< 2 Kings 1 >

1 Forsothe Moab trespasside ayens Israel, after that Achab was deed.
Bayan mutuwar Ahab, Mowab ta yi wa Isra’ila tawaye.
2 And Ocozie felde thorou the aleris of his soler, which he hadde in Samarie, and was sijk; and he sente messangeris, and seide to hem, Go ye, and councele Belzebub, god of Acharon, whether Y may lyue after this sijknesse of me.
Ahaziya fa ya fāɗo daga tagar ɗakin samansa a Samariya ya ji rauni. Saboda haka ya aiki masinjoji, yana cewa, “Ku je ku tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron, ku ga ko zan warke daga wannan rauni.”
3 Forsothe the aungel of the Lord spak to Elye of Thesbi, and seide, Rise thou, and go doun into the metynge of the messangeris of the kyng of Samarie; and thou schalt seie to hem, Whether God is not in Israel, that ye go to counsel Belzebub, god of Acharon?
Amma mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya mutumin Tishbe, “Ka haura ka taryi masinjojin sarkin Samariya, ka tambaye su, ‘Don babu Allah ne a Isra’ila da za ku tafi ku tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron?’
4 For which thing the Lord seith these thingis, Thou schalt not go doun of the bed, on which thou stiedist.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ba za ka tashi daga inda kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!’” Iliya ya yi kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, sai ya tafi.
5 And Elie yede. And the messangeris turneden ayen to Ocozie. And he seide to hem, Whi turneden ye ayen?
Da masinjojin suka koma wurin sarki, sai sarki ya ce da su, “Don me kuka komo?”
6 And thei answeriden to hym, A man mette vs, and seide to vs, Go ye, turne ye ayen to the kyng, that sente you; and ye schulen seie to him, The Lord seith these thingis, Whether for God was not in Israel, thou sendist, that Belzebub, god of Acharon, be counselid? Therfor thou schalt not go doun of the bed, on which thou stiedist, but thou schalt die bi deeth.
Sai suka amsa, “Wani mutum ya sadu da mu ya ce mana, ‘Ku koma wurin sarkin da ya aike ku, ku ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah ne a Isra’ila da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub allahn Ekron? Saboda haka ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba. Ba shakka za ka mutu!”’”
7 Which Ocozie seide to hem, Of what figure and abite is that man, that mette you, and spak to you these wordis?
Sai Sarkin ya tambaye su ya ce, “Wanda irin mutum ne ya yi muku wannan magana?”
8 And thei seiden, An heeri man, and gird with a girdil of skyn in the reynes. Which seide to hem, It is Elie of Thesbi.
Sai suka ce, “Mutumin ya sa riga mai gashi, ya kuma yi ɗamara da fata.” Sarkin ya ce, “Ai, Iliya mutumin Tishbe nan ne.”
9 And he sente to Elie a prince of fifti, and fifti men that weren vndur hym. Which prince stiede to hym, and seide to hym, sittynge in the cop of the hil, Man of God, the kyng comaundith, that thou come doun.
Sai sarki ya aiki kaftin da sojojin hamsin wurin Iliya. Kaftin ya haura wajen Iliya, wanda yake zaune a kan tudu, ya ce masa, “Mutumin Allah, sarki ya ce, ‘Ka sauko, ka zo!’”
10 And Elie answeride, and seide to the prince of fifti men, If Y am the man of God, fier come doun fro heuene, and deuoure thee and thi fifti men. Therfor fier cam doun fro heuene, and deuouride hym, and the fifti men that weren with hym.
Iliya ya ce masa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta tă sauko daga sama tă cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wuta ta sauko daga sama ta cinye kaftin tare da sojojinsa hamsin.
11 Eft he sente to Elie another prince of fifti, and fifti men with hym, which spak to Helye, Man of God, the kyng seith these thingis, Haste thou, come thou doun.
Da jin haka sai sarki ya sāke aiken wani kaftin tare da waɗansu sojojinsa hamsin wurin Iliya. Kaftin ya ce wa Iliya, “Mutumin Allah, ga abin da sarki ya ce, ‘Ka sauko, nan take ka zo!’”
12 Elie answeride, and seide, If Y am the man of God, fier come doun fro heuene, and deuoure thee and thi fifti men. Therfor the fier of God cam doun fro heuene, and deuouride hym and hise fifti men.
Sai Iliya ya amsa, “In ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta cinye ka da sojojinka hamsin!” Sai wutar Allah ta sauko daga sama ta cinye shi da sojojinsa hamsin.
13 Eft he sente the thridde prince of fifti men, and fifti men that weren with hym. And whanne this prynce hadde come, he bowide the knees ayens Elie, and preiede hym, and seide, Man of God, nyle thou dispise my lijf, and the lyues of thi seruauntis that ben with me.
Saboda haka sai sarki ya aiki kaftin na uku da sojojinsa hamsin. Wannan kaftin na ukun ya haura ya durƙusa a gaban Iliya, ya roƙe shi ya ce, “Mutumin Allah, ina roƙonka ka dubi darajar raina da na waɗannan sojoji hamsin, bayinka!
14 Lo! fier cam doun fro heuene, and deuouride tweyne, the firste princis of fifti men, and the fifti men that weren with hem; but now, Y biseche, that thou haue mercy on my lijf.
Duba, wuta ta sauko daga sama ta cinye su kaftin nan biyu waɗanda suka zo da farko da dukan sojojinsu. To, yanzu dai, ka daraja raina!”
15 Forsothe the aungel of the Lord spak to Helie of Thesbi, and seide, Go thou doun with hym; drede thou not. Therfor Elie roos, and cam doun with hym to the kyng;
Sai mala’ikan Ubangiji ya ce wa Iliya, “Sauka, ka tafi tare da shi; kada ka ji tsoro.” Saboda haka Iliya ya tashi ya sauko, ya tafi tare da shi wajen sarki.
16 and he spak to the kyng, The Lord seith thes thingis, For thou sentist messangeris to counsele Belzebub, god of Acharon, as if no God were in Israel, of whom thow myytist axe a word; therfor thou schalt not go doun of the bed, on which thou stiedist, but thou schalt die bi deeth.
Iliya ya ce wa sarki, “Ga abin da Ubangiji ya ce, don babu Allah a Isra’ila ne wanda za ka tuntuɓa da ka aika a tuntuɓi Ba’al-Zebub, allahn Ekron? Domin ka yi haka, ba za ka tashi daga gadon da kake kwance ba, ba shakka za ka mutu!”
17 Therfor he was deed bi the word of the Lord, which word Elie spak; and Joram, hys brothir, regnyde for hym, in the secounde yeer of Joram, the sone of Josephat, kyng of Juda; for Ocozie hadde no sone.
Ya kuwa mutu yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya. Da yake Ahaziya ba shi da ɗa, sai Yoram ya gāje shi, ya zama sarki a shekara ta biyu ta mulkin Yehoram, ɗan Yehoshafat, sarkin Yahuda.
18 Sotheli the residue of wordis of Ocozie, whiche he wrouyte, whether these ben not writun in the book of wordis of daies of the kyngis of Israel?
Game da dukan sauran abubuwan da suka faru a zamani Ahaziya, da abin da ya yi, ba a rubuce suke a littattafan tarihin sarakuna Isra’ila ba?

< 2 Kings 1 >