< 2 Chronicles 33 >

1 Manasses was of twelue yeer, whanne he bygan to regne, and he regnyde in Jerusalem fyue and fifti yeer.
Manasse yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyar.
2 Forsothe he dide yuel bifor the Lord bi abhomynaciouns of hethene men, whiche the Lord destriede bifor the sones of Israel.
Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji, yana bin ayyukan banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
3 And he turnede, and restoride the hiye places, whiche Ezechie, his fadir, hadde destried. And he bildide auteris to Baalym, and made wodis, and worschipide al the knyythod of heuene, and heriede it.
Ya sāke gina masujadan kan tudun da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe; ya tā da bagadan Ba’al, ya kuma gina ginshiƙan Ashera. Ya rusuna wa dukan rundunonin taurari, ya kuma yi musu sujada.
4 And he bildide auteris in the hows of the Lord, of which the Lord hadde seid, My name schal be in Jerusalem with outen ende.
Ya gina bagadai cikin haikalin Ubangiji, waɗanda Ubangiji ya ce, “Sunana zai kasance cikin Urushalima har abada.”
5 Sotheli he bildide tho auteris to al the knyythod of heuene in the twei large places of the hows of the Lord.
Cikin filayen haikalin Ubangiji, ya gina bagadai ga dukan rundunonin taurari.
6 And he made hise sones to passe thorouy the fier in the valei of Beennon; he kepte dremes; he suede fals diuynyng bi chiteryng of briddis; he seruyde witche craftis; he hadde with hym astronomyeris and enchaunteris, `ethir trigetours, that disseyuen mennus wittis, and he wrouyte many yuelis bifor the Lord to terre hym to wraththe.
Ya miƙa’ya’yansa maza hadaya a wuta cikin Kwarin Ben Hinnom, ya yi bokanci, ya yi duba, ya kuma yi maitanci, ya nemi shawarar mabiya da masu ruhohi. Ya yi abin da yake mugu ƙwarai a gaban Ubangiji, yana tsokanarsa yă yi fushi.
7 Also he settide a grauun signe and a yotun signe in the hows of the Lord, of which hows God spak to Dauid, and to Salomon, his sone, and seide, Y schal sette my name with outen ende in this hows and in Jerusalem, which Y chees of alle the lynagis of Israel;
Ya ɗauki siffar da aka sassaƙa wadda ya yi, ya sa ta a cikin haikalin Allah, wanda Allah ya ce wa Dawuda da kuma ɗansa Solomon, “Cikin wannan haikali da kuma cikin Urushalima, wanda na zaɓa daga cikin kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
8 and Y schal not make the foot of Israel to moue fro the lond which Y yaf to her fadris, so oneli if thei kepen to do tho thingis whiche Y comaundide to hem, and al the lawe, and cerymonyes, and domes, bi the hond of Moises.
Ba zan ƙara bari ƙafafun Isra’ilawa su bar ƙasar da na ba wa kakanninku ba, in dai suka yi hankali ga yin kome da na umarce su game da duka dokoki, ƙa’idodi da kuma farillai da na bayar ta wurin Musa.”
9 Therfor Manasses disseyuede Juda, and the dwelleris of Jerusalem, that thei diden yuel, more than alle hethene men, whiche the Lord hadde distriede fro the face of the sones of Israel.
Amma Manasse ya sa Yahuda da mutanen Urushalima suka kauce, har suka aikata mugunta fiye da al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
10 And the Lord spak to hym, and to his puple; and thei nolden take heed.
Ubangiji ya yi magana da Manasse da mutanensa, amma ba su kula ba.
11 Therfor the Lord brouyte on hem the princes of the oost of the kyng of Assiriens; and thei token Manasses, and bounden hym with chaynes, and stockis, and ledden hym in to Babiloyne.
Saboda haka Ubangiji ya kawo manyan hafsoshin mayaƙan sarkin Assuriya a kansu, waɗanda suka ɗauki Manasse a matsayi ɗan kurkuku, suka sa ƙugiya a hancinsa, suka daure shi da sarƙoƙin tagulla suka kuma kai shi Babilon.
12 And aftir that he was angwischid, he preiede `his Lord God, and dide penaunce gretli bifor the God of hise fadris.
Cikin wahalarsa ya nemi tagomashin Ubangiji Allahnsa ya kuma ƙasƙantar da kansa sosai a gaban Allah na kakanninsa.
13 And he preiede God, and bisechide ententifli; and God herde his preier, and brouyte hym ayen `in to Jerusalem in to his rewme; and Manasses knew, that the Lord hym silf is God.
Da ya yi addu’a gare shi, sai Ubangiji ya taɓu da tubansa, ya kuma saurari roƙonsa; saboda haka ya dawo da shi Urushalima da kuma zuwa mulkinsa. Sa’an nan Manasse ya san cewa Ubangiji shi ne Allah.
14 Aftir these thingis he bildide the wal with out the citee of Dauid, at the west of Gion, in the valei, fro the entryng of the yate of fischis, bi cumpas `til to Ophel; and he reiside it gretli; and he ordeynede princes of the oost in alle the stronge citees of Juda.
Daga baya ya sāke gina katangar waje na Birnin Dawuda, yamma da maɓulɓular Gihon a cikin kwari, har zuwa mashigin Ƙofar Kifi, ya kuma kewaye tudun Ofel; ya yi ta da tsayi sosai. Ya sa hafsoshin mayaƙa cikin dukan biranen katanga a Yahuda.
15 And he dide awei alien goddis and symylacris fro the hows of the Lord; and he dide awei the auteris, whiche he hadde maad in the hil of the hows of the Lord, and in Jerusalem, and he castide awei alle with out the citee.
Ya fid da baƙin alloli, ya kuma fid da siffofi daga haikalin Ubangiji, haka ma dukan bagadan da ya gina a kan tudun haikali da kuma cikin Urushalima, ya zubar da su a bayan birni.
16 Certis he restoride the auter of the Lord, and offride theronne slayn sacrifices, and pesible sacrifices, and preisyng; and he comaundide Juda to serue the Lord God of Israel.
Sa’an nan ya gyara bagaden Ubangiji ya kuma miƙa hadayun salama da kuma hadayun godiya a bagaden, ya kuma faɗa wa Yahuda su bauta wa Ubangiji, Allah na Isra’ila.
17 Netheles the puple offride yit in hiy places to `her Lord God.
Mutane dai suka ci gaba da miƙa hadayu a masujadai kan tudu, amma wa Ubangiji Allahnsu kaɗai.
18 Forsothe the residue of dedis of Manasses, and his bisechyng to `his Lord God, and the wordis of profetis, that spaken to hym in the name of the Lord God of Israel, ben conteyned in the wordis of the kyngis of Israel.
Sauran ayyukan mulkin Manasse, haɗe da addu’arsa ga Allahnsa da kuma kalmomin da mai duba ya yi masa cikin sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, suna a rubuce cikin tarihin sarakunan Isra’ila.
19 And his preier, and the heryng, and alle synnes, and dispisyng, also the places in whiche he bildide hiy thingis, and made wodis and ymagis, bifor that he dide penaunce, ben writun in the bokis of Ozai.
Addu’arsa da yadda Allah ya taɓu ta wurin tubansa, da kuma dukan zunubansa da rashin biyayyarsa, da wuraren da ya gina masujadan kan tudu ya kuma kafa ginshiƙan Ashera da gumaka kafin ya ƙasƙantar da kansa, duka suna a rubuce cikin tarihin mai duba.
20 Forsothe Manasses slepte with hise fadris, and thei birieden hym in his hows; and Amon, his sone, regnyde for hym.
Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a fadansa. Sai Amon ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
21 Amon was of two and twenti yeer, whanne he bigan to regne; and he regnyde twei yeer in Jerusalem.
Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki a Urushalima shekara biyu.
22 And he dide yuel in the siyt of the Lord, as Manasses, his fadir, hadde do; and he offride, and seruyde to alle the idols, whiche Manasses hadde maad.
Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda mahaifinsa Manasse ya yi. Amon ya bauta ya kuma miƙa hadayu ga dukan gumakan da Manasse ya yi.
23 And he reuerenside not the face of the Lord, as Manasses, `his fadir, reuerenside; and he dide mych gretter trespassis.
Amma ba kamar mahaifinsa Manasse ba, bai ƙasƙantar da kansa a gaban Ubangiji ba; Amon ya ƙara laifinsa.
24 And whanne his seruauntis `hadden swore to gyder ayens hym, thei killiden hym in his hows.
Fadawan Amon sukan yi masa maƙarƙashiya, suka kashe shi a fadansa.
25 Sotheli the residue multitude of the puple, aftir that thei hadden slayn hem that `hadden slayn Amon, ordeyneden Josie, his sone, kyng for hym.
Sa’an nan mutanen ƙasar suka kashe dukan waɗanda suka yi wa Sarki Amon maƙarƙashiya, suka naɗa Yosiya ɗansa sarki a maimakonsa.

< 2 Chronicles 33 >