< 2 Kings 18 >

1 In the thridde yeer of Osee, sone of Hela, kyng of Israel, regnyde Ezechie, sone of Achaz, kyng of Juda.
A shekara ta uku ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila, Hezekiya ɗan Ahaz sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 He was of fyue and twenti yeer, whanne he bigan to regne, and he regnyde in Jerusalem nyne and twenti yeer; the name of his modir was Abisa, douyter of Zacharie.
Yana da shekara ashirin da biyar da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara ashirin da tara a Urushalima. Sunan mahaifiyarsa Abiya’yar Zakariya.
3 And he dide that, that was good bifor the Lord, bi alle thingis, which Dauid, his fadir, hadde do.
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda kakansa Dawuda ya yi.
4 And he distriede hiye places, and al to-brak ymagis, and kittide doun wodis, and he brak the brasun serpent, whom Moyses hadde maad; for `til to that tyme the sones of Israel brenten encense to it; and he clepide the name therof Noestam.
Ya kawar da masujadan kan tudu, ya farfasa keɓaɓɓun duwatsu, ya sassare ginshiƙan Ashera. Ya fashe macijin tagullan da Musa ya yi, gama har zuwa lokacin nan Isra’ilawa suna ƙona turare gare shi. (An ba shi suna Nehushtan.)
5 And he hopide in the Lord God of Israel; therfor aftir hym noon was lijk hym of alle the kyngis of Juda, but `and nether in tho kyngis that weren bifor hym.
Hezekiya ya dogara ga Ubangiji, Allah na Isra’ila. Ba a yi wani kamar sa ba cikin dukan sarakunan Yahuda; ko kafin shi, ko kuma bayansa.
6 And he cleuyde to the Lord, and yede not awei fro hise steppis, and he dide the comaundementis of the Lord, whiche the Lord comaundide to Moises;
Ya manne wa Ubangiji, bai fasa binsa ba; ya yi biyayya da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa.
7 wherfor and the Lord was with hym, and he gouernede wiseli hym silf in alle thingis, to whiche he yede forth. Also he rebellide ayens the kyng of Assiriens, and therfor he seruede not to `that kyng of Asseriens;
Ubangiji kuma ya kasance tare da shi, ya yi nasara a duk abin da ya sa hannu. Ya yi tawaye ga sarkin Assuriya, ya ƙi yă bauta masa.
8 and he smoot Philisteis `til to Gazam, and alle the termes of hem, fro the tour of keperis `til to a citee maad strong.
Daga hasumiya zuwa birni mai katanga, ya ci Filistiyawa da yaƙi, har zuwa Gaza da kewaye.
9 In the fourthe yeer of kyng Ezechie, that was the seuenthe yeer of Osee, sone of Hela, kyng of Israel, Salmanazar, kyng of Assiriens, stiede to Samarie,
A shekara ta huɗu ta Hezekiya, wato, shekara ta bakwai ke nan ta mulkin Hosheya ɗan Ela sarkin Isra’ila; Shalmaneser Sarkin Assuriya ya tasam ma Samariya da yaƙi; ya kewaye ta.
10 and fauyt ayens it, and took it. For after thre yeer, in the sixte yeer of Ezechie, that is, in the nynthe yeer of Osee, kyng of Israel, Samarie was takun;
A ƙarshen shekara ta uku, Assuriyawa suka ci Samariya da yaƙi. An ci Samariya da yaƙi a shekara ta shida ta mulki Hezekiya, wanda ya zo daidai da shekara ta tara ta mulkin Hosheya sarkin Isra’ila.
11 and the kyng of Assiriens translatide Israel in to Assiriens, and settyde hem in Haila, and in Habor, ryueris of Gozam, in the citees of Medeis;
Sarkin Assuriya ya kwashe Isra’ila zuwa Assuriya ya zaunar da su a Hala, da Gozan a kogin Habor da kuma garuruwan Medes.
12 for thei herden not the vois of her Lord God, but thei braken his couenaunt; thei herden not, nether diden alle thingis, whiche Moises, the seruaunt of the Lord, comaundide.
Wannan ya faru ne domin ba su yi biyayya ga Ubangiji Allahnsu ba, amma suka karya alkawarinsu; da dukan abin da Musa bawan Ubangiji ya umarta. Ba su saurari umarnin ba, balle su kiyaye su.
13 In the fourtenthe yeer of kyng Ezechie, Senacherub, kyng of Assiryens, stiede to alle the strengthide citees of Juda, and took tho.
A shekara ta goma sha huɗu ta mulkin sarkin Hezekiya, sai sarki Sennakerib sarkin Assuriya ya kai farmaki wa biranen Yahuda masu katanga ya kuma kama su.
14 Thanne Ezechie, kyng of Juda, sente messangeris to the kyng of Assiriens in to Lachis, and seide, Y haue synned; go awei fro me, and Y schal bere `al thing, which thou schalt putte to me. Therfor the kyng of Asseriens puttide on Ezechie, kyng of Juda, thre hundrid talentis of siluer, and thretti talentis of gold.
Sai Hezekiya sarkin Yahuda ya aika saƙo ga sarkin Assuriya a Lakish cewa, “Na yi laifi, ka janye daga gare ni, zan kuma biya ka duk abin da ake bukata daga gare ni.” Sarkin Assuriya ya karɓi talenti ɗari uku na azurfa, da talenti talatin na zinariya daga hannun Hezekiya sarkin Yahuda.
15 And Ezechie yaf al the siluer, that was foundun in the hows of the Lord, and in the kyngis tresories.
Ya zama kuwa cewa, Hezekiya ya bayar da dukan azurfan da suke a haikalin Ubangiji da kuma a ma’ajin fadan sarki.
16 In that tyme Ezechie brak the yatis of the temple of the Lord, and the platis of gold, whiche he hadde fastned, and he yaf tho to the kyng of Assiriens.
A wannan lokaci ne Hezekiya sarkin Yahuda ya ɓaɓɓalle zinariyan da aka dalaye ƙofofi da madogaran ƙofofin haikalin Ubangiji, ya ba sarkin Assuriya.
17 Forsothe the kyng of Assiriens sente Thercha and Rabsaces fro Lachis to kyng Ezechie, with strong hond to Jerusalem; and whanne thei hadden stied, thei camen to Jerusalem, and stoden bisidis the water cundijt of the hiyere cisterne, which is in the weie of the fullere, `ethir toukere.
Sai sarkin Assuriya ya aika da babban shugaban sojojinsa, da shugaban dattawansa, da wakilinsa daga birnin Lakish tare da ƙungiyar sojoji masu yawa zuwa Urushalima domin su yaƙi Sarki Hezekiya. Da suka haura sai suka tsaya a wurin lambatun da yake kawo ruwa daga Tafkin Tudu, kusa da hanyar Filin Mai Wanki.
18 And thei clepiden the kyng; sotheli Eliachym, sone of Elchie, the souereyn of the hows, and Sobna, scryueyn, and Joahe, chaunseler, the sone of Asaph, yeden out to hem.
Suka kira sarki, sai Eliyakim ɗan Hilkiya sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci suka je wurinsu.
19 And Rabsaces seide to hem, Speke ye to Ezechie, The grete kyng, the kyng of Assiriens, seith these thingis, What is this trist, in which thou enforsist?
Jagoran dogarawan sarkin Assuriya ya ce musu, “Ku ce wa Hezekiya, “‘Ga abin da babban sarkin Assuriya ya ce, da wa kake taƙama?
20 In hap thou hast take counsel, that thou woldist make thee redi to batel. In whom tristist thou, that thou be hardi to rebelle?
Ka ce kana da dabara da ƙarfin soji, amma bagu kawai kake yi. Da wa ka dogara har da za ka yi mini tawaye?
21 Whethir thou hopist in a `staf of rehed and brokun, Egipt, on which, if a man lenith, it schal be brokun, and schal entre in to hys hond, and schal peerse it? So is Farao, kyng of Egipt, to alle men that tristen on hym.
Na sani kana dogara da Masar, wadda take kamar karar masara, wadda in ka jingina a kai, za tă karye tă soki hannunka. Haka Fir’auna sarkin Masar yake ga dukan wanda ya dogara da shi.
22 That if thou seist to me, We han trist in `oure Lord God; whether this is not he, whos hiye thingis and auteris Ezechie took awei, and comaundide to Juda and to Jerusalem, Ye schulen worschipe bifor this auter in Jerusalem?
Sai ya ci gaba da cewa, in kuma ka ce mini “Muna dogara ga Ubangiji Allahnmu ne,” ba masujadansa da bagadansa ne Hezekiya ya ciccire, yana ce wa Urushalima da Yahuda, “Dole ku yi sujada a gaban wannan bagade a Urushalima”?
23 Now therfor passe ye to my lord, the kyng of Assiriens, and Y schal yyue to you twei thousynde of horsis, and se ye, whether ye moun haue rideris of `tho horsis?
“‘Yanzu, ka zo ku shirya da shugabana, sarkin Assuriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu, in za ka sami mahayansu!
24 And hou moun ye withstonde bifor o prince of the leste seruauntis of my lord? Whether thou hast trist in Egipt, for charis and knyytis?
Yaya za ka yi tsayayya da mafi ƙanƙantan hafsan shugabana, ko da kana dogara da Masar don kekunan yaƙi da mahaya dawakai?
25 Whether Y stiede with outen `Goddis wille to this place, that Y schulde distrie it? `The Lord seide to me, `Stie thou to this lond, and distrie thou it.
Ban da haka ma, kana gani cewa na zo in hallaka wannan wuri ne ba tare da na ji daga Ubangiji ba? Ubangiji da kansa ne ya ce da ni in kawo wa wannan ƙasa hari in hallaka ta.’”
26 Forsothe Eliachym, sone of Elchie, and Sobna, and Joahe, seiden to Rabsaces, We preien, that thou speke bi the langage of Sirie to vs, thi seruauntis; for we vndirstondun this langage; and that thou speke not to vs bi the langage of Juwis, while the puple herith, which is on the wal.
Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, da Shebna, da Yowa suka ce wa jagoran dakarun, “Muna roƙonka ka yi wa bayinka magana da harshen Arameyik da yake muna ji. Kada ka yi mana magana da Yahudanci domin kada mutanen da suke bisa katanga su ji!”
27 And Rabsaces answeride, `and seide, Whethir my lord sente me to thi lord and to thee, that Y schulde speke these wordis, and not rather to the men `that sitten on the wal, that thei ete her toordis, and drynke her pisse with you?
Amma shugaban sojojin ya ce, “Ai, ba gare ku da sarkinku kaɗai ne shugabana ya aike ni ba. Amma har ga mutanen da suke zaune a kan katangar birnin, waɗanda za su ci kashinsu, su sha fitsarinsu!”
28 Therfor Rabsaces stood, and criede with greet vois bi langage of Jewis, and seide, Here ye the wordis of the greet kyng, the kyng of Assiriens.
Sai shugaban sojojin ya yi kira da Yahudanci ya ce, “Ku ji muryar babban sarki, sarkin Assuriya!
29 The kyng seith these thingis, Ezechie disceyue not you, for he may not delyuere you fro myn hond;
Ga abin da sarki ya faɗa; kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku. Ba zai iya cetonku daga hannuna ba.
30 nether yyue he trist to you on the Lord, and seie, The Lord delyuerynge schal delyuere vs, and this citee shal not be bitakun in the hond of the kyng of Assiriens;
Kada ku yarda Hezekiya yă rinjaye ku cewa ku dogara ga Allah, sa’ad da ya ce da ku, ‘Ba shakka Ubangiji zai cece mu; yana ce da ku birnin nan ba zai faɗa a hannun sarkin Assuriya ba.’
31 nyle ye here Ezechie. For the kyng of Assiriens seith these thingis, Do ye with me that, that is profitable to you, and go ye out to me; and eche man schal ete of his vyner, and of his fige tree, and ye schulen drynke watris of youre cisternes,
“Kada ku saurari Hezekiya. Ga abin da sarkin Assuriya ya ce, ku shirya zaman lafiya da ni, ku fito zuwa wurina. Kowane ɗayanku kuwa zai ci’ya’yan inabinsa da’ya’yan ɓaurensa, yă kuma sha ruwa daga randarsa,
32 til Y come, and translate you in to a lond which is lijk youre lond, in to a fruytful lond, and plenteuouse of wyn, a lond of breed, and of vineris, a lond of olyue trees, and of oile, and of hony; and ye schulen lyue, and ye schulen not die. Nyle ye here Ezechie, that disseyueth you, and seith, The Lord schal delyuere yow.
har lokacin da zan zo in kwashe ku, in kai ku wata ƙasa mai kama da taku, ƙasa mai yalwar hatsi, da ruwan inabi, da abinci, da gonakin inabi, da itatuwan zaitun, da zuma, don ku rayu, kada ku mutu! “Kada ku saurari Hezekiya, don karya yake muku, sa’ad da ya ce, ‘Ubangiji zai cece mu.’
33 Whether the goddis of hethene men delyueriden her lond fro the hond of the kyng of Assiriens?
Akwai allahn wata al’ummar da ya taɓa ceton ƙasarsa daga hannun sarkin Assuriya?
34 Where is god of Emath, and of Arphat? Where is god of Sapharuaym, of Ana, and of Aua? Whether thei delyueriden Samarie fro myn hond?
Ina allolin Hamat da na Arfad? Ina allolin Sefarfayim, da na Hena, da na Iffa? Sun cece Samariya daga hannuna?
35 For who ben thei in alle goddis of londis, that delyueriden her cuntrey fro myn hond, that the Lord may delyuere Jerusalem fro myn hoond?
Wanne a cikin dukan allolin ƙasashen nan ya iya ceton ƙasarsa da gare ni? Shugaban sojojin ya kuma ci gaba da cewa, ta yaya Ubangiji zai ceci Urushalima daga hannuna?”
36 Therfor the puple was stille, and answeride not ony thing to hym; for thei hadden take comaundement of the kyng, that thei schulden not answere to hym.
Amma mutane suka yi shiru ba su amsa masa ba, domin sarki ya umarta cewa, “Kada ku amsa masa.”
37 And Eliachym, sone of Elchie, the souereyn of the hows, and Sobna, scryuen, and Joahe, chaunceler, the sone of Asaph, camen with to-rent clothis to Ezechie; and telden to hym the wordis of Rabsaces.
Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, sarkin fada, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf, marubuci, suka je wurin Hezekiya da tufafinsu a kece, suka faɗa masa abin da shugaban sojojin ya faɗa.

< 2 Kings 18 >