< 1 Samuel 6 >
1 Therfor the arke of the Lord was in the cuntrei of Filisteis bi seuene monethis;
Lokacin da akwatin alkawarin Ubangiji ya kai wata bakwai a ƙasar Filistiyawa.
2 and aftir these thingis Filisteis clepiden preestis and false dyuynours, and seiden, What schulen we do of the arke of God? Shewe ye to vs, hou we schulen sende it in to his place.
Filistiyawa suka kira firistoci da bokaye suka ce, “Me za mu yi da akwatin alkawarin Ubangiji? Ku gaya mana yadda za mu komar da shi inda ya fito.”
3 Whiche seiden, If ye senden ayen the arke of God of Israel, nyle ye delyuere it voide, but yelde ye to hym that, that ye owen for synne; and thanne ye schulen be heelid, and ye schulen wite, whi `his hond goith not awei fro you.
Suka ce, in za ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila kada ku komar da shi hannu wofi; amma ku tabbata kun aika da hadaya don laifi zuwa wurinsa. Sa’an nan za ku warke ku kuma san dalilin da ya sa bai cire hannunsa a kanku ba.
4 And thei seiden, What is it, that we owen to yelde to hym for trespas?
Filistiyawa suka ce, “Wace irin hadaya don laifi za mu aika masa?” Suka ce, “Marurai biyar na zinariya da ɓeraye biyar na zinariya bisa ga yawan sarakunan Filistiyawa. Saboda annoba iri ɗaya ce ta buga ku da shugabanninku.
5 And thei answeriden to hem, Bi the noumbre of prouynces of Filisteis ye schulen make fyue goldun ersis, and fyue goldun myis; for o veniaunce was to alle you and to youre `wise men, ether princes. And ye schulen make the licnesse of youre ersis, and the licnesse of myis that distriede youre lond; and ye schulen yyue glorie to God of Israel, if in hap he withdrawe his hond fro you, and fro youre goddis, and fro youre lond.
Ku yi siffofin marurai da na ɓeraye da suke hallaka gari, ku ba da girma ga Allah na Isra’ila. Wataƙila zai ɗauke hukuncinsa daga gare ku da allolinku da kuma ƙasarku.
6 Whi maken ye heuy youre hertis, as Egipt, and Farao `made heuy his herte? Whether not after that he was smytun, thanne he delyuerede hem, and thei yeden forth?
Me ya sa kun taurare kanku kamar yadda Masarawa da Fir’auna suka yi? Da ya ba su matsanancin wahala, ba su bar Isra’ilawa suka tafi hanyarsu ba?
7 Now therfor take ye, and make o newe wayn, and ioyne ye twei kien hauynge caluys, on whiche kyen no yok was put; and close ye her calues at hoome.
“Yanzu fa ku shirya sabon keken shanu da shanu biyu masu ba wa’ya’yansu nono, waɗanda ba a taɓa sa musu karkiya ba. Ku daure keken shanu wa shanun, amma ku tsare’yan maruƙansu a gida.
8 And ye schulen take the arke of the Lord, and ye schulen sette in the wayn; and ye schulen put in a panyere at the side therof the goldun vessels, whiche ye payeden to hym for trespas; and delyuere ye the arke, that it go.
Ku ɗauki wani akwati ku sa siffofin zinariyan nan a ciki, waɗanda za su zama kyautai na shafen laifi, ku ajiye kusa da Akwati na UBANGIJI. Bayan haka sai ku sa keken shanun da akwatin a hanya, ku bar shi yă tafi.
9 And ye schulen biholde, and sotheli if it stieth ayens Bethsames bi the weie of `hise coostis, `he dide to you this greet yuel; but if nay, we schulen wite `for his hond touchide not vs, but `if it bifelde bi hap.
Amma ku zuba ido ku ga in ya haura zuwa yankinsa, zuwa Bet-Shemesh, to, Ubangiji ne ya kawo mana babban masifar a kanmu. Amma in bai bi ta nan ba, za mu san cewa ba shi ne ya buge mu ba, tsautsayi ne kawai.”
10 Therfor thei diden in this manere; and thei token twei kien that yauen mylk to caluys, and ioyneden to the wayn; and thei closiden her caluys at hoome.
Suka yi haka. Suka ɗauki shanun tatsa guda biyu suka ɗaura musu keken shanu, suka tsare’yan maruƙansu a gida.
11 And thei puttiden the arke of God on the wayn, and `thei puttiden the panyere, that hadde the goldun myis, and the licnesse of ersis `on the wayn.
Suka aza akwatin alkawarin Ubangiji a bisa keken shanun tare da akwatin siffofin ɓerayen zinariya da siffofin maruran.
12 Sotheli the kien yeden streiytli bi the weie that ledith to Bethsames; and tho yeden in o weie goynge and lowynge, and bowiden not nether to the riyt side nether to the left side; but also the wise men of Filisteis sueden `til to the termes of Bethsames.
Sai shanun suka miƙe zuwa Bet-Shemesh. Suka bi hanya daidai, ba su juya dama ko hagu ba. Shugabannin Filistiyawa suka bi har zuwa iyakar ƙasar Bet-Shemesh.
13 Forsothe men of Bethsames repiden whete in the valey, and thei reisiden the iyen, and sien the arke, and thei weren ioyful, whanne thei hadden sien `the arke.
A lokacin kuwa mutanen Bet-Shemesh suna girbin alkamansu a kwari da suka ɗaga ido suka hangi akwatin alkawarin Ubangiji, sai suka yi farin ciki ganinsa.
14 And the wayn cam in to the feelde of Josue of Bethsames, and stood there. Forsothe a greet stoon was there; and thei kittiden `the trees of the wayn, and puttiden the kien `on tho trees, a brent sacrifice to the Lord.
Keken shanun ya zo filin Yoshuwa a Bet-Shemesh ya tsaya a gefen wani babban dutse. Mutanen suka faskare keken shanun suka miƙa shanun hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
15 Sotheli dekenes token doun the arke of God, and the panyere, that was bisidis it, where ynne the goldun vessels weren; and thei settiden on the greet stoon. Forsothe the men of Bethsames offriden brent sacrifices, and offriden slayn sacrifices in that dai `to the Lord.
Lawiyawa suka saukar da akwatin alkawarin Ubangiji tare da babban akwati mai siffofin zinariya na ɓeraye da marurai suka ajiye su a kan ƙaton dutse. A wannan rana mutanen Bet-Shemesh suka miƙa hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu ga Ubangiji.
16 And fyue princes of Filisteis sien, and turneden ayen in to Accoron in that dai.
Shugabanni biyar na Filistiyawan nan suka ga duk abin da ya faru, suka koma zuwa Ekron a ranar.
17 Sotheli these ben the goldun ersis, whiche the Filisteis yeldiden to the Lord for trespas; Azotus yeldide oon; Gaza yeldide oon; Ascolon yeldide oon; Geth yeldide oon; Accaron yeldide oon;
Waɗannan su ne siffofi marurai na zinariya waɗanda Filistiyawa suka aika domin miƙa hadaya don laifi ga Ubangiji, ɗaya domin Ashdod, ɗaya domin Gaza, ɗaya domin Ashkelon, ɗaya domin Gat, ɗaya kuma domin Ekron.
18 and Filisteis yeldiden golden myis bi the noumbre of `citees of Filisteis of fyue prouynces, fro a wallid citee `til to `a town that was with out wal, and `til to the greet Abel, `on which thei puttiden the arke of the Lord, that was there `til in that dai in the feeld of Josue of Bethsames.
Filistiyawa kuma suka aika da siffofin ɓeraye biyar na zinariya. Yawan ɓerayen sun yi daidai da yawan garuruwan sarakunan nan biyar na Filistiyawa. Garuruwan sun ƙunshi waɗanda aka gina katangar birni kewaye da su, da kuma ƙauyukansu. Babban dutsen da suka ajiye akwatin alkawarin Ubangiji, ya zama shaida har wa yau a filin Yoshuwa a Bet-Shemesh.
19 Forsothe the Lord smoot of the men of Bethsames, for thei hadden seyn the arke of the Lord, and he smoot of the puple seuenti men, and fifty thousynde of the porail. And the puple morenyde, for the Lord hadde smyte `the puple with greet veniaunce.
Amma Allah ya kashe waɗansu mutum saba’in na mutanen Bet-Shemesh domin sun leƙa cikin akwatin alkawarin Ubangiji. Mutane kuwa suka yi makoki domin Ubangiji ya hallaka mutane da yawa.
20 And men of Bethsames seiden, Who schal now stonde in the siyt of the Lord God of this hooli thing, and to whom schal it stie fro vs?
Mutanen Bet-Shemesh suka yi tambaya suka ce, wa zai iya tsaya a gaban Ubangiji Allah Mai Tsarki? Wurin wa akwatin alkawari zai je daga nan?
21 And thei senten messangeris to the dwelleris of Cariathiarym, and seiden, Filisteis han brouyt ayen the arke of the Lord; come ye doun, and lede it ayen to you.
Sai suka aiki manzanni zuwa Kiriyat Yeyarim suka ce, “Filistiyawa sun komo da akwatin alkawarin Ubangiji, ku zo ku ɗauka ku kai wajenku.”