< 2 Chronicles 21 >

1 Forsothe Josaphat slepte with hise fadris, and was biried with hem in the citee of Dauid; and Joram, his sone, regnede for hym.
Yehoshafat ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sai Yehoram ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
2 And he hadde britheren, the sones of Josaphat, Azarie, Jahiel, and Zacarie, Anany, and Mychael, and Saphatie; alle these weren the sones of Josaphat, kyng of Juda.
’Yan’uwan Yehoram,’ya’yan Yehoshafat maza su ne, Azariya, Yehiyel, Zakariya, Azariyahu, Mika’ilu da Shefatiya. Dukan waɗannan su ne’ya’yan Yehoshafat sarkin Isra’ila maza.
3 And her fadir yaf to hem many yiftis of gold and of siluer, and rentis, with strongeste citees in Juda; but he yaf the rewme to Joram, for he was the firste gendrid.
Mahaifinsu ya ba su kyautai masu yawa na azurfa da zinariya da kayayyaki masu daraja, tare da birane masu katanga a Yahuda, amma ya ba da mulki ga Yehoram domin shi ne ɗan farinsa.
4 Forsothe Joram roos on the rewme of his fadir; and whanne he hadde confermyd hym silf, he killide alle hise britheren bi swerd, and summe of the princes of Juda.
Sa’ad da Yehoram ya kafa kansa sosai a bisa mulkin mahaifinsa, sai ya kashe dukan’yan’uwansa da takobi tare da waɗansu sarakunan Isra’ila.
5 Joram was of two and thritti yeer, whanne he bigan to regne; and he regnede eiyte yeer in Jerusalem.
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas.
6 And he yede in the weies of the kyngis of Israel, as the hows of Achab hadde do, for the douyter of Achab was his wijf; and he dide yuel in the siyt of the Lord.
Ya yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, kamar yadda gidan Ahab ta yi, gama ya auri’yar Ahab. Ya aikata mugayen ayyuka a idon Ubangiji.
7 But the Lord nolde distrie the hows of Dauid, for the couenaunt which he `hadde maad with Dauid, and for he `hadde bihiyte to yyue to hym a lanterne, and to hise sones in al tyme.
Duk da haka, domin alkawarin da Ubangiji ya yi wa Dawuda, Ubangiji bai so yă hallaka gidan Dawuda ba. Ubangiji ya riga ya yi alkawari zai ci gaba da riƙe fitila domin Dawuda da zuriyarsa har abada.
8 In tho daies Edom rebellide, that it was not suget to Juda, and it ordeynede a kyng to it silf.
A zamanin Yehoram, Edom ya tayar wa Yahuda ya kuma naɗa sarkinsa.
9 And whanne Joram hadde passide with hise princes, and al the multitude of knyytis, that was with hym, he roos bi niyt, and smoot Edom, that cumpasside him, and alle hise duykis of his multitude of knyytis.
Saboda haka Yehoram ya tafi can tare da shugabannin sojojinsa da kuma dukan keken yaƙinsa. Mutanen Edom suka kewaye shi da shugabannin keken yaƙinsa, amma ya tashi ya fatattaki su da dare.
10 Netheles Edom rebellide, that it was not vndir the lordschip of Juda `til to this dai. In that tyme also Lobna yede awei, that it was not vndur the hond of hym; for he hadde forsake the Lord God of hise fadris.
Har yă zuwa yau Edom na tawaye a kan Yahuda. Libna ya yi tawaye a lokaci guda, domin Yehoram ya yashe Ubangiji Allah na kakanninsa.
11 Ferthermore he made hiye places in the citees of Juda, and made the dwelleris of Jerusalem to do fornycacioun, `that is, idolatrie, and Juda to breke the lawe.
Ya gina masujadan kan tudu a tuddan Yahuda, ya kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, ya sa Yahuda suka kauce.
12 Forsothe lettris weren brouyt to hym fro Elie, the prophete, in whiche it was writun, The Lord God of Dauid,
Yehoram ya sami wasiƙa daga Iliya annabi, wadda ta ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na kakanka Dawuda ya ce, ‘Ba ka yi tafiya a hanyoyin mahaifinka Yehoshafat ko Asa sarkin Yahuda ba.
13 thi fadir, seith these thingis, For thou `yedist not in the weies of Josaphat, thi fadir, and in the weie of Asa, kyng of Juda, but thou yedist bi the weie of the kyngis of Israel, and madist Juda and the dwelleris of Jerusalem to do fornicacioun, and suedist the fornicacioun of the hows of Achab; ferthermore and thou hast slayn thi britheren and the hows of thi fadir, `that weren betere than thou; lo!
Amma ka yi tafiya a hanyoyin sarakunan Isra’ila, ka sa Yahuda ya kauce, ka kuma sa mutanen Urushalima suka yi karuwanci, kamar yadda gidan Ahab ta yi. Ka kuma kashe’yan’uwanka, membobi gidan mahaifinka, mutanen da suka fi ka kirki.
14 the Lord schal smyte thee with a greet veniaunce, and thi puple, and thi sones, and wyues, and al thi catel;
Saboda haka a yanzu Ubangiji yana shirin ya bugi mutanenka,’ya’yanka maza, matanka da kuma kome da yake naka, da bugu mai ƙarfi.
15 sotheli thou schalt be sijk `with the worste sorewe of wombe, til thin entrailis go out litil and litil bi ech dai.
Kai kuma za ka kamu da ciwon hanji wanda zai yi ta cinka kowace rana sai har hanjinka sun fito.’”
16 Therfor the Lord reiside ayens Joram the spirit of Filisteis and Arabeis, that marchen with Ethiopiens; and thei stieden in to the lond of Juda,
Ubangiji ya sa Filistiyawa da Larabawa waɗanda suke zama kusa da Kushawa su yi gāba da Yehoram
17 and wastiden it, and thei token awei al the catel, that was foundun in the hows of the kyng, ferthermore and hise sones, and wyues; and no sone was left to hym, no but Joachaz, that was the leeste in birthe.
Suka yaƙi Yahuda, suka kai masa hari, suka kwashe dukan abubuwa masu kyau da suka samu a fadan sarki, tare da’ya’yansa maza da kuma matansa. Ba wanda aka bari, sai dai Ahaziya autansa.
18 And ouer alle these thingis the Lord smoot hym with vncurable sorewe of the wombe.
Bayan dukan wannan, sai Ubangiji ya sa wa Yehoram cuta marar warkarwa ta ciki.
19 And whanne dai cam aftir a dai, and the spaces of tymes weren turned aboute, the cours of twey yeer was fillid; and so he was wastid `bi long rot, so that he castide out also his entrailis, and so he wantide sorewe and liyf togidere, and he was deed in the werste sikenesse. And the puple dide not to hym seruyce of deed men bi the custom of brennyng, as it hadde do to hise grettere, `ether auncetris.
Cikin lokaci, a ƙarshen shekara ta biyu, sai hanjin cikinsa suka fito saboda cutar, ya kuma mutu cikin tsananin zafi. Mutanensa suka hura wuta don girmama shi, kamar yadda suka yi wa kakanninsa.
20 He was of two and thritti yeer whanne he bigan to regne, and he regnede eiyte yeer in Jerusalem, and he yede not riytfuli; and thei birieden hym in the citee of Dauid, netheles not in the sepulcre of kingis.
Yehoram yana da shekara talatin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara takwas. Ya mutu, ba ma wanda ya kula, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda, amma ba a makabartan sarakuna ba.

< 2 Chronicles 21 >