< 2 Kings 3 >
1 Forsothe Joram, sone of Achab, regnede on Israel, in Samarie, in the eiytenthe yeer of Josephat, kyng of Juda. And he regnede twelue yeer,
Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
2 and he dide yuel bifor the Lord, but not as his fader and modir;
Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
3 for he took awei the ymagis of Baal, whiche his fadir hadde maad, netheles in the synnes of Jeroboam, sone of Nabath, that made Israel to do synne, `he cleuyde, and yede not awei fro tho.
Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
4 Forsothe Mesa, kyng of Moab, nurschide many beestis, and paiede to the kyng of Israel an hundrid thousynde of lambren, and an hundrid thousynde of wetheris, with her fleesis.
Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
5 And whanne Achab was deed, he brak the boond of pees, which he hadde with the kyng of Israel.
Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
6 Therfor kyng Joram yede out of Samarie in that dai, and noumbride al Israel.
To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
7 And he sente to Josephat, kyng of Juda, and seide, The kyng of Moab yede awei fro me; come thou with me ayens him to batel. Which Josephat answeride, Y schal stie; he that is myn, is thin; my puple is thi puple; and myn horsis ben thin horsis.
Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
8 And he seide, Bi what weie schulen we stie? And he answeride, Bi the deseert of Ydumee.
Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
9 Therfor the kyng of Israel, and the kyng of Juda, and the kyng of Edom, yeden forth, and cumpassiden bi the weie of seuene daies; and `watir was not to the oost, and to the beestis, that sueden hem.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
10 And the kyng of Israel seide, Alas! alas! alas! the Lord hath gaderide vs thre kyngis to bitake vs in the hond of Moab.
Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
11 And Josephat seide, Whether ony prophete of the Lord is here, that we biseche the Lord bi hym? And oon of the seruauntis of the kyng of Israel answeride, Elisee, the sone of Saphat, is here, that schedde watir on the hondis of Elie.
Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
12 And Josephat seide, Is the word of the Lord at hym? Whiche seiden, `It is. And the kyng of Israel, and Josephat, kyng of Juda, and the kyng of Edom, yeden doun to hym.
Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
13 Forsothe Elise seide to the kyng of Israel, What is to me and to thee? Go thou to the prophetis of thi fadir and of thi modir. And the kyng of Israel seide to hym, Whi hath the Lord gaderid these thre kyngis, to bitake hem into the hondis of Moab?
Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
14 And Elisee seide to hym, The Lord of oostis lyueth, in whos siyt Y stonde, if Y were not aschamed of the cheer of Josephat, king of Juda, treuli Y hadde not perseyued, nethir Y hadde biholde thee.
Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
15 Now forsothe brynge ye to me a sautrere. And whanne the sautrere song, the hond of the Lord was maad on hym, and he seide, The Lord seith these thingis,
Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
16 Make ye the wombe, ether depthe, of this stronde dichis and dichis.
ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
17 For the Lord seith these thingis, Ye schulen not se wynd, nethir reyn, and this depthe schal be fillid with watris, and ye schulen drynke, and youre meynees, and youre beestis.
Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
18 And this is litil in the siyt of the Lord. Ferthermore also he schal bitake Moab in to youre hondis;
Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
19 and ye schulen smyte ech strengthid citee, and ech chosun citee, and ye schulen kitte doun ech tre berynge fruyt, and ye schulen stoppe alle the wellis of watris, and ye schulen hile with stonys ech noble feeld.
Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
20 Therfor it was doon eerli, whanne sacrifice is wont to be offrid, and, lo! watris camen bi the weie of Edom, and the lond was fillid with watris.
Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
21 Sotheli alle men of Moab herden, that kyngis hadden stied to fiyte ayens hem; `and men of Moab clepiden togidere alle men, that weren gird with girdil aboue, and thei stoden in the termes.
To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
22 And men of Moab risiden ful eerli, and whanne the sunne was risun thanne euen ayens the watris, thei sien the watris reed as blood euene ayens.
Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
23 And thei seiden, It is the blood of swerd, `that is, sched out bi swerd; kyngis fouyten ayens hem silf, and thei ben slayn togider; now go thou, Moab, to the prey.
Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
24 And thei yeden in to the castels of Israel; forsothe Israel roos, and smoot Moab, and thei fledden bifor men of Israel. Therfor thei that hadden ouercome, camen, and smytiden Moab, and destrieden cytees;
Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
25 and alle men sendynge stoonys filliden ech beste feeld, and stoppiden alle the wellis of watris, and kittiden doun alle trees berynge fruyt, so that oneli `wallis maad of erthe weren left; and the citee was cumpassid of men settinge engynes, and was smytun bi greet part.
Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
26 And whanne the kyng of Moab hadde seyn this, that is, that the enemyes hadden the maistrie, he took with hym seuene hundrid men drawynge swerdis, that thei shulden breke in to the kyng of Edom; and thei myyten not.
Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
27 And he took his firste gendrid sone, that schulde regne for hym, and offride brent sacrifice on the wal; and greet indignacioun was maad in Israel; and anoon thei yeden awei fro hym, and turneden ayen in to her lond.
Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.