< 2 Chronicles 10 >

1 Forsothe Roboam yede forth in to Sichem; for al Israel came togidere thidur to make hym kyng.
Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan Isra’ilawa sun je can don su naɗa shi sarki.
2 And whanne Jeroboam, the sone of Nabath, that was in Egipt, `for he fledde thidur bifor Salomon, hadde herd this, he turnyde ayen anoon.
Da Yerobowam ɗan Nebat ya ji wannan (a lokacin yana a Masar, inda ya gudu daga Sarki Solomon ya tafi), sai ya dawo daga Masar.
3 And thei clepiden hym, and he cam with al Israel, and thei spaken to Roboam, and seiden,
Saboda haka suka aika a zo da Yerobowam, sai shi da dukan Isra’ila suka je wurin Rehobowam suka ce masa.
4 Thi fadir oppresside vs with ful hard yok; comaunde thou liytere thingis than thi fader, that settide on vs a greuouse seruage; and releese thou a litil of `the birthun, that we serue thee. And he seide,
“Mahaifinka ya sa mana kaya masu nauyi a kanmu, amma yanzu ka sauƙaƙa mana aiki mai zafin nan da kuma kaya masu nauyin da ya sa a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
5 After thre daies turne ye ayen to me. And whanne the puple was goon, he took counsel with elde men,
Rehobowam ya amsa, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.” Saboda haka mutanen suka watse.
6 that stoden bifor his fadir Salomon, while he lyuyde yit, and seide, What counsel yyuen ye, that Y answere to the puple?
Sai Sarki Rehobowam ya nemi shawarar dattawan da suka yi wa mahaifinsa Solomon hidima a lokacin da yake da rai, ya tambaye suya ce, “Wace shawara za ku ba ni don in amsa wa waɗannan mutane?”
7 And thei seiden to hym, If thou plesist this puple, and makist hem softe bi meke wordis, thei schulen serue thee in al tyme.
Suka amsa suka ce, “In za ka ji tausayi waɗannan mutane ka kuma gamshe su, ka kuma ba su amsar da ta dace, kullum za su zama bayinka.”
8 And he forsook the counsel of elde men, and bigan to trete with yonge men, that weren nurischid with hym, and weren in his cumpenye.
Amma Rehobowam ya ƙi shawarar da dattawa suka ba shi ya kuma nemi shawarar matasan da suka yi girma tare, suke kuma yin masa hidima.
9 And he seide to hem, What semeth to you? ether what owe Y answere to this puple, that seide to me, Releese thou the yok, which thi fadir puttide on vs?
Ya tambaye su ya ce, “Mece ce shawararku? Yaya zan amsa wa waɗannan mutanen da suke ce mini, ‘Ka sauƙaƙa nauyin da mahaifinka ya sa a kanmu’?”
10 And thei answeriden, as yonge men and nurschyd with hym in delicis, and seiden, Thus thou schalt speke to the puple that seide to thee, Thi fadir made greuouse oure yok, releese thou; and thus thou schalt answere to hem, My leeste fyngur is gretter than the leendis of my fader;
Matasan da suka yi girma tare shi suka amsa, “Faɗa wa mutanen da suke ce maka, ‘Mahaifinka ya sa kaya masu nauyi a kanmu, amma ka sauƙaƙa nauyinmu.’ Ka faɗa musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun mahaifina kauri.
11 my fadir puttide on you a greuouse yok, and Y schal leie to a gretter birthun; my fadir beet you with scourgis, forsothe Y schal bete you with `scorpiouns, that is, hard knottid roopis.
Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; zan ma sa mafi nauyi. Mahaifina ya bulale ku da bulala; zan bulale ku da kunamai.’”
12 Therfor Jeroboam and al the puple cam to Roboam in the thridde dai, as he hadde comaundid to hem.
Bayan kwana uku sai Yerobowam da dukan mutane suka dawo wurin Rehobowam, yadda sarki ya ce, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.”
13 And `the kyng answeride harde thingis, after that he hadde forsake the counsel of the eldere men,
Sarki ya amsa musu da kakkausar murya. Ya ƙi shawarar dattawan,
14 and he spak bi the wille of the yonge men, My fadir puttide on you a greuouse yok, which Y schal make greuousere; my fadir beet you with scourgis, sotheli Y schal bete you with scorpiouns.
ya kuma bi shawarar matasan ya ce, “Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; zan ma sa mafi nauyi. Mahaifina ya bulale ku da bulala; zan bulale ku da kunamai.”
15 And he assentide not to the preieris of the puple; for it was the wille of God, that his word schulde be fillid, which he hadde spoke bi the hond of Ahie of Silo to Jeroboam, sone of Nabath.
Saboda haka sarki bai saurari mutane ba, gama wannan juyin al’amura daga Allah ne, don a cika maganar Ubangiji da ya yi ga Yerobowam ɗan Nebat ta wurin Ahiya mutumin Shilo.
16 Sotheli whanne the kyng seide hardere thingis, al the puple spak thus to hym, No part is to vs in Dauid, nether eritage in the sone of Isai; Israel, turne thou ayen in to thi tabernaclis, sotheli thou, Dauid, feede thin hows. And Israel yede in to hise tabernaclis.
Sa’ad da Isra’ila suka ga sarki ya ƙi yă saurare su, sai suka amsa wa sarki, suka ce, “Wanda rabo muke da shi a wurin Dawuda, wanda sashe muke da shi daga ɗan Yesse? Kowa yă koma tentinsa, ya Isra’ila! Ka lura da gidanka, ya Dawuda!” Saboda haka dukan Isra’ilawa suka tafi gida.
17 Forsothe Roboam regnede on the sones of Israel, that dwelliden in the citees of Juda.
Amma game da Isra’ilawan da suke zama a garuruwan Yahuda kuwa, Rehobowam ya ci gaba da yin mulki a bisansu.
18 And kyng Roboam sente Adhuram, that was souereyn ouer the tributis; and the sones of Israel stonyden hym, and he was deed. Certis kyng Roboam hastide to stie in to the chare, and fledde in to Jerusalem.
Sarki Rehobowam ya aiki Hadoram wanda yake lura da aikin dole, amma Isra’ilawa suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu. Sarki Rehobowam kuwa ya gaggauta ya shiga keken yaƙinsa ya gudu zuwa Urushalima.
19 And Israel yede awei fro the hows of Dauid `til to this dai. Forsothe it was doon, whanne al Israel hadde herd, that Jeroboam turnede ayen, thei senten, and clepiden hym, whanne the cumpeny was gaderid, and thei ordeyneden him king on al Israel; and no man, outakun the lynage of Juda aloone, suede `the hows of Dauid.
Ta haka Isra’ila ya kasance cikin tawaye a kan gidan Dawuda har yă zuwa wannan rana.

< 2 Chronicles 10 >