< 1 Kings 15 >
1 Therfor in the eiytenthe yeer of the rewme of Jeroboam, sone of Nabath, Abia regnede on Juda.
A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yerobowam ɗan Nebat, Abiyam ya zama sarkin Yahuda,
2 Thre yeer he regnede in Jerusalem; the name of his modir was Maacha, douyter of Abessalon.
ya kuma yi mulki a Urushalima shekara uku. Sunan mahaifiyarsa Ma’aka ne,’yar Abisalom.
3 And he yede in alle the synnes of his fadir, which he dide bifor hym; and his herte was not perfit with his Lord God, as the herte of Dauid, his fadir, `was perfit.
Shi ma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Zuciyarsa ba tă bi Ubangiji Allahnsa, kamar yadda zuciyar Dawuda kakansa ta yi ba.
4 But for Dauid his Lord God yaf to hym a lanterne in Jerusalem, that he schulde reise his sone after hym, and that he schulde stonde in Jerusalem;
Duk da haka, saboda Dawuda Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima ta wurin ta da wani da ya gāje shi, ta wurinsa kuma Urushalima ta yi ƙarfi.
5 for Dauid hadde do riytfulnesse in the iyen of the Lord, and hadde not bowid fro alle thingis whiche the Lord hadde comaundid to him, in alle the daies of his lijf, outakun the word of Urie Ethei.
Gama Dawuda ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, bai kuma fasa kiyaye wani daga umarnan Ubangiji ba dukan kwanakinsa, sai dai a batun Uriya mutumin Hitti.
6 Netheles batel was bitwix Abia and Jeroboam, in al the tyme of his lijf.
Aka yi yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam a duk kwanakin Abiya.
7 Sotheli the residue of wordis of Abia, and alle thinges whiche he dide, whether these ben not writun in the book of wordis of daies of the kyngys of Juda? And batel was bitwixe Abia and Jeroboam.
Game da sauran ayyukan mulkin Abiyam kuwa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. Aka yi yaƙi tsakanin Abiyam da Yerobowam.
8 And Abia slepte with his fadris; and thei birieden hym in the citee of Dauid; and Asa, his sone, regnede for hym.
Sai Abiyam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Asa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
9 Sotheli Asa, king of Jude, regnede in the twentithe yeer of Jeroboam, kyng of Israel;
A shekara ta ashirin ta Yerobowam sarkin Isra’ila, Asa ya zama sarkin Yahuda,
10 and Asa regnede oon and fourti yeer in Jerusalem. The name of his modir was Maacha, douyter of Abessalon.
ya yi mulki a Urushalima shekara arba’in da ɗaya. Sunan mahaifiya mahaifiyarsa, Ma’aka ne’yar Abisalom.
11 And Asa dide riytfulnesse in the siyt of the Lord, as Dauid, his fadir, dide;
Asa ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi.
12 and he took awey fro the loond men of wymmens condiciouns, and he purgide alle the filthis of idols, whiche his fadris maden.
Ya kori dukan maza karuwai na masujadai daga ƙasar, ya kuma yi waje da dukan gumakan da mahaifinsa ya yi.
13 Ferthermore and he remouyde Maacha, his modir, that sche schulde not be princesse in the solempne thingis of Priapus, and in his wode which sche hadde halewid; and he distriede the denne of hym, and he brak the foulest symylacre, and brente in the stronde of Cedron;
Ya tuɓe mahaifiya mahaifiyarsa Ma’aka daga matsayinta na mahaifiyar sarauniya, gama ta gina ƙazantaccen ginshiƙin Ashera. Asa ya yanke ginshiƙin, ya kuma ƙone shi a Kwarin Kidron.
14 sotheli he dide not awei hiy thingis; netheles the herte of Asa was perfit with hys Lord God, in alle hise daies.
Ko da yake bai cire masujadai da suke kan tuddai ba, zuciyar Asa ta kasance da aminci ɗungum ga Ubangiji dukan kwanakinsa.
15 And he brouyte in to the hous of the Lord tho thingis, whiche his fadir hadde halewid and auowid, siluer, and gold, and vessel.
Ya kawo azurfa da zinariya da kayayyakin da shi da mahaifinsa suka keɓe a haikalin Ubangiji.
16 Forsothe batel was bitwixe Asa and Baasa, kyng of Israel, in alle the daies of hem.
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
17 And Baasa, kyng of Israel, stiede in to Juda, and bildide Rama, that no man of the part of Aza, kyng of Juda, myyte go out, ether go yn.
Ba’asha sarkin Isra’ila ya haura, ya yi yaƙi da Yahuda, ya kuma gina Rama don yă hana wani daga fita ko shiga yankin Asa, sarkin Yahuda.
18 Therfor Asa took al the siluer and gold, that lefte in the tresouris of the hows of the Lord, and in the tresouris of the kyngis hows, and yaf it in to the hondis of hise seruauntis; and sente to Benadab, sone of Tabrennon, sone of Ozion, the kyng of Sirie, that dwellide in Damask, and seide,
Sai Asa ya ɗauki dukan azurfa da kuma zinariyar da suka rage a ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma nasa fadan, ya ba da su ga wani shugabansa, ya kuma aika da su zuwa ga Ben-Hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, sarkin Aram, wanda yake mulki a Damaskus.
19 Boond of pees is bitwixe me and thee, and bitwixe my fadir and thi fadir, and therfor Y sente to thee yiftis, gold, and siluer; and Y axe, that thou come, and make voide the boond of pees, which thou hast with Baasa, kyng of Israel, and that he go awey fro me.
Ya ce, “Bari yarjejjeniya ta kasance tsakanina da kai, kamar yadda ta kasance tsakanin mahaifina da mahaifinka. Duba, ina aika maka kyautai na azurfa da na zinariya. Yanzu fa sai ka janye yarjejjeniyarka da Ba’asha sarkin Isra’ila, don yă janye daga gare ni.”
20 Benadab assentide to kyng Asa, and sente the princes of his oost in to the citees of Israel; and thei smytiden Ahion, and Dan, and Abel, the hows of Maacha, and al Cenoroth, that is, al the lond of Neptalym.
Ben-Hadad ya yarda da maganar Sarki Asa, ya kuma aika shugabannin sojojin mayaƙansa ya yi yaƙi da garuruwan Isra’ila. Ya kame Iyon, Dan, Abel-Bet-Ma’aka da dukan Kinneret, haɗe da Naftali.
21 And whanne Baasa hadde herd this thing, he lefte to bilde Rama, and turnede ayen in to Thersa.
Da Ba’asha ya ji haka, sai ya daina ginin Rama, ya janye zuwa Tirza.
22 Forsothe kyng Asa sente message in to al Juda, and seide, No man be excusid. And thei token the stoonys of Rama, and the trees therof, bi whiche Baasa hadde bildid; and kyng Asa bildide of the same `stoonys and trees Gabaa of Beniamyn, and Maspha.
Sai Sarki Asa ya ba da umarni ga dukan Yahuda, kuma babu wanda aka ware, kowa yă taimaka a kwashe duwatsu da katakan da Ba’asha yake amfani da su daga Rama. Da duwatsu da katakan ne Sarki Asa ya gina Geba a Benyamin da kuma Mizfa.
23 Sotheli the residue of alle wordis of Asa, and of al his strengthe, and alle thingis whiche he dide, and the citees whiche he bildide, whether these ben not writun in the book of wordis of daies of kingis of Juda? Netheles Asa hadde ache in feet, in the tyme of his eelde.
Game da sauran ayyukan mulkin Asa, dukan nasarorinsa, dukan abin da ya yi, da kuma biranen da ya gina, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda. A tsufansa, sai ƙafafunsa suka kamu da cuta.
24 And Asa slepte with hise fadris, and he was biried with hem in the citee of Dauid, his fader; and Josophat, his sone, regnede for him.
Sai Asa ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a birnin kakansa Dawuda. Sai Yehoshafat ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
25 Forsothe Nadab, the sone of Jeroboam, regnede on Israel, in the secunde yeer of Asa, king of Juda; and he regnede on Israel two yeer.
Nadab ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a shekara ta biyu ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila shekara biyu.
26 And he dide that, that was yuel in the siyt of the Lord, and he yede in the weies of his fadir, and in the synnes of hym, in whiche he made Israel to do synne.
Ya yi mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin mahaifinsa da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.
27 Forsothe Baasa, the sone of Ahia, of the hows of Ysachar, settide tresoun to hym, and smoot him in Gebethon, which is a citee of Filisteis; sothely Nadab and al Israel bisegiden Gebethon.
Ba’asha ɗan Ahiya na gidan Issakar ya yi maƙarƙashiya gāba da shi, ya buge shi a Gibbeton, a wani garin Filistiyawa, yayinda Nadab da dukan Isra’ila suke wa garin kwanto.
28 Therfor Baasa killide hym, in the thridde yeer of Asa, king of Juda, and regnede for hym.
Ba’asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, ya kuma gāje shi a matsayin sarki.
29 And whanne he hadde regnede, he smoot al the hows of Jeroboam; he lefte not sotheli not o man of his seed, til he dide awei hym, bi the word of the Lord, which he spak in the hond of his seruaunt, Ahia of Silo, a profete,
Nan da nan da ya fara mulki, sai ya kashe dukan iyalin Yerobowam. Bai bar wa Yerobowam wani da rai ba, amma ya hallaka su duka, bisa ga maganar Ubangiji da ya ba wa bawansa Ahiya, mutumin Shilo.
30 for the synnes of Jeroboam whiche he synnede, and in whiche he made Israel to do synne, and for the trespas, bi which he wraththide the Lord God of Israel.
Wannan abu ya faru saboda zunuban da Yerobowam ya yi, ya kuma sa Isra’ila ya yi, kuma saboda ya tsokane Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya yi fushi.
31 Sotheli the residue of wordis of Nadab, and alle thingis whiche he wrouyte, whether these ben not writun in the book of wordis of daies of the kyngis of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Nadab da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
32 And batel was bitwixe Asa and Baasa, kyng of Israel, in al the daies of hem.
Aka yi yaƙi tsakanin Asa da Ba’asha sarkin Isra’ila dukan kwanakin mulkinsu.
33 In the thridde yeer of Asa, kyng of Juda, Baasa, sone of Ahia, regnede on al Israel, in Thersa, foure and twenti yeer.
A shekara ta uku ta Asa sarkin Yahuda, Ba’asha ɗan Ahiya ya zama sarkin dukan Isra’ila a Tirza, ya kuma yi sarauta shekara ashirin da huɗu.
34 And he dide yuel bifor the Lord, and he yede in the weies of Jeroboam, and in hise synnes, bi whiche he made Israel to do synne.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, yana tafiya a hanyoyin Yerobowam da kuma cikin zunubinsa, wanda ya sa Isra’ila suka yi.