< 1 Samuel 2 >
1 And Anna worschipide, and seide, Myn herte fulli ioiede in the Lord, and myn horn is reisid in my God; my mouth is alargid on myn enemyes, for Y was glad in thin helthe.
Sai Hannatu ta yi addu’a ta ce, “Zuciyata tana farin ciki a cikin Ubangiji; a cikin Ubangiji an sa ina jin daɗi ƙwarai. Na buɗe bakina na yi wa abokan gābana dariya. Kai! Ina murna domin ka cece ni!
2 Noon is hooli as the Lord is; `for noon other is, outakun thee, and noon is strong as oure God.
“Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji babu wani, in ban da kai; babu wani dutse kamar Allahnmu.
3 Nyle ye multiplie to speke hiye thingis, and haue glorie; elde thingis go awey fro youre mouth; for God is Lord of kunnyngis, and thouytis ben maad redi to hym.
“Ka daina maganganu na girman kai ka kuma daina faɗin kalmomin ɗaga kai; gama Ubangiji Allah ne masani daga gare shi kuma ana auna ayyuka.
4 The bouwe of strong men is ouercomun, and sijk men ben gird with strengthe.
“An kakkarya bakkuna masu yaƙi, amma su da ka raunana an ba su makaman ƙarfi.
5 Men fillid bifore settiden hem silf to hire for looues, and hungri men ben fillid; while the bareyn womman childide ful manye, and sche that hadde many sones, was sijke.
Waɗanda a dā suna da abinci sosai; yanzu suna ƙodago saboda abinci, masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa. Ita da take bakararriya, ta haifi’ya’ya bakwai amma ita da tana da’ya’ya da yawa, ta zama mai baƙin ciki.
6 The Lord sleeth, and quikeneth; he ledith forth to hellis, and bryngith ayen. (Sheol )
“Ubangiji ne ke kawo mutuwa, yă kuma rayar yana kai ga kabari, yă kuma tā da. (Sheol )
7 The Lord makith pore, and makith riche; he makith low, and reisith.
Ubangiji ne yakan aika da talauci da kuma dukiya; yakan ƙasƙantar yă kuma ɗaukaka.
8 He reisith a nedi man fro poudur, and `he reisith a pore man fro dryt, that he sitte with princes, and holde the seete of glorie; for the endis of erthe ben of the Lord, and he hath set the world on tho.
Yakan tā da matalauci daga ƙura, yă kuma ɗaga mai bukata daga tarin toka; yă zaunar da su tare da’ya’yan sarki; yă kuma sa su gāji mulki na ɗaukaka. “Harsashin duniya na Ubangiji ne; a bisansu ne ya kafa duniya.
9 He schal kepe `the feet of hise seyntis, and wickid men schulen be stille to gidere in derknessis; for a man schal not be maad strong in his owne strengthe.
Zai kiyaye ƙafafun masu tsarki, amma mugaye za su lalace cikin duhu. “Ba bisa ga ƙarfi mutum ba ne mutum ke nasara;
10 Aduersaries of the Lord schulen drede hym, and in heuenes he schal thundre on hem; the Lord schal deme the endis of erthe, and he schal yyue lordschip to his kyng, and he schal enhaunse the horn, `that is, power, of his Crist.
waɗanda suke gāba da Ubangiji za su hallaka. Zai yi musu tsawa daga sama, Ubangiji zai hukunta dukan duniya. “Zai ba wa sarkinsa ƙarfi, yă kuma ɗaukaka shafaffensa.”
11 And Helcana yede in to Ramatha, in to his hows; forsothe the child was seruaunt in the siyt of the Lord bifor the face of Ely the preest.
Sa’an nan, Elkana ya koma gida a Rama amma yaron ya yi hidima a gaban Ubangiji a ƙarƙashin Eli firist.
12 Forsothe the sones of Hely weren sones of Belial,
’Ya’yan Eli firist, mutane ne masu mugunta. Ba su ɗauki Ubangiji a bakin kome ba.
13 and knewen not the Lord, nether the office of preestis to the puple; but who euer hadde offrid sacrifice, the child of the preest cam, while the fleischis weren in sething, and he hadde a fleischhook with thre teeth in his hond;
Al’ada ce ga firistoci da mutane cewa in wani ya miƙa hadaya, yayinda nama yake kan wuta, bawan firist zai zo da babban cokali mai yatsu,
14 and he sente it in to the `grete vessel of stoon, ethir in to the caudrun, ethir in to the pot, ethir in to the panne; and what euer thing the fleischhook reiside, the preest took to hym silf; so thei diden to al Israel of men comynge in to Silo.
zai soka cokali mai yatsun a tukunyar, ko butar da ake dafan naman. Duk abin da cokali mai yatsun ya cako daga tukunyar, ya zama na firist. Haka aka yi ta yi wa Isra’ilawan da suka zo miƙa hadaya a Shilo.
15 Yhe bifor that `the sones of Hely brenten the ynnere fatnesse, the `child of the preest cam, and seyde to the offerere, Yyue `thou fleisch to me, that Y sethe to the preest; for Y schal not take of thee sodun fleisch, but raw.
Tun ma kafin a ƙona kitse, bawan firist yakan zo yă ce wa mutumin da yake miƙa hadaya, “Ka ba wa firist nama domin yă gasa, ba zai karɓi dafaffen nama daga wurinka ba, sai ɗanye.”
16 And `the offrere seide to hym, The ynnere fatnesse be brent first to day bi the custom, and take thou to thee hou myche euer thi soule desirith. Whiche answeride, and seide to hym, Nay, for thou schalt yyue now; ellis Y schal take bi violence.
In kuwa mutumin ya ce masa, “Bari kitse yă ƙone tukuna, sa’an nan ka ɗiba duk abin da kake so.” Sai bawan yă ce masa, “A’a, ka ba ni yanzu, in ka ƙi kuwa zan ɗiba ƙarfi da yaji.”
17 Therfor the synne of the children was ful greuouse bifor the Lord; for thei withdrowen men fro the `sacrifice of the Lord.
Wannan zunubin samarin ya yi muni ƙwarai a gaban Ubangiji, domin sun wulaƙanta hadayar Ubangiji, ƙwarai da gaske.
18 `Forsothe Samuel, a child gird with a lynnun clooth, mynystride bifor the face of the Lord.
Amma yaron nan Sama’ila, yana hidima a gaban Ubangiji yana sanye da efod na lilin.
19 And his moder made to hym a litil coote, which sche brouyte in daies ordeyned, and stiede with hir hosebonde, that he schulde offre a solempne offryng, and his auow.
Kowace shekara mahaifiyarsa takan ɗinka’yar taguwa ta kai masa sa’ad da ita da mijinta suka je miƙa hadaya ta shekara.
20 And Heli blesside Helcana and his wijf; and Heli seide `to hym, The Lord yelde to thee seed of this womman, for the yifte which thou hast youe to the Lord. And thei yeden in to her place.
Eli yakan sa wa Elkana da matarsa albarka, yă ce, Ubangiji yă ba ka waɗansu’ya’ya ta wurin matan nan, maimakon wanda ta roƙa daga Ubangiji, ta kuma ba da shi ga Ubangiji. Bayan haka sai su koma gida.
21 Therfor the Lord visitide Anna, and sche conseyuede, and childide thre sones and twei douytris. And the child Samuel was `magnyfied at the Lord.
Hannatu kuwa ta sami alfarma daga Ubangiji. Ta yi ciki. Ana cikin haka Sama’ila kuwa sai girma yake ta yi a gaban Ubangiji.
22 Forsothe Hely was ful eld, and he herde alle `thingis whiche hise sones diden in al Israel, and hou thei slepten with wymmen, that awaitiden at the dore of the tabernacle.
To, Eli kuwa ya tsufa ƙwarai, yana kuma jin labari duk abin da’ya’yansa suke yi wa dukan Isra’ila, da yadda suke lalata da matan da suke hidima a bakin ƙofar Tentin Sujada.
23 And he seide to hem, Whi doen ye siche thingis, the worste thingis whiche Y here of al the puple?
Saboda haka ya ce musu, “Don me kuke yin waɗannan abubuwa? Na sami labari daga wurin mutane a kan duk ayyukan muguntanku.
24 Nyle ye, my sones; it is not good fame, which Y here, that ye make the `puple of the Lord to do trespas.
A’a,’ya’yana ba labari mai kyau nake ji cikin mutanen Ubangiji ba.
25 If a man synneth ayens a man, God may be plesid to him; forsothe if a man synneth ayens the Lord, who schal preye for hym? And thei herden not the vois of her fadir, for God wolde sle hem.
In mutum ya yi wa wani laifi Allah yakan kāre shi; amma in mutum ya yi wa Ubangiji zunubi wa zai kāre shi?” Duk da haka,’ya’yansa ba su kula da gargaɗin mahaifinsu ba, domin nufin Ubangiji ne yă hallaka su.
26 Forsothe the child Samuel profitide, and encreessyde, and pleside bothe God and men.
Yaron nan Sama’ila ya dinga girma cikin kwarjini da cikin tagomashi a gaba Ubangiji da mutane.
27 Sotheli a man of God cam to Hely, and seide to hym, The Lord seith these thingis, Whether Y was not schewid apertli to the hows of thi fadir, whanne he was in Egipt, in the hows of Farao?
Wani mutum ya zo wurin Eli ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ashe ban bayana kaina sosai ga mahaifinka lokacin da yake a Masar a ƙarƙashin Fir’auna ba?
28 And Y chees hym of alle lynagis of Israel `in to preest to me, that he schulde stie to myn auter, and schulde brenne encense to me, and that he schulde bere bifor me preestis cloth; and Y yaf to `the hows of thi fadir alle thingis of the sacrifices of the sones of Israel.
Na zaɓi mahaifinka daga cikin dukan kabilar Isra’ila yă zama firist nawa don yă yi hidima a bagade, don yă ƙona turare mai ƙanshi, don kuma yă sanya doguwar riga a gabana. Na kuma ba wa iyalin mahaifinka dukan hadaya ta ƙonawa da Isra’ila suka miƙa.
29 Whi hast thou cast awey with the heele my sacrifice, and my yiftis, whiche Y comaundide to be offrid in the temple; and thou onouridst more thi sones than me, that ye eeten the principal partis of ech sacrifice of `Israel, my puple?
Don me kuke rena hadayata da sadakokina da na ƙayyade domin mazaunina? Don me kake girmama’ya’yanka fiye da ni ta wurin cinye sashe mafi kyau na kowane hadayar da mutanena Isra’ila suka miƙa?’
30 Therfor the Lord God of Israel seith these thingis, Y spekynge spak, that thin hows and `the hows of thi fadir schulde mynystre in my siyt til in to with outen ende; `now forsothe the Lord seith, Fer be this fro me; but who euere onourith me, Y schal glorifie hym; forsothe thei that dispisen me, schulen be vnnoble.
“Saboda haka Ubangiji Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na yi alkawari cewa gidanka da gidan mahaifinka za su yi mini hidima a gabana har abada.’ Amma, yanzu Allah ya ce, ba zai yiwu ba; waɗanda suke girmama ni; Ni ma zan girmama su. Amma waɗanda suke ƙasƙantar da ni, haka za a ƙasƙantar da su.
31 Lo! daies comen, and Y schal kitte awei thin arm, and the arm of the hows of thi fadir, that an eld man be not in thin hows.
Lokaci yana zuwa sa’ad da zan rage ƙarfinka da ƙarfin iyalin gidan mahaifinka. Domin kada a sāke samun tsohon mutum a zuriyarka.
32 And thou schalt se thin enemy in the temple, in alle prosperitees of Israel; and an eld man schal not be in thin hows in alle daies.
Za ka zama da ɓacin rai a mazaunina ko da yake za a yi wa Isra’ila alheri. A zuriyarka ba za a taɓa samun tsohon mutum ba.
33 Netheles Y schal not outerli take awei of thee a man fro myn auter, but that thin iyen faile, and thi soule faile; and greet part of thin hows schal die, whanne it schal come to mannus age.
Kowannenku da ban kashe daga hidima a bagadena ba, za a bar shi don yă cika idanunka da hawaye da kuma baƙin ciki, dukan sauran zuriyarka kuwa za su mutu a ƙuruciyarsu.
34 Forsothe this schal be signe, that schal come to thi twei sones Ophym and Fynees, bothe schulen die in o dai.
“‘Abin da kuma ya faru da’ya’yanka biyu Hofni da Finehas zai zama alama a gare ka; saboda mutuwarsu za tă zama a rana ɗaya.
35 And Y schal reise to me a feithful preest, that schal do bi myn herte and my soule; and Y schal bilde to hym a feithful hows, and he schal go bifore my Crist in alle daies.
Zan tayar wa kaina amintaccen firist wanda zai aikata abin da nake so yă yi, zan kuwa ba shi zuriya da koyaushe za su yi aiki a gaban zaɓaɓɓen sarkina.
36 Forsothe it schal come, that who euer dwellith in thin hows, he come that `me preie for him, and that he offre a peny of siluer, and a cake of breed, and seie, Y biseche, suffre thou me to o `part of the preest, that Y ete a mussel of breed.
Sa’an nan duk wanda ya rage a zuriyarka zai zo yă durƙusa a gabansa yă roƙi kuɗi da abinci, zai kuma roƙa a yardar masa yă taimaki firistoci da aiki domin yă sami abin da zai ci.’”