< 1 Samuel 23 >
1 And thei telden to Dauid, and seiden, Lo! Filisteis fiyten ayens Seila, and rauyschen the corn floris.
Sa’ad da aka ce wa Dawuda, “Duba ga Filistiyawa suna yaƙi da mutanen Keyila, suna kwashe musu hatsi a masussukai.”
2 Therfor Dauid councelide the Lord, and seide, Whether Y schal go, and smyte Filisteis? And the Lord seide to Dauid, Go thou, and thou schalt smyte Filisteis, and thou schalt saue Seila.
Sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya ce, “In tafi in fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi?” Ubangiji kuwa ya ce masa, “Jeka ka yi yaƙi da Filistiyawa, ka ceci Keyila.”
3 And men, that weren with Dauid, seiden to him, Lo! we ben heere in Judee, and dredden; hou myche more, if we schulen go in to Seila ayens the cumpanyes of Filisteis.
Amma mutanen Dawuda suka ce masa, “Ga shi, a nan ma a Yahuda muna jin tsoro, balle mu tafi Keyila mu yi yaƙi da sojojin Filistiyawa!”
4 Therfor eft Dauid councelide the Lord; which answeride, and seide to Dauid, Rise thou, and go `in to Seila; for Y schal bitake Filisteis in thin hond.
Dawuda ya sāke nemi nufin Ubangiji, sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi ka gangara zuwa Keyila, gama zan ba da Filistiyawa a hannunka.”
5 Therfor Dauid yede, and hise men, in to Seila, and fauyt ayens Filisteis; and he droof awey her werk beestis, and smoot hem with greet wounde; and Dauid sauyde the dwelleris of Seila.
Sa’an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Keyila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kwashe musu shanunsu, suka jijji wa Filistiyawa ƙwarai, suka cece mutanen Keyila daga hannunsu.
6 Forsothe in that tyme, `wher ynne Abiathar, sone of Achymelech, fledde to Dauid in to Seile, he cam doun, and hadde with hym `ephoth, that is, the cloth of the hiyeste preest.
(Abiyatar ɗan Ahimelek ya zo da efod sa’ad da ya gudo zuwa wurin Dawuda a Keyila.)
7 Forsothe it was teld to Saul, that Dauid hadde come in to Seila; and Saul seide, The Lord hath take hym in to myn hondis, and he `is closid, and entride in to a citee, in which ben yatis and lockis.
Shawulu ya sami labari cewa Dawuda ya tafi Keyila, sai ya ce, “Allah ya bashe shi a hannuna, domin Dawuda ya kulle kansa ke nan da ya shiga birnin da yake da ƙofofin da ake kulle da ƙarafa.”
8 And Saul comaundide to al the puple, that it schulde go doun to batel in to Seila, and bisege Dauid and hise men.
Shawulu ya kira dukan sojojinsa don yaƙi, su gangaro zuwa Keyila su mamaye Dawuda da mutanensa.
9 And whanne Dauid perceyuede, that Saul made redi yuel priueli to hym, he seide to Abiathar, preest, Brynge hidur ephoth.
Da Dawuda ya ji labari Shawulu yana shirya hanyar da zai kashe shi, sai ya ce wa Abiyatar firist, “Kawo mini efod a nan.”
10 And Dauid seide, Lord God of Israel, thi seruaunt `herde fame, that Saul disposith to come to Seila, that he distrie the citee for me;
Dawuda ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bawanka ya sami labari cewa tabbatacce Shawulu yana shirin zuwa Keyila yă hallaka garin saboda ni.
11 if the men of Seila schulen bitake me in to hise hondis, and if Saul schal come doun, as thi seruaunt herde, thou Lord God of Israel schewe to thi seruaunt? And the Lord seide, He schal come doun.
Mutanen Keyila za su bashe ni a gare shi? Shawulu zai gangaro nan kamar yadda bawanka ya sami labari? Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka gaya wa bawanka.” Ubangiji ya ce, “Zai zo.”
12 And Dauid seide eft, Whether the men of Seila schulen bitake me, and the men that ben with me, in to the hondis of Saul? And the Lord seide, Thei schulen bitake, `that is, if thou dwellist in the citee, and Saul come thidur.
Dawuda ya sāke cewa, “Mutanen Keyila za su bashe ni da mutanena ga Shawulu?” Ubangiji ya ce, “Za su yi.”
13 Therfor Dauid roos, and hise men, as sixe hundrid; and thei yeden out of Seila, and wandriden vncerteyn hidur and thidur. And it was telde to Saul, that Dauid hadde fledde fro Seila, and was saued; wherfor Saul dissymylide to go out.
Saboda haka Dawuda da mutanensa wajen mutum ɗari shida suka bar Keyila, suka yi ta tafiya daga wannan wuri zuwa wancan. Sa’ad da aka gaya wa Shawulu cewa Dawuda ya tsere daga Keyila, sai ya fasa tafiya can.
14 Forsothe Dauid dwellide in the deseert, in strongeste places, and he dwellide in the hil of wildirnesse of Ziph, in a derk hil; netheles Saul souyte hym in alle daies, and the Lord bitook not hym in to the hondis of Saul.
Dawuda ya zauna a jeji cikin kogunan duwatsu da kuma tuddan jejin Zif. Kowace rana Shawulu ya yi ta neman Dawuda amma Allah bai bashe Dawuda a hannunsa ba.
15 And Dauid siy, that Saul yede out, that he schulde seke his lijf. Forsothe Dauid was in the deseert of Ziph, in a wode.
A lokacin da Dawuda yana zaune a Horesh cikin jejin Zif, ya sami labari cewa Shawulu ya fito don yă kashe shi.
16 And Jonathas, the sone of Saul, roos, and yede to Dauid in to the wode, and coumfortide hise hondis in God.
Yonatan ɗan Shawulu kuwa ya tafi wurin Dawuda a Horesh, ya ƙarfafa shi yă dogara ga Allah.
17 And he seide to Dauid, Drede thou not; for the hond of Saul my fadir schal not fynde thee, and thou schalt regne on Israel, and Y schal be the secounde to thee; but also Saul my father woot this.
Ya ce, “Kada ka ji tsoro, mahaifina Shawulu ba zai taɓa sa hannu a kanka ba. Za ka zama sarki a Isra’ila, ni kuma in zama na biyu gare ka. Kai, ko mahaifina Shawulu ma ya san da haka.”
18 Therfor euer eithir smoot boond of pees bifor the Lord. And Dauid dwellide in the wode; forsothe Jonathas turnede ayen in to his hows.
Su biyunsu kuwa suka ɗaura yarjejjeniya a gaban Ubangiji. Sai Yonatan ya koma gida amma Dawuda ya zauna Horesh.
19 Forsothe men of Ziph stieden to Saul in Gabaa, and seiden, Lo! whether not Dauid is hid at vs in the sikireste places of the wode, in the hille of Achille, which is at the riyt syde of deseert?
Zifawa suka tafi wurin Shawulu a Gibeya suka ce masa, “Ashe, ba Dawuda ne yake ɓuya a cikinmu a kogwannin duwatsu a Horesh a bisan tudun Hakila, kudu da Yeshimon ba?
20 Now therfor come thou doun, as thi soule desiride, that thou schuldist come doun; forsothe it schal be oure, that we bitake hym in to the hondis of the kyng.
Yanzu, ya sarki, ka gangaro, ka zo a duk lokacin da ka ga ya yi maka, ka zo mu kuma hakkinmu ne mu bashe shi a hannun sarki.”
21 And Saul seide, Blessid be ye of the Lord, for ye sorewiden `for my stide.
Shawulu ya ce, “Ubangiji ya yi muku albarka, gama kun damu da ni.
22 Therfor, Y preie, go ye, and make redi more diligentli, and do ye more curiousli ether intentifli, and biholde ye swiftly, where his foot is, ethir who siy hym there, where ye seiden; for he thenkith on me, that felli Y aspie hym.
Ku tafi ku ƙara shiri. Ku san inda yakan tafi, wane ne kuma ya gan shi a can. An gaya mini cewa shi mai wayo ne sosai.
23 Biholde ye, and se alle his hidyng places, in whiche he is hid, and turne ye ayen to me at a certeyn thing, that Y go with you; that if he closith hym silf yhe in to erthe, Y schal seke hym with alle the thousyndis of Juda.
Ku binciko duk wuraren da yakan ɓuya, sai ku dawo ku gaya mini tabbataccen labari. Sa’an nan zan tafi tare da ku in yana can. Zan nemi shi ko’ina cikin dukan kabilar Yahuda.”
24 And thei risiden, and yeden in to Ziph bifor Saul. Forsothe Dauid and hise men weren in the deseert of Maon, in the feldi places, at the riyt half of Jesymyth.
Sai suka tashi suka koma Zif, suka sha gaban Shawulu. Dawuda da mutanensa kuwa suna jejin Mawon cikin Araba, kudu da Yeshimon.
25 Therfor Saul yede and hise felowis to seke Dauid, and it was teld to Dauid; and anoon he yede doun to the stoon, and lyuyde in the deseert of Maon; and whanne Saul hadde herd this, he pursuede Dauid in the deseert of Maon.
Shawulu da mutanensa suka tafi neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya gangara cikin duwatsu ya zauna a cikin jejin Mawon. Sa’ad da Shawulu ya ji haka, sai ya tafi jejin Mawon yana fafaran Dawuda.
26 And Saul yede and hise men at the side of the hil `on o part; forsothe Dauid and hise men weren in the side of the hil on the tother part; sotheli Dauid dispeiride, that he myyte ascape fro the face of Saul. And so Saul and hise men cumpassiden bi the maner of a coroun Dauid and hise men, that thei schulden take hem.
Shawulu yana tafiya a gefe ɗaya na dutsen, Dawuda da mutanensa kuma suna a wancan gefe, suna hanzari su ɓace wa Shawulu. Sa’ad da Shawulu da sojojinsa suka kusa cimma Dawuda da mutanensa don su kama su,
27 And a messanger cam to Saul, and seide, Haste thou, and come, for Filisteis han spred hem silf on the lond.
sai wani manzo ya zo wurin Shawulu yana cewa, “Ka koma da sauri, Filistiyawa sun kawo wa ƙasar hari.”
28 Therfor Saul turnede ayen, and ceesside to pursue Dauid; and yede ayens the comyng of Filisteis. For this thing thei clepen that place the Stoon Departynge.
Shawulu kuwa ya janye daga fafaran Dawuda, ya tafi yă ƙara da Filistiyawa. Dalilin ke nan da ake kiran wannan wuri Sela Hammalekot, wato, dutsen tserewa.
29 Therfor Dauid stiede fro thennus, and dwellide in the sykireste places of Engaddi.
Dawuda kuwa ya haura daga can ya zauna a kogwannin duwatsun En Gedi.