< 2 Chronicles 22 >
1 Forsothe the dwelleris of Jerusalem ordeyneden Ocozie, `his leeste sone, kyng for hym; for theues of Arabeis, that felden in to the castels, hadden slayn alle the grettere `in birthe, that weren bifor hym. And Ocozie, the sone of Joram, kyng of Juda, regnede.
Mutanen Urushalima suka mai da Ahaziya, autan Yehoram, sarki a madadinsa, da yake’yan hari, waɗanda suka zo tare da Larabawa cikin sansani, sun kashe dukan manyan’ya’yansa. Saboda haka Ahaziya ɗan Yeroham sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 Ocozie was of two and fourti yeer, whanne he bigan to regne, and he regnede o yeer in Jerusalem; the name of his modir was Athalia, the douyter of Amry.
Ahaziya yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara guda. Sunan mahaifiyarsa Ataliya ce, jikanyar Omri.
3 But he entride bi the weie of the hows of Achab; for his modir compellide hym to do yuele.
Shi ma ya yi tafiya a hanyoyin gidan Ahab, gama mahaifiyarsa ta ƙarfafa shi yă yi abin da ba shi da kyau.
4 Therfor he dide yuel in the siyt of the Lord, as the hows of Achab; for thei weren counselouris to hym in to his perischyng, aftir the deth of his fadir;
Ya aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, yadda gidan Ahab ta yi, gama bayan mutuwar mahaifinsa, sai gidan Ahab ta zama masu ba shi shawara, shawarar da ta kai shi ga lalacewa.
5 and he yede in the counsele of hem. And he yede with Joram, the sone of Achab, kyng of Israel, in to batel ayens Azahel, kyng of Sirye, in to Ramoth of Galaad. And men of Sirie woundiden Joram;
Ya kuma bi shawararsu sa’ad da ya tafi tare da Yoram ɗan Ahab sarkin Isra’ila don yă yaƙi Hazayel sarkin Aram a Ramot Gileyad. Sai Arameyawa suka yi wa Yoram rauni;
6 which turnede ayen for to be heelid in Jezrahel; for he hadde take many woundis in the forseid batel. Therfor Ocozie, kyng of Juda, the sone of Joram, yede doun to visite Joram, the sone of Achab, sijk in Jezrahel;
saboda haka ya dawo Yezireyel don yă yi jinyar raunin da suka yi masa a Rama cikin yaƙinsa da Hazayel sarkin Aram. Sa’an nan Azariya ɗan Yehoram sarkin Yahuda ya gangara zuwa Yezireyel don yă ga Yoram ɗan Ahab domin ya ji rauni.
7 for it was Goddis wille ayens Ocozie, that he cam to Joram. And whanne he was comun, he yede out with hym ayens Hieu, the sone of Namsi, whom God anoyntide, that he schulde do awey the hows of Achab.
Ta wurin ziyarar Yoram, Allah ya kawo fāɗuwar Ahaziya. Sa’ad da Ahaziya ya iso, ya tafi tare da Yoram domin yă sadu da Yehu ɗan Nimshi, wanda Ubangiji ya shafe don yă hallaka gidan Ahab.
8 Therfor whanne Hieu destriede the hows of Achab, he foond the princis of Juda, and the sones of the britheren of Ocozie, that `mynystriden to hym; and he killide hem.
Yayinda Yehu yake hukunta wa gidan Ahab, sai ya sami fadawan Yahuda da kuma’ya’yan dangin Ahaziya maza, waɗanda suke yi wa Ahaziya hidima, sai ya kashe su.
9 And he souyte thilke Ocozie, and cauyte him hid in Samarie, and after that he was brouyt to Hieu, Hieu killide hym; and thei birieden hym, for he was the sone of Josaphat, that hadde souyt God in al his herte. And noon hope was more, that ony of the generacioun of Ocozie schulde regne.
Ya kuma sa aka nemi Ahaziya. Aka kamo shi sa’ad da ya ɓuya a Samariya, suka kawo shi wurin Yehu, suka kashe shi, suka binne shi, gama sun ce, “Shi jikan Yehoshafat ne, wanda ya nemi Ubangiji da dukan zuciyarsa.” Ta haka babu wani a gidan Ahaziya da yake da ƙarfin cin gaba da mulkin.
10 For Athalia, his modir, siy, that hir sone was deed, and sche roos, and killide alle the kyngis generacioun of the hows of Joram.
Sa’ad da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga cewa ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta hallaka dukan’yan gidan sarautar Yahuda.
11 Forsothe Josabeth, the douyter of the kyng, took Joas, the sone of Ocozie, and stal hym fro the myddis of the sones of the kyng, whanne thei weren slayn; and sche hidde hym with his nurse in the closet of beddis. Forsothe Josabeth, that `hadde hid hym, was the douytir of kyng Joram, and wijf of Joiada, the bischop, and the sister of Ocozie; and therfor Athalia killide not hir.
Amma Yehosheba,’yar Sarki Yehoram, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya ta sace shi daga cikin’ya’yan gidan sarauta waɗanda ake shiri a kashe, ta sa shi tare da mai renonsa a ɗakin kwana. Haka fa, Yehosheba’yar sarki Yoram, matar Yehohiyada firist, ta yi, gama ita’yar’uwar Ahaziya ce, ta ɓoye Yowash don kada Ataliya tă kashe shi.
12 Therfor he was hid with hem in the hows of God sixe yeer, in whiche Athalia regnede on the lond.
Ya kasance a ɓoye tare da su a haikalin Allah shekara shida, yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.