< 2 Kings 15 >

1 In the seuenthe and twentithe yeer of Jeroboam, king of Israel, Azarie, sone of Amasie, kyng of Juda, regnede;
A shekara ta ashirin da bakwai ta mulkin Yerobowam sarkin Isra’ila, Azariya ɗan Amaziya, sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 he was of sixtene yeer, whanne he bigan to regne, and he regnede two and fifti yeer in Jerusalem; the name of his modir was Jecelia of Jerusalem.
Yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya daga Urushalima.
3 And he dide that, that was plesaunt bifor the Lord, bi alle thingis which Amasie, his fadir, hadde do;
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
4 netheles he distriede not hiy thingis; yit the puple made sacrifice, and brente encense in hiye thingis.
Amma bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane kuwa suka yi ta yin hadaya da ƙona turare a can.
5 Forsothe the Lord smoot the kyng, and he was leprouse til in to the day of his deeth; and he dwellide in an hous freli bi hym silf. Sotheli Joathas, sone of the kyng, gouernde the palis, and demyde the puple of the lond.
Ubangiji ya sa wa sarki ciwon kuturta har mutuwarsa, ya kuma zauna a keɓe. Yotam ɗan sarki, shi ne ya gudanar da sha’anin fada, ya kuma shugabanci mutanen ƙasar.
6 Forsothe the residue of the wordis of Azarie, and alle thingis whiche he dide, whether these ben not writun in the book of wordis of daies of the kyngis of Juda?
Game da sauran ayyukan mulkin Azariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
7 And Azarie slepte with hise fadris; and thei birieden hym with hise eldre men in the citee of Dauid; and Joathas, his sone, regnede for hym.
Azariya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi kusa da su a Birnin Dawuda. Yotam ɗansa, kuma ya gāje shi.
8 In the eiyte and threttithe yeer of Azarie, kyng of Juda, Zacharie, sone of Jeroboam, regnede on Israel in Samarie sixe monethis.
A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Zakariya ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki wata shida.
9 And he dide that, that was yuel bifor the Lord, as his fadris diden; he departide not fro the synnes of Jeroboam, sone of Nabath, that made Israel to do synne.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi. Bai bar aikata zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila suka yi ba.
10 Forsothe Sellum, the sone of Jabes, conspiride ayens hym in Samarie; and Sellum smoot hym opynli, and killide hym, and regnede for hym.
Sai Shallum ɗan Yabesh ya ƙulla wa Zakariya maƙarƙashiya. Ya tasam masa a gaban jama’a, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
11 Sotheli the residue of the wordis of Zacharie, whethir these ben not writun in the book of wordis of daies of the kyngis of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Zakariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
12 Thilke is the word of the Lord, which he spak to Hieu, and seide, `Thi sones `til to the fourthe generacioun schulen sitte `of thee on the trone of Israel; and it was doon so.
Ta haka maganar Ubangiji da ya yi wa Yehu ta cika, wadda ya ce, “Zuriyarka za tă zauna a kursiyin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
13 Sellum, sone of Jabes, regnede in the nynthe and thritty yeer of Azarie, kyng of Juda; sotheli he regnyde o monethe in Samarie.
Shallum ɗan Yabesh ya zama sarki a shekara ta talatin da tara ta mulkin Uzziya sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki na wata ɗaya a Samariya.
14 And Manaheu, the sone of Gaddi, styede fro Thersa, and cam in to Samarie; and he smoot Sellum, sone of Jabes, in Samarie, and killide hym, and regnede for hym.
Sa’an nan Menahem ɗan Gadi ya gangara daga Tirza ya haura zuwa Samariya. Ya tasam wa Shallum ɗan Yabesh a Samariya, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
15 Sotheli the residue of wordis of Sellum, and his conspirasie, bi which he settide tresouns, whether these ben not writun in the book of wordis of daies of the kyngis of Israel.
Game da sauran ayyukan mulkin Shallum, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
16 Thanne Manaheu smoot Capham, and alle men that weren thereynne, and the termes therof fro Thersa, for thei nolden opyn to hym; and he killide alle wymmen therof with child, and karf hem.
A lokacin nan sai Menahem ya taso daga Tirza, ya kai wa Tifsa hari da kowa wanda yake a birnin da kewayenta, don sun ƙi su buɗe ƙofofinsu. Ya kori Tifsa daga aiki, ya kuma tsattsaga cikin dukan mata masu juna biyu.
17 In the nynthe and thrittithe yeer of Azarie, kyng of Juda, Manaheu, sone of Gaddi, regnede on Israel ten yeer in Samarie.
A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Menahem ɗan Gadi ya zama sarkin Isra’ila, ya yi mulki a Samariya shekara goma.
18 And he dide that, that was yuel bifor the Lord; he departide not fro the synnes of Jeroboam, sone of Nabath, that made Israel to do synne.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. A duk tsawon mulkinsa, bai rabu da zunuban da Yerobowam ɗan Nebat ya sa Isra’ila suka aikata ba.
19 In alle the daies of hym Phul, the kyng of Assiries, cam in to Thersa. And Manaheu yaf to Phul a thousynde talentis of siluer, that he schulde be to hym in to help, and schulde make stidefast his rewme;
Sai Ful sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar hari, Menahem kuwa ya ba shi talenti dubu na azurfa don yă sami goyon bayansa, yă kuma ƙarfafa kahuwa mulkin.
20 and Manaheu settide taliage of siluer on Israel to alle myyti men and riche, that he schulde yyue to the kyng of Assiries; he settide fifti siclis of siluer bi alle men; and the king of Assiries turnede ayen, and dwellide not in Thersa.
Menahem ya tara kuɗin ne ta hanyar haraji a Isra’ila inda ya sa kowane attajiri ya ba da shekel hamsin don a ba sarkin Assuriya. Sa’an nan sarkin Assuriya ya janye, bai ƙara kasance a ƙasar ba.
21 Forsothe the residue of wordis of Manaheu, and alle thingis whiche he dide, whether these ben not wrytun in the book of wordis of daies of the kyngis of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Menahem, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
22 And Manaheu slepte with hise fadris; and Phaceia, his sone, regnyde for hym.
Menahem ya huta tare da kakanninsa. Fekahiya ɗansa kuma ya gāje shi.
23 In the fiftithe yeer of Azarie, kyng of Juda, Phaceia, sone of Manaheu, regnede on Israel in Samarie twei yeer.
A shekara ta hamsin ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Fekahiya ɗan Menahem ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekara biyu.
24 And he dide that, that was yuel bifor the Lord; he departide not fro the synnes of Jeroboam, sone of Nabath, that made Israel to do synne.
Fekahiya ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat wanda ya sa Isra’ila ya aikata ba.
25 Forsothe Phacee, sone of Romelie, duyk of his oost, conspiride ayens hym, and smoot hym in Samarie, in the tour of the kyngis hous, bisidis Argob, and bisidis Arib; `and he smoot hym with fifti men of the sones of Galaditis; and Phacee killide hym, and regnede for hym.
Ɗaya daga cikin manyan fadawansa, Feka ɗan Remaliya, ya ƙulla masa maƙarƙashiya. Ɗauke da mutanen Gileyad hamsin, ya kashe Fekahiya tare da Argob da kuma Ariye a fadan sarki a Samariya. Ta haka Feka ya kashe Fekahiya ya kuma gāje shi.
26 Sotheli the residue of wordis of Phacee, and alle thingis whiche he dide, whether these ben not writun in the book of wordis of daies of the kyngis of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Fekahiya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
27 In the two and fiftithe yeer of Azarie, kyng of Juda, Phasee, sone of Romelie, regnyde in Samarie twenti yeer.
A shekara ta hamsin da biyu ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Feka ɗan Remaliya ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya yi mulki shekara ashirin.
28 And he dide that, that was yuel bifor the Lord; and he departide not fro the synnes of Jeroboam, sone of Nabath, that made Israel to do synne.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai kauce wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta yi ba.
29 In the daies of Phacee, kyng of Israel, Teglat Phalasar, kyng of Assur, cam, and took Aion, and Aibel, the hows of Maacha, and Janoe, and Cedes, and Asor, and Galaad, and Galilee, and al the lond of Neptalym; and translatide hem in to Assiriens.
A zamanin Feka sarkin Isra’ila, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo ya kama Iyon, Abel-Bet-Ma’aka, Yanowa da Kedesh da kuma Hazor. Ya kame Gileyad da Galili, haɗe da dukan ƙasar Naftali, ya kuma kwashi mutanen zuwa Assuriya.
30 Forsothe Osee, sone of Hela, conspiride, and settide tresouns ayens Phasee, sone of Romelie, and smoot hym, and killide hym; and he regnyde for hym, in the twentithe yeer of Joathan, sone of Ozie.
Sa’an nan Hosheya ɗan Ela ya ƙulla wa Feka ɗan Remaliya maƙarƙashiya. Ya fāɗa masa ya kuma kashe shi, sa’an nan ya gāje shi a matsayin sarki a shekara ta shirin ta mulkin Yotam ɗan Uzziya.
31 Forsothe the residue of wordis of Phacee, and alle thingis whiche he dide, whether these ben not writun in the book of wordis of daies of the kyngis of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Feka da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
32 In the secounde yeer of Phacee, sone of Romelie, kyng of Israel, Joathan, sone of Ozie, kyng of Juda, regnyde;
A shekara ta biyu ta mulkin Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila, Yotam ɗan Uzziya sarkin Yahuda ya fara mulki.
33 he was of fyue and twenti yeer, whanne he bigan to regne, and he regnede sixtene yeer in Jerusalem; the name of his modir was Jerusa, the douyter of Sadoch.
Ya zama sarki yana da shekara ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Sunan mahaifiyarsa Yerusha,’yar Zadok.
34 And he dide that, that was plesaunt bifor the Lord; he wrouyte bi alle thingis, whiche his fadir Ozie hadde do;
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa Uzziya ya yi.
35 netheles he dide not awey hiy thingis; yit the puple made sacrifice, and brente incense in hiy thingis; he bildide the hiyeste yate of the hows of the Lord.
Duk da haka, bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙona turare a can. Yotam ya sāke gina Ƙofar Bisa ta haikalin Ubangiji.
36 Forsothe the residue of wordis of Joathan, and alle thingis whiche he dide, whether these ben not writun in the book of wordis of daies of the kyngis of Juda?
Game da sauran ayyukan mulkin Yotam da aikin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
37 In tho daies the Lord bigan to sende in to Juda Rasyn, the kyng of Sirie, and Phacee, the sone of Romelie.
(A kwanakin nan Ubangiji ya fara aikan Rezin sarkin Aram da Feka ɗan Remaliya, su yi gāba da Yahuda.)
38 And Joathan slepte with hise fadris, and was biried with hem in the citee of Dauid, his fadir; and Achaz, his sone, regnyde for hym.
Yotam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda, birnin mahaifinsa. Ahaz ɗansa kuma ya gāje shi.

< 2 Kings 15 >