattara Gibeyonawa ya yi musu magana. (To, Gibeyonawa ba sashen Isra’ilawa ba ne, amma mutanen Amoriyawa ne da suka ragu, waɗanda Isra’ila ta rantse za tă bari da rai, amma Shawulu cikin kishinsa don Isra’ila da Yahuda ya yi ƙoƙari yă hallaka su duka.)
3 therfor Dauid seide to Gabaonytis, What schal Y do to you, and what schal be youre amendis, that ye blesse the eritage of the Lord?
Dawuda ya ce wa Gibeyonawa, “Me zan yi muku? Yaya zan yi kafara domin ku sa wa masu gādon Ubangiji albarka?”
4 And Gabaonytis seiden to hym, No questioun is to vs on gold and siluer, but ayens Saul, and ayens his hows; nether we wolen, that a man of Israel be slayn. To whiche the kyng seide, What therfor wolen ye, that Y do to you?
Gibeyonawa suka ce, “Ba mu da’yanci mu nemi zinariya ko azurfa daga wurin Shawulu ko gidansa, ba mu kuwa da wani’yanci mu sa a kashe wani a Isra’ila.” Dawuda ya ce, “To, me kuke so in yi muku?”
5 Whiche seiden to the king, We owen to do awei so the man, that `al to brak ethir defoulide vs, and oppresside wickidli, that not oon sotheli be residue of his generacioun in alle the coostis of Israel.
Suka ce wa sarki, “Mutumin da ya hallaka mu ya kuma yi mana makirci don kada mu kasance tare da Isra’ilawa ko’ina a cikin ƙauyukansu,
6 Seuene men of hise sones be youun to vs, that we `crucifie hem to the Lord in Gabaa of Saul, sum tyme the chosun man of the Lord. And the kyng seide, Y schal yyue.
a ba mu zuriyarsa maza bakwai, mu kashe su, mu kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji a Gibeya na Shawulu wannan zaɓaɓɓen Ubangiji.” Sai sarki ya ce, “Zan ba ku su.”
7 And the kyng sparide Myphibosech, sone of Jonathas, sone of Saul, for the ooth of the Lord, that was bitwixe Dauid and bitwixe Jonathas, sone of Saul.
Sarki ya ware Mefiboshet ɗan Yonatan jikan Shawulu, saboda rantsuwar da take tsakanin Dawuda da Yonatan, ɗan Shawulu a gaban Ubangiji.
8 Therfor the kyng took twei sones of Respha, douyter of Ahira, whiche sche childide to Saul, Armony, and Mysphibosech; and he took fyue sones of Mychol, douyter of Saul, whiche sche gendride to Adriel, sone of Berzellai, that was of Molaty.
Amma sarki ya ɗauki Armoni da Mefiboshet,’ya’ya biyu maza waɗanda Rizfa’yar Aiya ta haifa wa Shawulu, tare da’ya’ya maza biyar na Merab’yar Shawulu, waɗanda ta haifa wa Adriyel ɗan Barzillai, mutumin Mehola.
9 And he yaf hem in to the hondis of Gabaonytis, whiche crucifieden tho sones in the hil bifor the Lord; and these seuene felden slayn togidere in the daies of the firste rep, whanne the repyng of barli bigan.
Ya ba da su ga Gibeyonawa, waɗanda suka kashe su, suka kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji. Dukan bakwai ɗin an kashe su gaba ɗaya; an kashe su a farkon kwanankin girbi, daidai lokacin fara girbin sha’ir.
10 Forsothe Respha, douytir of Ahia, took an heire, and `araiede to hir silf a place aboue the stoon, fro the bigynnyng of heruest til watir droppide `on hem fro heuene; and sche suffride not briddis to tere hem bi dai, nether beestis bi nyyt.
Rizfa’yar Aiya ta ɗauki tsumma ta yi wa kanta shimfiɗa a kan dutse. Tun daga farkon girbi har ruwa damina ya sauko a kan gawawwakin, ba tă yarda tsuntsayen sama su taɓa su da rana ko mugayen namun jeji da dare ba.
11 And tho thingis whiche Respha, secoundarie wijf of Saul, douytir of Ahia, hadde do, weren teld to Dauid.
Da aka gaya wa Dawuda abin da Rizfa’yar Aiya ƙwarƙwaran Shawulu ta yi,
12 And Dauid yede, and took the boonys of Saul, and the boonys of Jonathas, his sone, of the men of Jabes of Galaad; that hadden stole tho boonys fro the street of Bethsan, in which street the Filisteis hadden hangid hem, whanne thei hadden slayn Saul in Gelboe.
sai ya je ya kwashe ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga mutanen Yabesh Gileyad (Gama mutanen sun saci gawawwakin Shawulu da Yonatan daga inda Filistiyawa suka kakkafa su a kan itace a filin Bet-Shan, bayan da Filistiyawa suka kashe su a Gilbowa.)
13 And Dauid bar out fro thennus the boonys of Saul, and the boonys of Jonathas, his sone; and thei gaderiden the boonys of hem that weren crucified, and birieden tho with the boonys of Saul and of Jonathas, his sone, in the lond of Beniamyn, in the side of the sepulcre of Cys, fadir of Saul.
Dawuda ya kawo ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga can, a kuma aka tattara dukan ƙasusuwan waɗanda Gibeyonawan suka kashe, suka kuma rataye.
14 And thei diden al thingis, what euer thingis the kyng comaundide; and the Lord dide mercy to the lond aftir these thingis.
Suka binne ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan a kabarin Kish, mahaifin Shawulu, a Zela a Benyamin. Suka kuma yi kome da sarki ya umarta. Bayan wannan Allah ya ji addu’arsu a madadin ƙasar.
15 Forsothe batel of Filisteis was maad eft ayens Israel; and Dauid yede doun, and hise seruauntis with hym, and fouyten ayen Filisteis.
Har yanzu yaƙi ya sāke ɓarke tsakanin Filistiyawa da Isra’ila. Sai Dawuda ya gangara tare da mutanensa don su yaƙi Filistiyawa, gajiya ta kama shi.
16 Sotheli whanne Dauid failide, Jesbydenob, that was of the kyn of Arapha, that is, of giauntis, and the yrun of his spere peiside thre hundrid ouncis, and he was gird with a newe swerd, enforside to smyte Dauid.
Ishbi-Benob kuwa, wani daga zuriyar Rafa, wanda nauyin kan māshinsa na tagulla ya yi shekel ɗari uku, wanda yake kuma da sabon māshi, ya ce zai kashe Dawuda.
17 And Abisai, sone of Saruye, was in help to Dauid; and he smoot and killide the Filistei. Than the men of Dauid sworen, and seiden, Now thou schalt not go out with vs in to batel, lest thou quenche the lanterne of Israel.
Amma Abishai ɗan Zeruhiya ya kawo wa Dawuda gudummawa; ya bugi Bafilistin, ya kashe shi. Sa’an nan mutanen Dawuda suka rantse masa suka ce, “Ba za ka ƙara fita tare da mu wurin yaƙi ba, don kada fitilar Isra’ila tă mutu.”
18 Also the secounde batel was in Gob ayens Filisteis; thanne Sobothai of Osothai smoot Zephi, of the generacioun of Arapha, of the kyn of giauntis.
Ana nan, sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa, a Gob. A lokacin Sibbekai mutumin Husha ya kashe Saf, wani daga zuriyar Rafa.
19 Also the thridde batel was in Gob ayens Filisteis; in which batel a man youun of God, the sone of forest, a broiderer, a man of Bethleem, smoot Golyath of Geth, whos `schaft of spere was as a beem of webbis.
Sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Ya’are-Oregim mutumin Betlehem ya kashe Goliyat mutumin Gat, wanda girmar sandan māshinsa ta yi kama da taɓarya.
20 The fourthe batel was in Geth; where ynne was an hiy man, that hadde sixe fyngris in the hondis and feet, that is, foure and twenti; and he was of the kyn of Arapha;
Har wa yau a wani yaƙin da aka yi a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu, da kuma yatsotsi shida a kowane ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriya Rafa ne.
21 and he blasfemyde Israel; sotheli Jonathan, sone of Samaa, brother of Dauid, killide hym.
Da ya yi wa Isra’ila reni, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwa Dawuda, ya kashe shi.
22 These foure weren borun of Arapha in Geth, and thei felden doun in the hond of Dauid, and of hise seruauntis.
Waɗannan huɗu zuriyar Rafa ne a Gat, suka kuwa mutu ta hannu Dawuda da mutanensa.

< 2 Samuel 21 >