< 2 Samuel 20 >
1 Also it bifelde, that a man of Belial was there, Siba bi name, the sone of Bothri, a man of the generacioun of Gemyny; and he sownede with a clarioun, and seide, No part is to vs in Dauid, nether eritage in the sone of Ysai; thou, Israel, turne ayen in to thi tabernaclis.
Akwai wani mai tā-da-na-zaune-tsaye, sunansa Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Benyamin, a wurin. Sai ya busa ƙaho, ya yi ihu ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu da sashe a wurin ɗan Yesse! Kowa yă nufi tentinsa, ya Isra’ila!”
2 And al Israel was departid fro Dauid, and suede Siba, the sone of Bothri; forsothe the men of Juda cleuyden to her kyng, fro Jordan `til to Jerusalem.
Saboda haka dukan mutane Isra’ila suka bar Dawuda don su bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka kasance a wurin sarki tun daga Urdun har zuwa Urushalima.
3 And whanne the kyng hadde come in to his hows in Jerusalem, he took ten wymmen, hise secundarie wyues, whiche he hadde left to kepe the hous, and he bitook hem in to keping, and yaf mete to hem; and he entride not to hem; but thei weren closid `til to the dai of her deeth, and lyueden in widewehed.
Da Dawuda ya komo fadarsa a Urushalima, sai ya ɗauko ƙwarƙwaran goma nan da ya bari su lura da fada, ya keɓe su a wani gida inda za a yi tsaronsu. Ya tanada musu, amma bai kwana da su ba. Aka sa su a keɓe har iyakar rayuwarsu, suka yi zama kamar gwauraye.
4 Forsothe Dauid seide to Amasa, Clepe thou to gidere to me alle the men of Juda in to the thridde dai, and be thou present.
Sa’an nan sarki ya ce wa Amasa, “Ka tattaro mutanen Yahuda su zo wurina cikin kwana uku, kai kuwa ka kasance a can kai kanka.”
5 Therfor Amasa yede, that he clepe to gidere the puple of Juda; and he dwellide ouer the couenaunt, which the kyng hadde set to hym.
Amma da Amasa ya tafi kiran mutanen Yahuda, ya ɗauki lokaci fiye da lokacin da sarki ya ba shi.
6 Sotheli Dauid seide to Abisai, Now Siba, the sone of Botri, schal turmente vs more than Absolon dide; therfor take the seruauntis of thi lord, and pursue hym, lest in hap he fynde strengthid citees, and ascape vs.
Dawuda ya ce wa Abishai, “Ina gani Sheba ɗan Bikri zai ba mu wuya fiye da Absalom. Ka ɗauki mutanen maigidanka ka fafare shi, don kada yă sami garuruwa masu katanga yă tsere mana.”
7 Therfor the men of Joab yeden out with Abisai, and Cerethi and Ferethi, and alle stronge men yeden out of Jerusalem to pursue Siba, the sone of Bochry.
Saboda haka mutanen Yowab da Keretawa da Feletiyawa da dukan jarumawa suka fita a ƙarƙashin Abishai. Suka fita daga Urushalima don su fafari Sheba ɗan Bikri.
8 And whanne thei weren bisidis the greet stoon, which is in Gabaon, Amasa cam, and ran to hem; forsothe Joab was clothid with a streit coote at the mesure of his abit, and was gird aboue with a swerd, `ether dagger, hangynge doun `til to the entrayls in a schethe, `which swerd maad `craftily myyte go out bi liyt touchyng, and smyte. Therfor Joab seide to Amasa,
Yayinda suke a babban dutse a Gibeyon, Amasa ya zo don yă tarye su. Yowab kuwa yana sanye da doguwar rigar soja, a ɗamarar da ya sha kuwa akwai wuƙa a cikin kube. Da ya zo gaba sai wuƙar ta zāre daga kube ta fāɗi.
9 Heil, my brother! And he helde with the riyt hond the chyn of Amasa, as kissinge him.
Yowab ya ce wa Amasa, “Yaya kake, ɗan’uwana?” Sai Yowab ya kama gemun Amasa da hannun dama don yă yi masa sumba.
10 Forsothe Amasa took not kepe of the swerd, `which swerd Joab hadde, and Joab smoot Amasa in the side, and schedde out his entrailis in to the erthe, and Amasa was deed; and Joab addide not `the secounde wounde. Forsothe Joab and Abisai, his brother, pursueden Siba, the sone of Bochri.
Amasa kuwa bai lura da wuƙar da take hannun Yowab ba, Yowab kuwa ya soke shi da wuƙar a ciki, hanjinsa suka zube ƙasa. Ba tare da ƙarin suƙa ba, Amasa ya mutu. Sa’an nan Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka fafari Sheba ɗan Bikri.
11 In the meene tyme whanne `sum men of the children of Dauid, of the felowis of Joab, hadden stonde bisidis the deed bodi of Amasa, thei seiden, Lo! he that wolde be the felowe of Dauid for Joab.
Ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya kusa da Amasa ya ce, “Duk mai son Yowab, kuma duk mai son Dawuda, yă bi Yowab!”
12 Forsothe Amasa was bispreynt with blood, and lay in the myddil of the weie. Sum man siy this, that al the puple abood to se Amasa, and he remouyde Amasa fro the weie in to the feeld, and he hilide Amasa with a cloth, lest men passynge schulden abide for hym.
Amasa kuwa yana kwance cikin tafkin jininsa a kan hanya, sai mutumin ya ga dukan sojoji suka zo suka tsaya cik a can. Da ya gane cewa duk wanda ya haura zuwa wurin Amasa sai ya tsaya, sai ya ja gawar Amasa daga hanyar ya kai can cikin wani fili ya rufe shi da zane.
13 Therfor whanne he was remouyd fro the weie, ech man passide suynge Joab to pursue Siba, the sone of Bochri.
Bayan an ɗauke Amasa daga hanya, sai dukan mutane suka bi Yowab don fafaran Sheba ɗan Bikri.
14 Forsothe Siba hadde passide bi alle the lynagis of Israel til in to Habela, and in to Bethmacha; and alle chosun men weren gaderid to hym.
Sheba ya bi ta dukan kabilan Isra’ila zuwa Abel da kuma ta dukan yankin Beriyawa, waɗanda suka taru suka bi shi.
15 Therfor thei camen, and fouyten ayens hym in Habela, and in Bethmacha, and cumpassiden the citee with strengthingis; and the citee was bisegid. Sotheli al the cumpany, that was with Joab, enforside to distrie the wallis.
Sai dukan rundunonin da suke tare da Yowab suka zo suka yi wa Sheba kwanton ɓauna a Abel-Bet-Ma’aka. Suka tara ƙasa kewaye da jikin katangar birnin daidai da tsayinta. Sa’an nan waɗansu kuma suna ƙoƙarin rushe katangar.
16 And a wijs womman of the citee criede an hiy, Here ye! here ye! seie ye to Joab, Neiye thou hidur, and Y schal speke with thee.
Sai wata mata mai hikima ta yi kira daga ciki birnin ta ce, “Ku saurara! Ku saurara! Ku gaya wa Yowab yă zo nan ina so in yi magana da shi.”
17 And whanne he hadde neiyed to hir, sche seide to hym, Art thou Joab? And he answeride, Y am. To whom sche spak thus, Here thou the wordis of thin handmayde. Which Joab answeride, Y here.
Ya tafi wurinta, sai ta ce, “Kai ne Yowab?” Ya ce, “Ni ne”. Ta ce, “Ka ji abin da zan ce maka.” Ya ce, “Ina jinki.”
18 And eft sche seide, A word was seid in eld prouerbe, Thei that axen, axe in Habela; and so thei profitiden.
Ta ci gaba ta ce, “A dā can, akan ce, ‘Sami amsarka a Abel,’ shi ke nan an gama.
19 Whethir Y am not, that answere treuthe to Israel? and sekist thou to distrie a citee, and to distrie a modir citee in Israel? whi castidist thou doun the eritage of the Lord?
Mu ne masu salama da kuma amintattu na Isra’ila. Kana ƙoƙari ka hallaka birnin da yake uwa a Isra’ila. Don me kake so ka hallakar da gādon Ubangiji?”
20 And Joab answeride, and seide, Fer be, fer be this fro me; Y `caste not doun, nether Y distrye.
Yowab ya ce, “Allah yă sawwaƙe! Allah yă sawwaƙe in hallaka, ko in lalace gādon Ubangiji.
21 The thing hath not so it silf; but a man of the hil of Effraym, Siba, sone of Bochri, bi surname, reiside his hond ayens kyng Dauid; bitake ye him aloone, and we schulen go awei fro the citee. And the womman seide to Joab, Lo! his heed schal be sent to thee bi the wal.
Ba haka ba ne batun. Wani mai suna Sheba ɗan Bikri ne, daga ƙasar tudun Efraim, ya tayar wa sarki, yana gāba da Dawuda. Ki ba mu wannan mutum, zan kuwa janye daga birnin.” Matar ta ce wa Yowab, “Za a jefa maka kansa daga katanga.”
22 Therfor the womman entride to al the puple, and sche spak to hem wiseli; whiche `castiden forth to Joab the heed of Siba, sone of Bochri, gird of. And Joab sownede with a trumpe, and thei departiden fro the citee, ech man in to hise tabernaclis; forsothe Joab turnede ayen to Jerusalem to the kyng.
Sa’an nan matar ta tafi wurin dukan mutane da shawararta mai hikima, sai suka datse kan Sheba ɗan Bikri suka jefa wa Yowab. Saboda haka sai ya busa ƙaho, mutanensa kuwa suka watse daga birnin, kowa ya koma gidansa. Yowab kuma ya koma wurin sarki a Urushalima.
23 Therfor Joab was on al the oost of Israel; forsothe Benanye, sone of Joiada, was on Cerethi and Ferethi;
Yowab ne yake shugabancin dukan rundunoni; Benahiya ɗan Yehohiyada ne yake shugabancin Keretawa da Feletiyawa;
24 forsothe Adhuram was on tributis; forsothe Josaphat, sone of Achilud, was chaunceler; forsothe Siba was scryueyn;
Adoniram kuwa shi ne shugaban aikin gandu; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubucin tarihi;
25 forsothe Sadoch and Abiathar weren preestis;
Shewa kuwa magatakarda; Zadok da Abiyatar su ne firistoci;
26 forsothe Hira of Hiarith was preest of Dauid.
Ira mutumin Yayir kuwa shi ne firist na Dawuda.