< 2 Samuel 12 >

1 Therfor the Lord sente Nathan to Dauid; and whanne he hadde come to Dauid, he seide to Dauid, Answere thou doom to me; twei men weren in o citee; o man was riche, and the tother was pore.
Ubangiji ya aiki Natan wurin Dawuda. Da ya tafi wajensa, sai ya ce, “An yi waɗansu mutum biyu a wani gari, ɗaya mai arziki, ɗayan kuma matalauci.
2 The riche man hadde ful many scheep, and oxun;
Mai arzikin yana da babban garken tumaki, da kuma shanu,
3 sotheli the pore man hadde vttirli no thing, outakun o litil scheep, which he hadde bouyt, and nurschid, and which `hadde wexid at hym with hise sones, and eet togidere of his breed, and drank of his cuppe, and slepte in his bosum; and it was as a douyter to hym.
amma matalauci ba shi da kome sai’yar tunkiyar da ya sayo. Ya yi kiwonta, ta kuwa yi girma tare shi da yaransa. Takan ci tare da shi ta sha ruwa a kwaf nasa, har ma ta kwanta a ƙirjinsa. Ta ma zama kamar’ya a gare shi.
4 Forsothe whanne a pilgrym `hadde come to the riche man, he sparide to take of hise scheep and oxun, that he schulde make a feeste to that pilgrym, that cam to hym; and he took the scheep of the pore man, and `made redi metis to the man that cam to hym.
“To, sai ga wani baƙo ya zo wurin mai arzikin nan, amma mai arzikin ya ƙi yă kama tunkiyarsa, ko saniyarsa yă yanka don yă shirya wa baƙon da ya zo abinci. A maimako, sai ya je ya kama’yar tunkiyan nan ta matalaucin ya yanka ya shirya wa mutumin da ya zo masa.”
5 Forsothe Dauid was ful wrooth with indignacioun ayens that man, and seide to Nathan, The Lord lyueth, for the man that dide this is the sone of deeth;
Dawuda ya husata ƙwarai da mutumin, ya ce wa Natan, “Muddin Ubangiji yana a raye, mutumin da ya yi wannan ya cancanci yă mutu!
6 he schal yelde the scheep in to foure folde, for he dide this word, and sparide not.
Dole yă biya diyyar tunkiyan nan sau huɗu, domin ya aikata haka ba tausayi.”
7 Forsothe Nathan seide to Dauid, Thou art thilke man, that hast do this thing. The Lord God of Israel seith these thingis, Y anoyntide thee `in to kyng on Israel, and Y delyuerede thee fro the hond of Saul,
Sai Natan ya ce wa Dawuda, “Kai ne mutumin! Ga abin da Ubangiji, Allah ya ce, ‘Na naɗa ka sarki bisa Isra’ila, na kuma cece ka daga hannun Shawulu.
8 and Y yaf to thee the hows of thi lord, and the wyues of thi lord in thi bosum, and Y yaf to thee the hows of Israel, and of Juda; and if these thingis ben litil, Y schal adde to thee myche grettere thingis.
Na ba ka gidan maigidanka, da matan maigidanka duka. Na ba ka gidan Isra’ila da Yahuda. Da a ce dukan waɗannan sun kāsa maka, ai, da na ƙara maka.
9 Whi therfor hast thou dispisid the word of the Lord, that thou didist yuels in my siyt? Thou hast smyte by swerd Vrye Ethei, and thou hast take his wijf in to wijf to thee, and thou hast slayn hym with the swerd of the sones of Amon.
Me ya sa ka rena maganar Ubangiji ta wurin yin mugunta haka a idonsa? Ka kashe Uriya mutumin Hitti da takobi, ka kuma ɗauki matarsa tă zama matarka. Ka kashe shi da takobin Ammonawa.
10 Wherfor swerd schal not go awey fro thin hows til in to with outen ende; for thou dispysidist me, and tokist the wijf of Vrye Ethei, that sche schulde be thi wijf.
To, fa, takobi ba zai taɓa rabu da gidanka ba, domin ka rena ni, ka kuma ƙwace matar Uriya mutumin Hitti ta zama matarka.’
11 Therfor the Lord seith these thingis, Lo! Y schal reise on thee yuel of thin hows, and Y schal take thi wyues in `thin iyen, and Y schal yyue to thi neiybore, and he schal slepe with thi wyues in the iyen of this sunne, `that is, opynli bifor alle men, as in xv. chapitre.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Daga cikin iyalinka zan kawo masifa a kanka. A idanunka zan ɗauki matanka in ba wa wani da yake kusa da kai, zai kuwa kwana da su da rana tsaka.
12 For thou hast do priueli; forsothe Y schal do this word in the siyt of al Israel, and in the siyt of this sunne.
Ka aikata wannan a ɓoye, amma zan aikata wannan da rana tsaka, a gaban dukan Isra’ila.’”
13 And Dauid seide to Nathan, Y haue synned to the Lord. And Nathan seide to Dauid, Also the Lord hath turned awei thi synne; thou schalt not die.
Sai Dawuda ya ce wa Natan, “Na yi wa Ubangiji zunubi.” Natan ya ce, “Ubangiji ya yafe maka zunubin. Ba za ka mutu ba.
14 Netheles for thou madist enemyes to blasfeme the name of the Lord, for this word the child which is borun to thee schal die bi deeth.
Amma saboda ka yi haka ka sa abokan gāba suka rena Ubangiji, yaron da aka haifa maka zai mutu.”
15 And Nathan turnede ayen in to his hows. And the Lord smoot the litil child, whom the wijf of Vrye childide to Dauid, and he dispeiride.
Bayan Natan ya tafi gida, sai Ubangiji ya bugi yaron da matar Uriya ta haifa wa Dawuda, ya kuwa kamu da ciwo.
16 And Dauid preiede the Lord for the litil child; and Dauid fastide bi fastyng, and entride asidis half, and lai on the erthe.
Dawuda ya roƙi Allah saboda yaron. Ya yi azumi, ya kuma shiga gidansa ya kwana kwance a ƙasa.
17 Sotheli the eldere men of his hows camen, and constreyneden hym `bi meke preieris, that he schulde rise fro the erthe; and he nolde, nethir he eet mete with hem.
Dattawan iyalinsa suka tsaya kusa da shi don su ɗaga shi daga ƙasa, amma ya ƙi, bai kuwa ci wani abu tare da su ba.
18 Forsothe it bifelde in the seuenthe dai, that the yong child diede; and the seruauntis of Dauid dredde to telle to hym, that the litil child was deed; for thei seiden, Lo! whanne the litil child lyuede yit, we spaken to hym, and he herde not oure vois; hou myche more, if we seien the child is deed, he schal turment himsilf?
A rana ta bakwai sai yaron ya rasu. Barorin Dawuda suka ji tsoro su gaya masa cewa yaron ya mutu, gama sun yi tunani cewa, “Yayinda yaron yake da rai, mun yi magana da Dawuda bai ji mu ba. Yaya za mu gaya masa yaron ya mutu? Ai, zai yi wa kansa ɓarna.”
19 Therfore whanne Dauid hadde herd his seruauntis spekynge priueli, `ether moterynge, he understood that the yong child was deed; `and he seyde to his seruauntis, Whether the child is deed? Whiche answeriden to hym, He is deed.
Dawuda ya gane bayinsa suna wa juna raɗan wani abu, sai ya gane yaron ya mutu. Sai ya ce, “Yaron ya rasu ko?” Suka ce, “I, ya rasu.”
20 Therfor Dauid roos fro the erthe, and was waischid, and anoyntid; and whanne he hadde chaungid cloth, he entride in to the hows of the Lord, and worschipide, and cam in to his hows; and he axide, that thei schulden sette breed to hym, and he eet.
Sa’an nan Dawuda ya tashi daga ƙasa. Bayan ya yi wanka, ya shafa mai, ya kuma canja rigunarsa, sa’an nan ya shiga gidan Ubangiji ya yi sujada. Sai ya tafi gidansa, ya nemi a ba shi abinci, aka ba shi, ya kuwa ci.
21 Sothely his seruauntis seiden to hym, What is the word which thou hast do? Thou fastidist, and weptist for the yong child, whanne he lyuede yit; sotheli whanne the child was deed, thou risidist and etist breed?
Barorinsa suka ce masa, “Me ya sa kake yin haka? Yayinda yaron yake da rai, ka yi azumi, ka kuma yi kuka, amma yanzu da yaron ya mutu, ka tashi, ka kuma ci abinci!”
22 And Dauid seide, Y fastide and wepte for the yong child, whanne he lyuyde yit; for Y seide, Who woot, if perauenture the Lord yyue hym to me, and the yong child lyue?
Ya ce musu, “Yayinda yaron yake da rai, na yi azumi, na kuma yi kuka. Na yi tunani na ce, ‘Wa ya sani? Ko Ubangiji zai yi mini alheri yă bar yaron yă rayu.’
23 `Now forsothe for he is deed, whi `fast Y? whether Y schal mow ayen clepe hym more? Y schal `go more to hym, but he schal not turne ayen to me.
Amma yanzu da ya mutu, me zai sa in yi azumi? Zan iya dawo da shi ne? Ni zan je wajensa, ba shi zai dawo wurina ba.”
24 And Dauid coumfortid Bersabee, his wijf; and he entride to hir, and slepte with hir. And sche gendride a sone, and Dauid clepide his name Salomon; and the Lord louyde hym.
Sai Dawuda ya yi wa matarsa Batsheba ta’aziyya, ya kuma tafi wurinta ya kwana da ita. Ta kuma haifi ɗa, suka ba shi suna Solomon. Ubangiji ya ƙaunace shi;
25 And he sente Salomon in the hond of Nathan, the prophete; and he clepide his name Amyable to the Lord, for the Lord louyde hym.
kuma saboda Ubangiji ya ƙaunace shi, sai ya aika da saƙo ta wurin annabi Natan yă ba shi suna Yedidiya.
26 Therfor Joab fauyt ayens Rabath, of the sones of Amon, and he fauyt ayens the `kyngis citee.
Ana cikin haka, sai Yowab ya yi yaƙi da Rabba na Ammonawa, ya kuma ƙwace babban birnin.
27 And Joab sente messangeris to Dauid, and seide, Y fauyte ayens Rabath, and the citee of watris schal be takun.
Sa’an nan Yowab ya aika manzanni wurin Dawuda yana cewa, “Na yaƙi Rabba na kuma ƙwace hanyar samun ruwanta.
28 Now therfor gadere thou the tother part of the puple, and bisege thou the citee, and take thou it, lest whanne the citee is wastid of me, the victorie be arettid to my name.
Yanzu fa ka tattara saura rundunoni ka fāɗa wa birnin ka ci shi. In ba haka ba zan karɓe birnin, a kuma kira shi da sunana.”
29 Therfor Dauid gaderide al the puple, and he yede forth ayens Rabath; and whanne he hadde fouyte, he took it.
Saboda haka Dawuda ya tattara sauran rundunar sojojin suka tafi Rabba suka fāɗa masa suka kuma ci shi.
30 And he took the diademe of the kyng of hem fro his heed, bi weiyte a talent of gold, hauynge preciouseste peerlis; and it was put on the heed of Dauid, `that is, aftir that it was weldid and purgid bi fier; but also Dauid bar awey ful myche prey of the citee.
Ya ɗauke rawanin daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti, na zinariya, an kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, aka aza shi a kan Dawuda. Ya kuma kwashe ganima mai yawa daga garin.
31 Also he ledde forth the puple therof, and sawide, and `dide aboute hem `yrun instrumentis of turment, and departide with knyues, and `ledde ouer bi the licnesse of tijl stoonus; so he dide to alle the citees of the sones of Amon. And Dauid turnede ayen, and al his oost, in to Jerusalem.
Ya fito da mutanen da suke a can, ya sa su su yi aiki da zarto, da diga, da kuma gatari, ya kuma sa su bugan bulok. Haka ya yi wa dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da dukan sojoji suka koma Urushalima.

< 2 Samuel 12 >