< 2 Peter 3 >

1 Lo! ye moost dereworth britheren, Y write to you this secounde epistle, in which Y stire youre clere soule bi monesting togidere,
Abokaina ƙaunatattu, wannan ita ce wasiƙata ta biyu gare ku. Na rubuta su biyun su zama abin tuni don su faɗakar da ku ga tunani mai kyau.
2 that ye be myndeful of tho wordis, that Y biforseide of the hooli prophetis, and of the maundementis of the hooli apostlis of the Lord and sauyour.
Ina so ku tuna da kalmomin da annabawa masu tsarki na dā suka faɗa da kuma umarnin da Ubangijinmu da Mai Cetonmu ya bayar ta wurin manzanninku.
3 First wite ye this thing, that in the laste daies disseyueris schulen come in disseit, goynge aftir her owne coueityngis,
Da farko dai, dole ku fahimci wannan cewa a kwanakin ƙarshe masu ba’a za su zo suna ba’a, suna bin mugayen sha’awace-sha’awacensu.
4 seiynge, Where is the biheest, or the comyng of hym? for sithen the fadris dieden, alle thingis lasten fro the bigynnyng of creature.
Za su ce, “Ina wannan ‘dawowar’ da ya yi alkawari ne? Tun mutuwar kakanninmu, kome yana tafiya kamar yadda yake tun farkon halitta.”
5 But it is hid fro hem willynge this thing, that heuenes were bifore, and the erthe of water was stondynge bi watir, of Goddis word;
Amma da gangan suke manta cewa tun dā can ta wurin maganar Allah sammai suka kasance aka kuma yi ƙasa daga ruwa ta wurin ruwa kuma.
6 bi which that ilke world clensid, thanne bi watir perischide.
Ta wurin waɗannan ruwan ne aka nutsar, aka kuma hallakar da duniya ta wancan lokaci.
7 But the heuenes that now ben, and the erthe, ben kept bi the same word, and ben reseruyd to fier in to the dai of doom and perdicioun of wickid men.
Ta wurin wannan magana ce aka ajiye sammai da ƙasa na yanzu domin wuta, an ajiye su kuma don ranar hukunci da hallaka ta mutane marasa tsoron Allah.
8 But, ye moost dere, this o thing be not hid to you, that o dai anentis God is as a thousynde yeeris, and a thousynde yeeris ben as o dai.
Amma kada ku manta da wannan abu guda ɗaya, abokaina ƙaunatattu. Ga Ubangiji kwana ɗaya kamar shekaru dubu ne, shekaru dubu kuma kamar kwana ɗaya ne.
9 The Lord tarieth not his biheest, as summe gessen, but he doith pacientli for you, and wole not that ony men perische, but that alle turne ayen to penaunce.
Ubangiji ba mai jinkiri ba ne wajen cika alkawarinsa, yadda waɗansunku suka fahimci jinkiri. Yana haƙuri da ku, ba ya so wani yă hallaka, sai dai kowa yă kai ga tuba.
10 For the dai of the Lord schal come as a theef, in which heuenes with greet bire schulen passe, and elementis schulen be dissoluyd bi heete, and the erthe, and alle the werkis that ben in it, schulen be brent.
Amma ranar Ubangiji za tă zo kamar ɓarawo. Sammai za su ɓace da ruri, abubuwan da suke cikinsu za su ƙone, ƙasa kuma da dukan abin da yake cikinta za su tonu.
11 Therfor whanne alle these thingis schulen be dissolued, what manner men bihoueth it you to be in hooli lyuyngis and pitees,
Da yake za a hallaka dukan abubuwa ta haka, waɗanne irin mutane ne ya kamata ku zama? Ya kamata ku yi rayuwar tsarki da ta tsoron Allah,
12 abidinge and hiyynge in to the comyng of the dai of oure Lord Jhesu Crist, bi whom heuenes brennynge schulen be dissoluyd, and elementis schulen faile bi brennyng of fier.
yayinda kuke zuba ido ga zuwan ranar Allah kuna gaggauta zuwanta. Wannan rana za tă kawo wa sammai hallaka ta ƙunan wuta, abubuwa kuma za su narke don zafi.
13 Also we abiden bi hise biheestis newe heuenes and newe erthe, in which riytwisnesse dwellith.
Amma bisa ga alkawarinsa muna zuba ido ga sabuwar sama da kuma sabuwar ƙasa, inda adalci zai yi zama.
14 For which thing, ye moost dere, abidynge these thingis, be ye bisye to be foundun to hym in pees vnspottid and vndefoulid.
Saboda haka, abokaina ƙaunatattu, da yake kuna zuba ido ga wannan, sai ku yi matuƙar ƙoƙari don a same ku ba tabo, sai dai zaman salama da shi.
15 And deme ye long abiding of oure Lord Jhesu Crist youre heelthe, as also oure moost dere brother Poul wroot to you, bi wisdom youun to hym.
Ku yi zaman sanin cewa haƙurin Ubangijinmu yana nufin ceto ne, kamar yadda ƙaunataccen ɗan’uwanmu Bulus ma ya rubuta muku da hikimar da Allah ya ba shi.
16 As and in alle epistlis he spekith `in hem of these thingis; in which ben summe hard thingis to vndurstonde, whiche vnwise and vnstable men deprauen, as also thei don othere scripturis, to her owne perdicioun.
Haka yake rubutu cikin dukan wasiƙunsa, yana magana a cikinsu a kan waɗannan al’amura. Wasiƙunsa sun ƙunshi waɗansu abubuwa masu wuyar fahimta, waɗanda jahilai da kuma waɗanda ba tsayayyu ba ne suke murɗe ma’anarsu, kamar yadda suke yi da sauran Nassosi, ta haka suke jawo wa kansu hallaka.
17 Therfor ye, britheren, bifor witynge kepe you silf, lest ye be disseyued bi errour of vnwise men, and falle awei fro youre owne sadnesse.
Saboda haka, abokaina ƙaunatattu, da yake kun riga kun san wannan, sai ku zauna a faɗake don kada a ɗauke hankalinku ta wurin kuskuren marasa bin dokan nan har ku fāɗi daga matsayinku.
18 But wexe ye in the grace and the knowyng of oure Lord Jhesu Crist and oure Sauyour; to hym be glorie now and in to the dai of euerlastyngnesse. Amen. (aiōn g165)
Sai dai ku yi girma cikin alheri da sanin Ubangijinmu da Mai Cetonmu Yesu Kiristi. A gare shi ɗaukaka ta tabbata yanzu da har abada! Amin. (aiōn g165)

< 2 Peter 3 >

The Great Flood
The Great Flood