< 1 Samuel 7 >
1 Therfor men of Cariathiarym camen, and ledden ayen the arke of the Lord, and brouyten it in to the hows of Amynadab in Gabaa. Sotheli thei halewiden Eleazar his sone, that he schulde kepe the ark of the Lord.
Mutanen Kiriyat Yeyarim suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji. Suka kai a gidan Abinadab da ke kan tudu, suka keɓe Eleyazar ɗansa yă lura da akwatin alkawarin Ubangiji.
2 And it was doon, fro which dai `the arke of the Lord dwellide in Caryathiarym, daies weren multiplied; for the twentithe yeer was now, after that Samuel bigan to teche the puple; and al Israel restide aftir the Lord.
Akwatin Alkawarin ya daɗe a Kiriyat Yeyarim ya kai shekara ashirin cif. Sai dukan mutanen Isra’ila suka yi makoki suka nemi Ubangiji.
3 Forsothe Samuel spak to al the hows of Israel, and seide, If in al youre herte ye turnen ayen to the Lord, do ye awei alien goddis, Balym and Astaroth, fro the myddis of you; and make ye redi youre hertis to the Lord, and serue ye hym aloone; and he schal delyuere you fro the hond of Filisteis.
Saboda haka Sama’ila ya yi magana da dukan gidan Isra’ila ya ce, in har da zuciya ɗaya kuke juyowa ga Ubangiji sai ku raba kanku da baƙin alloli da gunkin nan Ashtarot, ku ba da kanku ga Ubangiji. Ku yi masa bauta shi kaɗai, zai kuɓutar da ku daga hannun Filistiyawa.
4 Therfor the sones of Israel diden awey Baalym and Astoroth, and serueden the Lord aloone.
Sai Isra’ilawa suka rabu da gumakan Ba’al da Ashtarot suka bauta wa Ubangiji kaɗai.
5 Forsothe Samuel seide, Gadere ye al Israel in to Masphat, that Y preie the Lord for you.
Sama’ila ya ce, “Ku tattara dukan Isra’ila a Mizfa, ni kuwa zan yi addu’a ga Ubangiji dominku.”
6 And thei camen togidere in to Masphat, and thei drowen watir, and shedden out in the `siyt of the Lord; and thei fastiden in that day, and seiden, Lord, we synneden to thee. And Samuel demyde the sones of Israel in Masphat.
Sa’ad da suka taru a Mizfa, suka kawo ruwa suka zuba a gaban Ubangiji. A wannan rana suka yi azumi suka tuba, suka ce, “Mun yi wa Ubangiji zunubi!” Sama’ila kuwa ya zauna a Mizfa ya yi mulkin Isra’ilawa.
7 And Filisteis herden that the sones of Israel weren gaderid in Masphat; and the princes of Filisteis stieden to Israel. And whanne the sones of Israel hadden herd this, thei dredden of the face of Filisteis.
Da Filistiyawa suka ji cewa Isra’ila sun taru a Mizfa, sai shugabanninsu suka zo don su yaƙe Isra’ila. Da Isra’ilawa suka ji labarin, sai suka tsorata saboda Filistiyawa.
8 And `thei seiden to Samuel, Ceesse thou not to crye for vs to oure Lord God, that he saue vs fro the `hoond of Filisteis.
Suka ce wa Sama’ila, “Kada ka fasa kai kukanmu ga Ubangiji Allahnmu saboda mu, don yă cece mu daga hannun Filistiyawa.”
9 Forsothe Samuel took o soukynge lomb, and offride that hool in to brent sacrifice to the Lord. And Samuel criede to the Lord for Israel; and the Lord herde hym.
Sama’ila ya kama ɗan rago ya miƙa shi ɗungum hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. Ya yi roƙo ga Ubangiji a madadin Isra’ila, Ubangiji kuwa ya amsa addu’arsa.
10 Forsothe it was doon, whanne Samuel offryde brent sacrifice, that Filisteis bigunnen batel ayens Israel. Sotheli the Lord thundride with greet thundur in that dai on Filisteis, and made hem aferd; and thei weren slayn of the sones of Israel.
Lokacin da Sama’ila yana miƙa hadaya ta ƙonawa, Filistiyawa suka matso kusa don su yi yaƙi da Isra’ila. A ranar Ubangiji ya sa babban tsawa ya ruɗar da Filistiyawa har suka gudu a gaban Isra’ilawa.
11 And the sones of Israel yeden out of Masphat, and pursueden Filisteis, and smytiden hem `til to the place that was vndur Bethachar.
Isra’ilawa suka fito a guje daga Mizfa suka fafari Filistiyawa suka yi ta karkashe su a hanya har kwarin Bet-Kar.
12 Forsothe Samuel took o stoon, and puttide it bitwixe Masphat, and bitwixe Sen; and he clepide the name of that place The stoon of help. And he seide, Hidir to the Lord helpide vs.
Sa’an nan Sama’ila ya ɗauki dutse ya kafa tsakanin Mizfa da Shen, ya sa masa suna, Ebenezer ma’ana, “Har zuwa wannan lokaci Ubangiji ya taimake mu.”
13 And Filisteis weren maad low, and addiden no more to come in to the termes of Israel. And so the `hond of the Lord was maad on Filisteis in alle the daies of Samuel.
Ta haka Isra’ilawa suka ci Filistiyawa. Daga ranan Filistiyawa ba su ƙara yin nasara a kan Isra’ila ba. Ubangiji ya yi gāba da Filistiyawa har ƙarshen zamanin Sama’ila.
14 And the citees whiche the Filisteis token fro Israel, weren yoldun to Israel, fro Accaron `til to Geth and `hise termes; and the Lord delyuerede Israel fro the hond of Filisteis; and pees was bitwixe Israel and Ammorrey.
Filistiyawa suka mayar wa Isra’ila da garuruwan da suka ƙwato, wato, daga Ekron zuwa Gat, dukan yankin ƙasarsu da yake ƙarƙashin ikon Filistiyawa. Aka kuma sami zaman lafiya tsakanin Isra’ilawa da Amoriyawa.
15 Also Samuel demyde Israel in alle the daies of his lijf, that is, `til to the ordeynyng `and confermyng of Saul;
Sama’ila kuwa ya ci gaba da mulkin Isra’ila dukan rayuwarsa.
16 and he yede bi `alle yeeris, and cumpasside Bethel, and Galgal, and Masphat, and he demyde Israel in the forseid places.
Shekara-shekara Sama’ila yakan fita rangadi zuwa Betel, da Gilgal da Mizfa inda yakan yi musu shari’a.
17 And he turnede ayen in to Ramatha, for his hows was there; and he demyde Israel there, and he bildide there also an auter to the Lord.
Amma yakan komo Rama inda gidansa yake, a nan yakan yi wa Isra’ila shari’a. A nan ne kuma ya gina wa Ubangiji bagade.