< 1 Samuel 13 >

1 Saul was a child of o yeer whanne he bigan to regne; forsothe he regnede on Israel twei yeer.
Shawulu yana da shekara talatin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarautar Isra’ila shekara arba’in da biyu.
2 And Saul chees to hym thre thousynde of Israel, and twei thousynde weren with Saul in Machynas, in the hil of Bethel; forsothe a thousynde weren with Jonathas in Gabaath of Beniamyn; sotheli he sente ayen the tother puple ech man in to `hise tabernaclis.
Sai ya zaɓi sojoji dubu uku daga jama’ar Isra’ila. Ya keɓe dubu biyu su kasance tare da shi a Mikmash da kuma a tuddan yankin Betel. Ya kuma bar dubu ɗaya tare da ɗansa Yonatan a Gibeya a yankin zuriyar Benyamin. Sauran sojojin kuwa Shawulu ya sallame su su koma gidajensu.
3 And Jonathas smoot the stacioun of Filisteis, that was in Gabaa. And whanne Filisteis hadden herd this, Saul sownede with a clarioun in al the lond, and seide, Ebreys here.
Yonatan ya kai wa Filistiyawa hari a Geba, sai Filistiyawa suka sami labarin. Sai Shawulu ya sa aka busa ƙaho ko’ina a ƙasar ya ce, “Bari Ibraniyawa su ji!”
4 And al Israel herde siche a fame, Saul smoot the stacioun of Filisteis; and Israel reiside hym silf ayens Filisteis; therfor the puple criede after Saul in Galgala.
Haka kuwa dukan Isra’ila suka ji labari cewa, “Shawulu ya kai hari a ƙasar Filistiyawa, yanzu Isra’ila ta zama abin ƙi ga Filistiyawa.” Aka kira mutane su haɗu da Shawulu a Gilgal.
5 And Filisteis weren gaderid to fiyte ayens Israel; `of Filisteis weren thretti thousynde of charis, and sixe thousynde of knyytis, and the tother comyn puple, as grauel `which is ful myche in the brynke of the see; and thei stieden, and settiden tentis in Machynas, at the eest of Bethauen.
Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra’ilawa. Suka fito da kekunan-dawakan yaƙi dubu talatin, da masu hawan dawakai dubu shida, da sojoji masu yawa kamar yashi a bakin teku. Suka tafi Mikmash a gabashin Bet-Awen, suka kafa sansani a can.
6 And whanne men of Israel hadden seyn this, that thei weren set in streiytnesse, for the puple was turmentid, thei hidden hem silf in dennes, and in priuey places, and in stonys, and in dychis, and in cisternes.
Sa’ad da Filistiyawa suka fāɗa wa Isra’ilawa da yaƙi mai tsanani, suka sa su cikin wani hali mai wuya, sai Isra’ilawa suka ɓuya a kogwanni, da ciyayi, da duwatsu, da ramummuka, da rijiyoyi.
7 Sotheli Ebreis passiden Jordan in to the lond of Gad and of Galaad. And whanne Saul was yit in Galgala, al the puple was aferd that suede hym.
Waɗansunsu ma suka haye Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Shawulu ya zauna Gilgal, dukan ƙungiyoyi sojojin da suke tare da shi suka yi rawan jiki don tsoro.
8 And seuene daies he abood Samuel bi couenaunt, and Samuel cam not in to Galgala; and the puple yede a wei fro Saul.
Ya jira har kwana bakwai bisa ga lokacin da Sama’ila ya bayar. Amma Sama’ila bai zo Gilgal ba, mutanen Shawulu suka fara watsewa.
9 Therfor Saul seide, Brynge ye to me brent sacrifice, and pesible sacrifices; and he offride brent sacrifice.
Sai ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.” Sai Shawulu ya miƙa hadaya ta ƙonawa.
10 And whanne he hadde endid offrynge brent sacrifice, lo! Samuel cam; and Saul yede out ayens hym, to greete Samuel.
Daidai yana gama miƙa hadaya ke nan sai Sama’ila ya iso. Shawulu kuma ya fito domin yă yi masa maraba.
11 And Samuel spak to hym, What hast thou do? Saul answeride, For Y siy that the puple yede awei fro me, and thou camest not bi the daies of couenaunt; certis Filisteis weren gaderid in Machynas;
Sama’ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Shawulu ya ce, “Sa’ad da na ga mutane suna watsewa, kai kuwa ba ka zo cikin lokaci ba, ga Filistiyawa kuma suna taruwa a Mikmash,
12 Y seide, Now Filisteis schulen come doun to me in to Galgala, and Y haue not plesyd the face of the Lord; Y was compellid bi nede, and Y offryde brent sacrifice to the Lord.
sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ga ni kuma ban riga na nemi nufin Ubangiji ba.’ Shi ya sa ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa.”
13 And Samuel seide to Saul, Thou hast do folili, and thou `keptist not the heestis of thi Lord God, whiche he comaundide to thee; and if thou haddist not do this thing, riyt now the Lord hadde maad redi thi rewme on Israel with outen ende;
Sama’ila ya ce, “Ka yi wauta da ba ka bi umarnin da Ubangiji Allahnka ya ba ka ba. Da ka yi haka da Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra’ila har abada.
14 but thi rewme schal not rise ferthere. The Lord hath souyt a man to hym silf after his herte; and the Lord comaundide to hym, that he schulde be duyk on his puple, for thou keptist not tho thingis whiche the Lord comaundide.
Amma yanzu, masarautarka ba za tă dawwama ba, Ubangiji ya riga ya sami wani wanda zuciyarsa ke ƙauna, ya naɗa shi shugaban mutanensa gama ba ka bi umarnin Ubangiji ba.”
15 Forsothe Samuel roos, and stiede fro Galgala in to Gabaa of Beniamyn; and the `residue puplis stieden after Saul ayens the puple which fouyten ayens hem; and thei camen fro Galgala in to Gabaa, in the hil of Beniamyn. And Saul noumbride the puple, that weren foundun with hym as sixe hundrid men.
Sama’ila ya tashi daga Gilgal ya tafi Gibeya a ƙasar Benyamin. Shawulu kuma ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, yawansu ya kai wajen mutum ɗari shida.
16 And Saul, and Jonathas his sone, and the puple that was foundun with hem, was in Gabaa of Beniamyn; forsothe Filisteis saten togidere in Machynas.
Shawulu da ɗansa Yonatan da mutanen da suke tare da shi suka zauna a Geba ta Benyamin. Sa’an nan Filistiyawa suka yi sansani a Mikmash.
17 And thre cumpanyes yeden out of the `castels of Filisteis to take prey; o cumpany yede ayens the weie of Effraym to the lond of Saul;
Rundunar mayaƙa uku suka fito daga sansani Filistiyawa. Ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal.
18 sothely an other cumpeny entride bi the weie of Bethoron; forsothe the thridde cumpenye turnede it silf to the weie of the terme in the lond of Sabaa; and that terme neiyeth to the valey of Seboym ayens the deseert.
Runduna guda kuma ta nufi Bet-Horon, ɗayan kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar Kwarin Ziboyim wajen jeji.
19 Forsothe `no smyyth of yrun was foundun in al the lond of Israel; for Filisteis `weren war, ether eschewiden, lest perauenture Ebreis maden a swerd ether a spere.
Ba a sami maƙeri ɗaya a dukan ƙasar Isra’ila ba domin Filistiyawa sun ce, “In ba haka ba Ibraniyawa za su ƙera wa kansu takuba ko māsu.”
20 Therfor al Israel yede doun to Filisteis, that ech man schulde scharpe his schar, and picoise, and ax, `and sarpe;
Saboda haka dukan Isra’ila sukan gangara zuwa wajen Filistiyawa domin su gyara bakin garemaninsu, da fartanansu, da gaturansu, da kuma laujunansu.
21 `and so alle egis weren bluntid `of scharris, and of picoisis, and of `forkis of thre teeth, and of axis, `til to a pricke to be amendid.
Duk lokacin da za su gyara bakin garmansu da fartanyarsu sai sun biya tsabar azurfa biyu. Haka ma idan za su gyara gatari ko bakunan abin korar shanun noma sai sun biya tsabar azurfa ɗaya.
22 And whanne the dai of batel cam, no swerd and spere was foundun in the hond of al the puple that was with Saul and Jonathas, outakun Saul, and Jonathas his sone.
A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Shawulu da Yonatan. Sai dai Shawulu da ɗansa Yonatan kaɗai.
23 Forsothe the stacioun of Filisteis yede out, that it schulde passe in to Machynas.
Ana nan sai sojojin Filistiyawa suka fita zuwa mashigin Mikmash.

< 1 Samuel 13 >